Categories
L. KID

L. KID 4

Ayyukan da aka Danƙa wa Iyalin Kohat

1 Ubangiji ya faɗa wa Musa da Haruna,

2 su ƙidaya ‘ya’yan Kohat, maza, daga cikin ‘ya’yan Lawi bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu,

3 su ƙidaya daga mai shekara talatin zuwa hamsin, wato waɗanda suka isa su yi aiki a alfarwa ta sujada.

4 Wannan shi ne aikin ‘ya’yan Kohat, maza, a cikin alfarwa ta sujada a kan abubuwa mafi tsarki.

5 Sa’ad da za a tashi daga zango, sai Haruna, tare da ‘ya’yansa maza, su shiga cikin alfarwa, su kwance labulen kāriya, su rufe akwatin alkawari da shi.

6 Sa’an nan kuma su rufe shi da fatun awaki, su kuma shimfiɗa shuɗin zane a bisansa, su zura masa sandunansa.

7 Sai su shimfiɗa shuɗin zane a kan tebur na gurasar ajiyewa, sa’an nan su dībiya farantai, da cokula, da kwanonin, da butocin hadaya ta sha, da gurasar ajiyewa.

8 Sa’an nan su rufe su da jan zane, a kuma rufe su da fatun awaki, sa’an nan su zura masa sandunansa.

9 Su kuma ɗauki shuɗin zane su rufe alkuki, da fitilunsa, da hantsukansa, da farantansa, da dukan kwanonin man da akan zuba masa.

10 Sai su sa alkukin da dukan kayayyakinsa a cikin fatar awaki su naɗe, su sarƙafa shi asandan ɗaukarsa.

11 A rufe bagaden zinariya da shuɗin zane, a kuma rufe shi da fatun awaki, sa’an nan a zura sandunan ɗaukarsa.

12 Su ɗauki dukan kwanonin da ake amfani da su a Wuri Mai Tsarki, su sa su cikin shuɗin zane, sa’an nan su rufe su da fatun awaki, a sarƙafa su a sanda don a ɗauka.

13 Za su kwashe tokar da take cikin bagaden, su rufe bagaden da shunayyan zane.

14 Sa’an nan su sa dukan kayayyakin bagaden a kansa waɗanda ake aiki da su a wurin, wato su farantai don wuta, da cokula masu yatsotsi, da manyan cokula, da daruna da dai dukan kayayyakin bagaden. Su kuma rufe bagaden da fatun awaki, sa’an nan su zura sandunan ɗaukarsa.

15 Sa’ad da Haruna da ‘ya’yansa maza suka gama kintsa Wuri Mai Tsarki da kayayyakinsa duka a lokacin tashi, sai ‘ya’yan Kohat, maza, su zo su ɗauke kayayyakin, amma kada su taɓa abubuwan nan masu tsarki domin kada su mutu.

Waɗannan su ne ayyukan ‘ya’yan Kohat a duk lokacin da za a naɗe alfarwa ta sujada.

16 Ele’azara kuwa, ɗan Haruna, firist, shi ne zai lura da man fitila, da turare, da hadayar gari ta kullum, da man keɓewa, ya kuma kula da dukan alfarwar, da duk abin da yake cikinta, da Wuri Mai Tsarki, da kayayyakinsa.

17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,

18 “Kada ku bar zuriyar Kohat

19 ta hallaka ta wurin kusatar waɗannan tsarkakakkun abubuwa. Maganin abin, shi ne sai Haruna da ‘ya’yansa maza, su shiga, su nuna wa kowannensu irin aikin da zai yi, da kayan da zai ɗauka.

20 Amma idan Kohatawa suka shiga alfarwar suka tarar firistoci suna shisshirya tsarkakakkun abubuwa don tashi, har dai in sun gani, to za su mutu.”

Ayyukan Gershonawa

21 Ubangiji ya kuma faɗa wa Musa,

22 ya ƙidaya ‘ya’yan Gershon, maza, bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu

23 ya rubuta su tun daga mai shekara talatin, har zuwa mai shekara hamsin, duk wanda ya isa yin aikin da zai yi a alfarwa ta sujada.

24 Wannan shi ne aikin da iyalan Gershonawa za su yi wajen ɗaukar kaya.

25 Za su ɗauki alfarwa ta sujada, da labule na ciki da na waje, da murfi na fatun tumaki wanda yake a bisa alfarwar, da kuma labulen ƙofar alfarwa ta sujada,

26 da labulen farfajiya, da labulen ƙofar farfajiya wadda ta kewaye alfarwar da bagaden, da igiyoyinsu, da duk kayayyakinsu na yin aiki. Sai su yi dukan abin da ya kamata a yi da su.

27 Haruna ne da ‘ya’yansa maza za su nuna wa ‘ya’yan Gershonawa irin aikin da za su yi, da kayayyakin da za su ɗauka. Sai a faɗa musu dukan abin da za su yi, da dukan abinda za su ɗauka.

28 Wannan shi ne aikin da iyalan Gershonawa za su yi a alfarwa ta sujada. Itamar ɗan Haruna, firist, shi zai shugabance su cikin aikin da za su yi.

Ayyukan Merariyawa

29 Ubangiji kuma ya faɗa wa Musa ya ƙidaya Merariyawa bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu,

30 ya rubuta su tun daga mai shekara talatin, har zuwa mai shekara hamsin, duk wanda ya isa yin aikin da zai yi a alfarwa ta sujada.

31 Wannan shi ne abin da aka umarce su su riƙa ɗauka na wajen aikinsu a alfarwa ta sujada, katakan alfarwar, da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta,

32 da dirkokin farfajiya wadda take kewaye da alfarwar, da kwasfansu, da turakunsu, da igiyoyi, da dukan kayayyakinsu. Sai ya faɗa wa kowa kayan da zai ɗauka.

