Categories
L. KID

L. KID 14

Mutane suka yi Yaji

1 Sai dukan taron jama’a suka yi kuka da babbar murya dukan dare saboda wahala.

2 Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, suke ce, “Da ma mun mutu a ƙasar Masar, ko kuwa a wannan jeji.

3 Me ya sa Ubangiji ya kawo mu a wannan ƙasa, mu mutu da takobi? Matanmu da ƙanananmu za su zama ganima. Ba zai fi mana kyau, mu koma Masar ba?”

4 Sai suka ce wa juna, “Bari mu shugabantar da wani, mu koma Masar.”

5 Sa’an nan Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban dukan taron jama’ar Isra’ilawa.

6 Sai Joshuwa, ɗan Nun, da Kalibu, ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu.

7 Suka ce wa dukan taron jama’ar Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa ta don mu leƙi asirinta, ƙasa ce mai kyau ƙwarai da gaske.

8 Idan Ubangiji yana jin daɗinmu zai kai mu a wannan ƙasa da take cike da yalwar abinci, ya ba mu ita.

9 Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji, kada kuwa ku ji tsoron mutanen ƙasar. Za mu ci su ba wuya, Ubangiji kuma zai lalatar da gumakansu da suke kāre su. Ubangiji kuwa yana tare da mu