33 Wannan shi ne aikin iyalan ‘ya’yan Merari, maza. Aikinsu ke nan duka a alfarwa ta sujada. Itamar ɗan Haruna, firist, shi ne zai shugabance su.

Yawan Lawiyawa

34-48 Musa da Haruna da shugabannin taron jama’a kuwa suka ƙidaya iyalan Lawiyawa uku, wato Kohatawa, da Gershonawa da Merariyawa bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu, aka rubuta dukan mazaje daga mai shekara talatin zuwa mai shekara hamsin, waɗanda za su iya aiki a alfarwa ta sujada, kamar haka,

Kohat dubu biyu da ɗari bakwai da hamsin (2,750),
Gershon dubu biyu da ɗari shida da talatin (2,630),
Merari dubu uku da ɗari biyu (3,200),
Jimilla duka, dubu takwas da ɗari biyar da tamanin (8,580).

49 Aka ba kowannensu aikinsa da ɗaukar kaya bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa. Haka kuwa aka ƙidaya su kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Categories
L. KID

L. KID 5

Ƙazantattun Mutane

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

2 “Ka umarci Isra’ilawa su fitar da kuturu, da mai ɗiga, da wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin zango.

3 Su fitar da mace ko namiji daga cikin zango, don kada su ƙazantar da zangonku inda nake zaune.”

4 Sai Isra’ilawa suka fitar da su daga cikin zango kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Musa. Haka mutanen Isra’ila suka yi.

Biyan Diyya saboda Ɓarna

5 Ubangiji kuma ya ba Musa

6 waɗannan ka’idodi domin Isra’ilawa. Idan wani ya aikata rashin gaskiya ga Ubangiji, ta wurin saɓa wa wani,

7 sai ya hurta zunubinsa, sa’an nan ya biya cikakkiyar diyyar abin da ƙarin humushin abin, ya ba mutumin da ya yi wa laifin.

8 Idan wanda ya yi wa laifin ya rasu, ba shi kuma da wani dangi na kusa wanda za a ba diyyar, sai a kai diyyar gaban Ubangiji domin firist, tare da ragon hadaya, don yin kafarar da za a yi masa.

9 Dukan sadakoki na tsarkakakkun abubuwa na Isra’ilawa waɗanda sukan kawo wa firist, za su zama nasa.

10 Kowane firist zai adana sadakokin da aka ba shi.

Matsalar Miji mai Kishi

11 Ubangiji kuma ya umarci Musa

12-14 ya faɗa wa Isra’ilawa waɗannan ka’idodi. Idan mutum yana shayin matarsa kan tana yi masa rashin aminci, har ta ƙazantar da kanta ta wurin kwana da wani mutum, amma mijin bai tabbatar ba, domin ta yi abin a asirce, ba kuwa mai shaida, ba a kuma kama ta tana cikin yi ba, ko kuma mijin ya yi shayinta ko da ba ta aikata irin wannan laifi ba,

15 duk da haka sai mutum ya kawo matarsa a gaban firist, ya kawo kuma hadayar da ake bukata, wato humushin garwar garin sha’ir, amma kada ya zuba mai ko kayan ƙanshi, gama hadaya ce domin kishi, domin a bayyana gaskiya a fili.

16 Sai firist ya kawo ta kusa, ya tsai da ita a gaban Ubangiji.

17 Ya ɗebo ruwa mai tsarki a cikin kasko, ya kuma ɗauki ƙurar ƙasar da take a alfarwa ta alkawari ya zuba a ruwan.

18 Sa’an nan firist zai kwance gashin kanta, ya sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi. Ya riƙe ruwan nan mai ɗaci da yake kawo la’ana a hannunsa.

19 Sa’an nan zai sa ta ta yi rantsuwa, ya ce mata, “Idan wani mutum bai kwana da ke ba, to, bari ki kuɓuta daga la’anar da ruwan nan mai ɗaci zai kawo.

20 Amma idan kin kwana da wani mutum wanda ba mijinki ba ne,

21 bari Ubangiji ya sa sunanki ya la’antu cikin jama’arki, ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbure.

22 Bari ruwan nan ya shiga cikinki, ya sa cikinki ya kumbure, cinyarki kuma ta shanye.”

Sai matar ta amsa, ta ce, “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka.”

23 Firist ɗin zai rubuta waɗannan la’anoni a cikin littafi sa’an nan ya wanke rubutun da ruwan nan mai ɗaci.

24 Ya sa matar ta shanye ruwa wanda yake kawo la’ana, sai ruwan ya shiga cikinta, ya zama la’ana mai ɗaci.

25 Firist kuma zai karɓi hadaya ta gari don kishi a hannun matar, ya kaɗa ta a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya kai wurin bagade.

26 Sai ya ɗibi garin hadaya cike da tafin hannu don yin hadayar tunawa, ya ƙone shi a bisa bagaden, bayan wannan ya sa matar ta sha ruwan.

27 Bayan da ya sa ta ta sha ruwan, idan ta ƙazantar da kanta, ta kuwa ci amanar mijinta, ruwan nan mai kawo la’ana zai shiga cikinta ya zama la’ana mai ɗaci, cikinta zai kumbure, cinyarta ta shanye, matar kuwa za ta zama la’ananniya cikin jama’arta.

28 Amma idan matar ba ta ƙazantar da kanta ba, ita tsattsarka ce, za ta kuɓuta, har ta haifi ‘ya’ya.

29 Wannan ita ce dokar kishi idan mutum yana shayin matarsa, wai wani yana kwana da ita.

30 Matar kuwa za ta tsaya a gaban Ubangiji, firist kuwa zai yi da ita bisa ga wannan doka duka.

31 Mijin zai kuɓuta daga muguntar, amma matar za ta ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.

Categories
L. KID

L. KID 6

Ka’idodin Zama Keɓaɓɓe

1 Ubangiji kuma ya umarci Musa

2 ya faɗa wa Isra’ilawa, cewa idan mace ko namiji ya ɗau wa’adi na musamman na zama keɓaɓɓe domin ya keɓe kansa ga Ubangiji,

3 sai ya keɓe kansa daga ruwan inabin da yake sa maye da ruwan inabi mai tsami. Kada kuma ya sha ruwan inabi mai tsami da yake sa maye da kowane irin abin sha da aka yi da ‘ya’yan inabi mai tsami. Kada kuma ya ci ɗanyu ko busassun ‘ya’yan inabi.

4 A dukan kwanakin nan da ya keɓe kansa, kada ya ci kowane irin abu da aka yi da kurangar inabi, ko da ƙwayar inabi ko da ɓawonsa.

5 A dukan kwanakin wa’adinsa na keɓewa, kada aska ta taɓa kansa, sai kwanakin keɓewar kansa ga Ubangiji sun cika. Zai zama mai tsarki, zai kuma bar sumarsa ta yi tsawo.

6 A dukan kwanakin da ya keɓe kansa ga Ubangiji, kada ya kusaci gawa.

7 Ko ta mahaifinsa ce, ko ta mahaifiyarsa, ko ta ɗan’uwansa, ko ta ‘yar’uwarsa, ba zai ƙazantar da kansa ba, tun da yake ya keɓe kansa ga Allahnsa.

8 Shi tsattsarka ne ga Ubangiji dukan kwanakin da ya keɓe kansa.

9 Idan farat ɗaya wani mutum ya rasu kusa da shi, to, keɓewarsa ta ƙazantu, sai ya aske kansa a ranar tsarkakewarsa a kan rana ta bakwai.

10 A rana ta takwas kuwa zai kawo wa firist ‘yan kurciyoyi biyu, ko ‘yan tattabarai biyu a bakin ƙofar alfarwa ta sujada.

11 Sai firist ya miƙa ɗaya don hadayar zunubi, ɗaya kuma don hadayar ƙonawa, ya yi kafara dominsa, gama ya yi zunubi saboda gawa. A wannan rana zai sāke keɓe kansa.

12 Sai ya sāke keɓe kansa ga Ubangiji daidai da kwanakin da ya ɗauka a dā. Zai kawo ɗan rago bana ɗaya na yin hadaya don laifi. Kwanakin da ya yi a dā ba su cikin lissafi domin keɓewarsa ta dā ta ƙazantu.

13 Wannan ita ce ka’idar zama keɓaɓɓe a ranar da keɓewarsa ta cika. Za a kai shi ƙofar alfarwa ta sujada,

14 ya miƙa wa Ubangiji hadayarsa ta ɗan rago bana ɗaya mara lahani don yin hadaya ta ƙonawa, da ‘yar tunkiya bana ɗaya marar lahani ta yin hadaya don zunubi, da rago marar lahani don yin hadaya ta salama,

15 da kwandon abinci marar yisti da aka yi da lallausan gari kwaɓaɓɓe da mai, da ƙosai wanda aka yayyafa masa mai, da hadaya ta gari, da hadayu na sha.

16 Sai firist ɗin ya kai su gaban Ubangiji, ya miƙa hadaya don zunubi, da hadaya ta ƙonawa.

17 Ya kuma miƙa rago don hadaya ta salama ga Ubangiji tare da kwandon abinci, da ƙosai. Firist ɗin kuma zai miƙa hadaya ta gari, da hadaya ta sha.

18 Sai kuma keɓaɓɓen ya aske sumarsa a ƙofar alfarwa ta sujada, sa’an nan ya kwashe sumar, ya zuba cikin wutar da take ƙarƙashin hadaya ta salama.

19 Firist ɗin zai ɗauki dafaffiyar kafaɗar ragon, da malmala guda marar yisti daga cikin kwando, da ƙosai guda, ya sa su a tafin hannun keɓaɓɓen bayan da keɓaɓɓen ya riga ya aske sumarsa.

20 Firist ɗin zai haɗa su don yin hadayar kaɗawa a gaban Ubangiji. Za su zama rabo mai tsarki na firist tare da ƙirjin da aka kaɗa da cinyar da aka yi hadayar ɗagawa da ita. Bayan haka keɓaɓɓen ya iya shan ruwan inabi.

21 Wannan ita ce ka’ida a kan keɓaɓɓe wanda ya ɗau wa’adi. Hadayarsa ga Ubangiji za ta zama bisa ga keɓewarsa, banda kuma abin da ya iya bayarwa. Sai ya cika wa’adin da ya ɗauka bisa ga ka’idar keɓewarsa.

Albarkar da Firist zai Sa wa Jama’a

22 Ubangiji ya umarci Musa

23 ya faɗa wa Haruna da ‘ya’yansa maza, su sa wa Isra’ilawa albarka haka, su ce musu,

24 “Ubangiji ya sa muku albarka, ya kiyaye ku.

25 “Ubangiji ya sa fuskarsa ta haskaka ku, ya yi muku alheri.

26 “Ubangiji ya dube ku da idon rahama, ya ba ku salama.”

27 Idan suka sa wa jama’a wannan albarka sa’ad da suke addu’a ga Ubangiji domin Isra’ilawa, Ubangiji zai sa musu albarka.

Categories
L. KID

L. KID 7

Hadayun Keɓe Bagade

1 A ranar da Musa ya gama kafa alfarwa ta sujada, ya shafa mata mai, ya tsarkake ta, da dukan kayayyakinta, ya kuma shafa wa bagaden mai, ya tsarkake shi da dukan kayayyakinsa.

2 Sai shugabannin Isra’ila, wato shugabannin gidajen kakanninsu, su ne shugabannin kabilansu, waɗanda suka shugabanci waɗannan da aka ƙidaya,

3 suka kawo hadayarsu a gaban Ubangiji, karusai shida rufaffu, da takarkarai goma sha biyu. Shugabanni biyu suka ba da karusa ɗaya, kowannensu kuwa ya ba da takarkari ɗaya, da suka gama miƙa su,

4 sai Ubangiji ya ce wa Musa,

5 “Karɓi waɗannan daga gare su domin a yi aiki da su a alfarwa ta sujada. Ka ba da su ga Lawiyawa, a ba kowane mutum bisa ga aikinsa.”

6 Musa kuwa ya karɓi karusan, da takarkaran, ya ba Lawiyawa.

7 Ya ba ‘ya’ya maza na Gershon karusai biyu da takarkarai huɗu bisa ga aikinsu.

8 Ya kuwa ba ‘ya’ya maza na Merari karusai huɗu da takarkarai takwas bisa ga aikinsu, a hannun Itamar ɗan Haruna, firist.

9 Amma bai ba ‘ya’ya maza na Kohat kome ba, domin aikinsu shi ne lura da kayayyaki masu tsarki waɗanda ake ɗauka a kafaɗa.

10 Sai shugabanni suka miƙa hadayu domin keɓewar bagade a ranar da aka zuba masa mai. Suka fara miƙa sadakokinsu a bagaden,

11 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Bari shugabannin su kawo hadayunsa domin keɓewar bagade, har kwana sha biyu, kowa a ranarsa.”

12-83 Suka miƙa hadayunsu bi da bi kamar haka,

Yahuza Nashon ɗan Amminadab
Issaka Netanel ɗan Zuwar
Zabaluna Eliyab ɗan Helon
Ra’ubainu Elizur ɗan Shedeyur
Saminu Shelumiyel ɗan Zurishaddai
Gad Eliyasaf ɗan Deyuwel
Ifraimu Elishama ɗan Ammihud
Manassa Gamaliyel ɗan Fedazur
Biliyaminu Abidan ɗan Gideyoni
Dan Ahiyezer ɗan Ammishaddai
Ashiru Fagiyel ɗan Okran
Naftali Ahira ɗan Enan

Hadayun da kowannensu ya kawo duk daidai da juna suke, farantin azurfa na shekel ɗari da talatin, da kwanon azurfa na shekel saba’in, bisa ga ma’aunin kuɗin da ake aiki da shi, duka suna cike da garin da aka kwaɓa da mai domin hadaya ta gari, cokali na zinariya guda na shekel goma, cike da kayan ƙanshi, da ɗan bijimi guda, da rago ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya domin hadaya ta ƙonawa, da akuya guda domin hadaya ta zunubi, da bijimai biyu, da raguna biyar, da awaki biyar, da ‘yan raguna biyar bana ɗaya ɗaya, domin hadaya ta salama.

84-88 Ga jimillar hadayun da shugabanni goma sha biyu suka kawo domin keɓewar bagaden:

farantan azurfa goma sha biyu da kwanonin azurfa goma sha biyu, duka nauyinsu shekel dubu biyu da ɗari huɗu

cokulan zinariya goma sha biyu, nauyinsu duka shekel ɗari da ashirin cike da kayan ƙanshi

bijimai goma sha biyu, da raguna goma sha biyu, da ‘yan raguna goma sha biyu bana ɗaya ɗaya, da kuma hadaya ta gari da za a haɗa da waɗannan domin hadaya ta ƙonawa

awaki goma sha biyu domin hadaya don zunubi

bijimai ashirin da huɗu, da raguna sittin, da awaki sittin, da ‘yan raguna bana ɗaya ɗaya guda sittin domin hadaya ta salama.

89 Duk lokacin da Musa ya shiga alfarwa ta sujada domin ya yi magana da Ubangiji, sai ya ji Ubangiji yana magana da shi daga bisa murfin akwatin alkawari, a tsakanin kerubobi masu fikafikai biyu.

Categories
L. KID

L. KID 8

Haruna ya Kakkafa Fitilu

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa ya

2 faɗa wa Haruna cewa, “Sa’ad da za ka kakkafa fitilun nan bakwai, sai ka kakkafa su yadda za su haskaka sashin gaba.”

3 Haka kuwa Haruna ya yi. Ya kakkafa fitilun yadda za su haskaka a gaban alkukin, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

4 Da zinariya aka ƙera alkukin tun daga samansa har gindinsa, bisa ga fasalin da Ubangiji ya nuna wa Musa.

Keɓewar Lawiyawa

5 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,

6 “Keɓe Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa ka tsarkake su.

7 Ga yadda za ka tsarkake su. Ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa. Su aske jikunansu duka, su kuma a wanke tufafinsu, sa’an nan za su tsarkaka.

8 Su kuma ɗauki maraƙi tare da lallausan garin hadaya kwaɓaɓɓe da mai. Kai kuma ka ɗauki wani maraƙi na yin hadaya don zunubi.

9 Sa’an nan ka gabatar da Lawiyawa a gaban alfarwa ta sujada, ka kira taron Isra’ilawa duka.

10 Sa’ad da ka gabatar da Lawiyawa a gaban Ubangiji, sai Isra’ilawa su ɗibiya hannuwansu bisa Lawiyawa.

11 Haruna kuma zai gabatar da Lawiyawan a gaban Ubangiji kamar hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa domin su zama masu yi wa Ubangiji aiki.

12 Sa’an nan Lawiyawa za su ɗibiya hannuwansu a bisa kawunan maruƙan. Za ka yi hadaya domin zunubi da maraƙi ɗaya, ɗaya kuma ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji domin ka yi kafara saboda Lawiyawa.

13 “Za ka keɓe Lawiyawa su zama kamar hadaya ta kaɗawa gare ni, ka sa Haruna da ‘ya’yansa maza su lura da su.

14 Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa su zama nawa.

15 Bayan da ka tsarkake su, ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, za su cancanta su yi aiki a alfarwa ta sujada.

16 Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato dukan ‘ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.

17 A ranar da na kashe ‘ya’yan fari na ƙasar Masar, na keɓe wa kaina dukan ‘ya’yan fari na Isra’ilawa, na mutum, da na dabba.

18 Na kuwa keɓe wa kaina Lawiyawa a maimakon dukan ‘ya’yan fari na Isra’ilawa.

19 Daga cikin Isra’ilawa kuwa na ba da Lawiyawa ga Haruna da ‘ya’yansa maza don su yi wa Isra’ilawa hidima a alfarwa ta sujada, su kuma yi kafara dominsu don kada annoba ta sami Isra’ilawa sa’ad da suka kusaci alfarwa ta sujada.”

20 Musa da Haruna kuwa da dukan taron Isra’ilawa suka yi wa Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarce Musa, haka kuwa Isra’ilawa suka yi musu.

21 Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka wanke tufafinsu. Haruna kuwa ya keɓe su, suka zama kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji, ya kuma yi kafara dominsu don ya tsarkake su.

22 Bayan haka Lawiyawa suka shiga alfarwa ta sujada don su yi aiki a gaban Haruna da ‘ya’yansa maza, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa a kan Lawiyawa, haka kuwa suka yi musu.

Adadin yawan Shekarun Aikin Lawiyawa

23 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,

24 “Wannan ita ce ka’idar aikin Lawiyawa, tun daga mai shekara ashirin da biyar zuwa gaba, zai shiga yin aiki a alfarwa ta sujada.

25 Amma daga shekara hamsin, sai su huta daga aiki alfarwa ta sujada.

26 Amma su taimaki ‘yan’uwansu da tafiyar da ayyuka a cikin alfarwa ta sujada, sai dai ba za su ɗauki nauyin gudanar da aikin ba. Haka za ka shirya wa Lawiyawa aikinsu.”

Categories
L. KID

L. KID 9

Idin Ƙetarewa na Biyu

1 Sai Ubangiji ya yi wa Musa magana a jejin Sinai a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar, ya ce,

2 “Sai Isra’ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokacinsa.

3 A rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, da maraice za su kiyaye shi a ƙayyadadden lokacinsa bisa ga dokokinsa da ka’idodinsa duka.”

4 Musa kuwa ya faɗa wa Isra’ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa.

5 Sai suka kiyaye Idin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu ga watan farko da maraice a cikin jejin Sinai bisa ga dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa. Haka kuwa Isra’ilawa suka yi.

6 Akwai waɗansu mutane da suka ƙazantu ta wurin taɓa gawar wani mutum,don haka ba su iya kiyaye Idin Ƙetarewar a ranar ba. Sai suka zo wurin Musa da Haruna a ranar,

7 suka ce masa, “Ai, mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa. Me ya sa aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran ‘yan’uwanmu a ƙayyadadden lokacin yinta?”

8 Sai Musa ya ce musu, “Dakata, har na ji abin da Ubangiji zai umarta a kanku.”

9 Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa

10 ya faɗa wa Isra’ilawa ya ce, “Idan wani mutum na cikinku, ko na cikin zuriyarku, ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji.

11 Za su kiyaye shi da maraice a watan biyu yana da kwana goma sha huɗu. Za su ci shi da abinci marar yisti da ganyaye masu ɗaci.

12 Kada su bar kome daga cikinsa ya kai gobe, kada kuwa a fasa ƙashinsa, sai su yi shi bisa ga dukan umarnin Idin Ƙetarewa.

13 Amma mutumin da yake da tsarki, bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi kiyaye Idin Ƙetarewa, sai a raba wannan mutum da jama’arsa, gama bai miƙa hadayar Ubangiji a ƙayyadadden lokacin yinta ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.

14 “Idan baƙo yana zaune a wurinku, shi ma sai ya kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji bisa ga umarnai da ka’idodi na Idin Ƙetarewa. Ka’ida ɗaya ce ga baƙo da ɗan gari.”

Girgijen Wuta

15-16 A ranar da aka kafa alfarwa ta sujada, sai girgije ya sauko ya rufe ta. Da maraice kuwa girgijen yana kamar wuta.

17 A duk lokacin da aka gusar da girgijen, sai Isra’ilawa su kama hanya. A inda girgijen ya tsaya, nan kuma Isra’ilawa za su kafa zango.

18 Da umarnin Ubangiji Isra’ilawa suke tashi, da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana bisa alfarwar, sukan yi ta zamansu a zangon.

19 Ko da girgije ya daɗe a bisa alfarwar Isra’ilawa ba sukan tashi ba, sukan bi umarnin Ubangiji.

20 Wani lokaci girgijen yakan yi ‘yan kwanaki ne kawai bisa alfarwar. Tashinsu da zamansu sun danganta ga umarnin Ubangiji.

21 Wani lokaci girgijen yakan zauna a bisa alfarwar daga maraice zuwa safiya ne kawai, sa’an nan ya tashi, su kuma sai su tashi. Amma idan girgijen ya yini, ya kwana, sa’an nan ya tashi, su kuma sai su tashi.

22 Ko kwana biyu ne girgijen ya yi, yana zaune a bisa alfarwar ko wata guda, ko fi, sai Isra’ilawa su yi ta zamansu a zangon, ba za su tashi ba. Amma in ya tashi, sai su kuma su tashi.

23 Da umarnin Ubangiji suke sauka, da umarninsa kuma suke tashi, suna bin faɗarsa, yadda ya umarci Musa.

Categories
L. KID

L. KID 10

Kakaki na Azurfa

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

2 “Ka ƙera kakaki biyu na azurfa don ka riƙa kirawo taron jama’a, don kuma ka riƙa sanashe su lokacin tashi daga zangon.

3 Lokacin da aka busa kakaki biyu ɗin gaba ɗaya, sai taron jama’a duka su tattaru a wurinka a ƙofar alfarwa ta sujada.

4 Amma idan ɗaya kaɗai aka busa, sai shugabannin Isra’ila su tattaru a wurinka.

5 Sa’ad da kuka yi busar faɗakarwa, waɗanda suke zaune a gabashin zangon za su tashi.

6 Sa’ad da kuma kuka yi busar faɗakarwa ta biyu, waɗanda suke a kudancin zangon za su tashi. Sai a yi busar faɗakarwa a kowane lokaci da za su tashi.

7 Amma idan za a kira jama’a ne sai a yi busa da ƙarfi amma banda faɗakarwa.

8 ‘Ya’yan Haruna, maza, firistoci, su ne za su busa kakakin.

“Kakakin za su zama muku ka’ida ta din din din cikin dukan zamananku.

9 Sa’ad da kuka tafi yaƙi a ƙasarku gāba da maƙiyanku da suke matsa muku lamba, sai ku yi busar faɗakarwan nan da kakakin, Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, ya cece ku daga maƙiyanku.

10 A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Tashin Isra’ilawa daga Sinai

11 A rana ta ashirin ga watan biyu a shekara ta biyu, sai aka gusar da girgijen daga kan alfarwa ta sujada.

12 Isra’ilawa kuwa suka tashi daki-daki daga jejin Sinai. Girgijen kuma ya tsaya a jejin Faran.

13 Suka fara tafiyarsu bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa.

14 Tutar zangon kabilar mutanen Yahuza ta fara tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Nashon, ɗan Amminadab, shi ne shugaban rundunarsu.

15 Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar.

16 Shugaban rundunar kabilar mutanen Zabaluna Eliyab ne, ɗan Helon.

17 Sa’an nan aka kwankwance alfarwar, sai ‘ya’yan Gershon, da ‘ya’yan Merari masu ɗaukar alfarwar suka kama hanya.

18 Tutar zangon kabilar mutanen Ra’ubainu ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Elizur ne, ɗan Shedeyur.

19 Shugaban rundunar kabilar mutanen Saminu kuwa Shelumiyel ne, ɗan Zurishaddai.

20 Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel.

21 Daga nan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar.

22 Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud.

23 Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur.

24 Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni.

25 A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai.

26 Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran.

27 Shugaban rundunar kabilar mutanen Naftali Ahira ne, ɗan Enan.

28 Wannan shi ne tsarin tafiyar Isra’ilawa bisa ga rundunansu sa’ad da sukan tashi.

29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra’ila alheri.”

30 Amma ya ce masa, “Ba zan tafi ba, zan koma ƙasata da wurin dangina.”

31 Musa kuwa ya ce masa, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu, gama ka san jejin da muke zango, kai za ka zama idonmu.

32 Idan ka tafi tare da mu, kowane irin alheri da Ubangiji zai yi mana, mu kuma haka za mu yi maka.”

Mutanen suka Kama Hanya

33 Sai suka tashi daga dutsen Ubangiji, wato Sinai, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji kuwa ya wuce gabansu don ya nemar musu masauki.

34 A duk lokacin da suka tashi daga zango, sai girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.

35 Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.”

36 Sa’ad da akwatin ya sauka kuma, Musa yakan ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubun dubbai na iyalan Isra’ila.”

Categories
L. KID

L. KID 11

Ubangiji zai Ba su Nama

1 Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai, wutarsa ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone wani gefe na zangon.

2 Sai mutanen suka yi ta yi wa Musa kuka, Musa kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.

3 Aka sa wa wurin suna Tabera, wato matoya, domin wutar Ubangiji ta yi ƙuna a cikinsu.

4 Tattarmukan da suke cikinsu kuwa suka faye kwaɗayin nama, har Isra’ilawa ma da kansu suka fara gunaguni suna cewa, “Wa zai ba mu nama mu ci?

5 Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, da su kakamba, wato wani irin kayan lambu ne mai yaɗuwa, da guna, da sāfa, da albasa, da tafarnuwa.

6 Yanzu ranmu ya yi yaushi, ba wani abu, sai dai wannan manna muke gani.”

7 Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuwa kamar na ƙāro ne.

8 Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa, ko kuwa su daka, su dafa, su yi waina da ita. Dandanar wainar tana kamar wadda aka yi da mai.

9 Manna takan zubo tare da raɓa da dad dare a zangon.

10 Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar alfarwarsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai.

11 Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Don me ka wahalar da bawanka? Me ya sa ban sami tagomashi a gare ka ba, da ka jibga wahalar dukan mutanen nan a kaina?

12 Ni na ɗauki cikinsu? Ko kuwa ni ne na haife su, har da za ka ce mini, ‘Ka ɗauke su a ƙirjinka, kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka rantse za ka bai wa kakanninsu?’

13 A ina zan samo nama da zan ba wannan jama’a duka? Gama suna ta gunaguni a gabana, suna cewa, ‘Ba mu nama mu ci.’

14 Ba zan iya ɗaukar nawayar mutanen nan ni kaɗai ba, gama nauyin ya fi ƙarfina.

15 Idan haka za ka yi da ni, ina roƙonka ka kashe ni, idan na sami tagomashi a gare ka, don kada in rayu in ga wannan baƙin ciki.”

16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tattaro mini mutum saba’in daga cikin dattawan Isra’ila waɗanda aka sani su ne dattawa da shugabannin jama’ar, ka kawo su a alfarwa ta sujada, ka sa su tsaya tare da kai.

17 Ni kuwa zan sauko, in yi magana da kai a can. Zan ɗiba daga cikin ruhun da yake cikinka, in ba su. Su kuma za su ɗauki nawayar jama’ar tare da kai, domin kada ka ɗauki nawayar kai kaɗai.

18 Ka ce wa jama’ar, su tsarkake kansu don gobe, za su ci nama, gama Ubangiji ya ji gunagunin da suka yi, da suka ce, ‘Wa zai ba mu nama mu ci? Ai, zama cikin Masar ya fi mana.’ Domin haka Ubangiji zai ba su nama, za su kuwa ci.

19 Ba ma don kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko ashirin kaɗai za su ci ba.

20 Amma har wata guda cur. Za su ci har ya gundure su, ya zama musu abin ƙyama saboda sun ƙi Ubangiji wanda yake tare da su, suka yi gunaguni a gabansa , suna cewa, ‘Me ya sa ma, muka fito Masar?’ ”

21 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutum dubu ɗari shida (600,000) ne suke tafe tare da ni, ga shi kuwa, ka ce za ka ba su nama, za su ci har wata guda cur.

22 Za a yanyanka musu garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu, don su ishe su? Ko kuwa za a tattara musu dukan kifayen teku don su ishe su?”

23 Sai Ubangiji ya amsa wa Musa, “Ikon Ubangiji ya gaza ne? Yanzu za ka gani ko maganata gaskiya ce, ko ba gaskiya ba ce.”

Shugabanni sun yi Annabci

24 Musa kuwa ya fita, ya faɗa wa jama’a maganar Ubangiji, ya kuma tattara dattawa saba’in daga cikin jama’ar, ya sa su tsaya kewaye da alfarwar.

25 Sa’an nan Ubangiji ya sauko cikin girgije, ya yi masa magana, ya kuma sa ruhun da yake kansa, ya zama a kan dattawan nan saba’in. Sa’ad da ruhun ya zauna a kansu sai suka yi annabci, amma daga wannan kuma ba su ƙara yi ba.

26 Akwai mutum biyu da suka ragu a zangon, sunan ɗayan Eldad, ɗayan kuwa Medad. Ruhun kuma ya zauna a kansu gama suna cikin dattawan nan da aka lasafta, amma ba su fita zuwa alfarwa ba, sai suka yi annabci a zangon.

27 Sai wani saurayi ya sheƙa a guje ya faɗa wa Musa, ya ce, “Ga Eldad da Medad suna nan suna annabci a cikin zangon.”

28 Joshuwa ɗan Nun, mai yi wa Musa barantaka, ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun, ya ce, “Ya shugabana, Musa, ka hana su.”

29 Amma Musa ya ce masa, “Kishi kake yi domina? Da ma jama’ar Ubangiji duka annabawa ne, har ma ya sa Ruhunsa a cikinsu!”

30 Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma zango.

Ubangiji ya Aiko da Makware

31 Sai iska ta huro daga wurin Ubangiji, ta koro makware daga teku, ta bar su birjik kusa da zango, misalin nisan tafiyar yini guda ta kowace fuska. Tsayin tashinsu daga ƙasa misalin kamu biyu ne.

32 Sai mutane suka tashi suka yi ta tattara makware dukan wannan yini, da dukan dare, har kashegari duka. Wanda ya tattara kaɗan, ya tara garwa metan. Suka shanya abinsu kewaye da zangon.

33 Tun suna cikin cin naman, sai Ubangiji ya husata da mutanensa, ya bugi jama’a da annoba mai zafi.

34 Don haka aka sa wa wurin suna Kibrot-hata’awa, wato makabarta, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.

35 Daga Kibrot-hata’awa mutanen suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.

Categories
L. KID

L. KID 12

Aka Hukunta Maryamu

1 Sai Maryamu da Haruna suka zargi Musa saboda mace, Bahabashiya, wadda ya aura.

2 Suka ce, “Da Musa kaɗai ne, Ubangiji ya yi magana, bai yi magana da mu kuma ba?” Ubangiji kuwa ya ji.

3 (Musa dai mai tawali’u ne ƙwarai, fiye da kowane mutum a duniya.)

4 Farat ɗaya sai Ubangijiya ce wa Musa, da Haruna, da Maryamu, “Ku uku, ku tafi zuwa alfarwa ta sujada.” Sai su uku suka tafi.

5 Ubangiji kuwa ya zo cikin al’amudin girgije, ya tsaya a ƙofar alfarwar, ya yi kira, “Haruna! Maryamu!” Su biyu fa suka gusa gaba.

6 Ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa! Idan akwai annabawa a cikinku, nakan bayyana gare su cikin wahayi, in kuma yi magana da su ta cikin mafarki.

7 Ba haka nake magana da bawana Musa ba, na sa shi ya lura da dukkan jama’ata Isra’ila.

8 Nakan yi magana da shi fuska da fuska a sarari, ba a duhunce ba. Yakan kuma ga zatina. Me ya sa ba ku ji tsoron zargin bawana Musa ba?”

9 Ubangiji kuwa ya husata da su, ya rabu da su.

10 Sa’ad da al’amudin girgijen ya tashi daga kan alfarwar, sai ga Maryamu ta kuturce, fari fat kamar auduga. Da Haruna ya juya wajen Maryamu, ya ga ta zama kuturwa.

11 Sai ya ce wa Musa, “Ya shugabana, ina roƙonka, kada ka hukunta mu saboda wannan zunubi, mun yi aikin wauta.

12 Na roƙe ka kada ka bari ta zama kamar matacce wanda rabin jikinsa ruɓaɓɓe ne a lokacin da aka haife shi.”

13 Sai Musa ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ya Allah, ka warkar da ita.”

14 Amma ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata yau a fuskarta, ba za ta ji kunya har kwana bakwai ba? Bari a fitar da ita a bayan zangon kwana bakwai, bayan haka a shigar da ita.”

15 Aka fitar da Maryamu a bayan zangon har kwana bakwai. Jama’ar kuwa ba su ci gaba da tafiya ba, sai da aka shigar da Maryamu a zangon.

16 Bayan wannan jama’a suka tashi daga Hazerot suka sauka a jejin Faran.

Categories
L. KID

L. KID 13

‘Yan Leƙen Asirin Ƙasa

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,

2 “Ka aiki mutane su leƙi asirin ƙasar Kan’ana wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila na kakanninsu, ka zaɓi mutum guda wanda yake shugaba a cikinsu.”

3-15 Musa kuwa ya yi biyayya, daga jejin Faran ya aika da waɗannan shugabanni,

Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ra’ubainu.

Shafat ɗan Hori, daga kabilar Saminu.

Kalibu ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuza.

Igal ɗan Yusufu, daga kabilar Issaka.

Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Ifraimu.

Falti ɗan Rafu, daga kabilar Biliyaminu.

Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zabaluna.

Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manassa.

Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan.

Setur ɗan Maikel, daga kabilar Ashiru.

Nabi ɗan Wofsi,daga kabilar Naftali.

Geyuwel ɗan Maci,daga kabilar Gad.

16 Waɗannan su ne mutanen da Musa ya aika su leƙo asirin ƙasar. Amma Musa ya ba Hosheya, ɗan Nun, suna Joshuwa.

17 Sa’ad da Musa ya aike su leƙen asirin ƙasar Kan’ana, ya ce musu, “Ku haura, ku bi ta Negeb har zuwa ƙasar tuddai,

18 ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanenta ƙarfafa ne, ko raunana ne, ko su kima ne, ko kuwa suna da yawa,

19 ko ƙasa tasu mai ni’ima ce, ko babu, ko biranensu marasa garu ne, ko masu garu ne,

20 ko ƙasar tana da wadata,ko matalauciya ce, ko ƙasar kurmi ce, ko fili. Ku yi jaruntaka, ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Gama lokacin farkon nunan inabi ne.)

21 Sai suka haura, suka leƙo asirin ƙasar tun daga jejin Zin har zuwa Rehob kusa da Hamat.

22 Suka haura ta wajen Negeb, suka isa Hebron inda Ahimaniyawa, da Sheshaiyawa, da Talmaiyawa, zuriyar ƙarfafan mutanen da ake kira Anakawa suke zaune. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)

23 Da suka isa Kwarin Eshkol, sai suka datse reshe guda na nonon inabi da ‘ya’ya cunkus. Suka rataya a sanda, mutum biyu suka ɗauka a kafaɗunsu. Suka kuma kawo rumman da ɓaure.

24 Aka kira wurin Kwarin Eshkol, wato “nonon inabi,” saboda nonon inabi wanda ‘yan leƙen ƙasa suka yanko a wurin.

25 Bayan sun yi kwana arba’in suna leƙen asirin ƙasar, sai suka komo.

26 Suka zo wurin Musa, da Haruna, da dukan taron jama’ar Isra’ila a jejin Faran a Kadesh. Suka faɗa musu labarin tafiyarsu, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar da suka kawo.

27 Suka ce wa Musa, “Mun tafi ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana da yalwar abinci, ga kuma amfanin ƙasar.

28 Amma mazaunan ƙasar ƙarfafa ne, biranenta kuma manya ne, masu garu, banda wannan kuma, mun ga Anakawa a can.

29 Amalekawa suna zaune a Negeb, Hittiyawa kuwa, da Yebusiyawa, da Amoriyawa suna zaune a ƙasar tuddai, Kan’aniyawa suna zaune kusa da teku, da kuma kusa da Kogin Urdun.”

30 Amma Kalibu ya sa mutane su yi shiru a gaban Musa, ya ce, “Bari mu tafi nan da nan mu mallaki ƙasar, gama za mu iya cinta.”

31 Sai mutanen da suka tafi tare da shi suka amsa suka ce, “Ba za mu iya haurawa, mu kara da mutanen ba, gama sun fi mu ƙarfi.”

32 Haka suka kawo wa ‘yan’uwansu, Isra’ilawa, mugun rahoton ƙasa wadda suka leƙi asirinta, suka ƙara da cewa, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zaune a cikinta, dukan mutane kuma da muka gani a cikinta ƙatti ne.

33 Mun kuma ga manyan mutane a can, wato mutanen Anakawa da suka fito daga Nefilawa. Sai muka ga kanmu kamar fara ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”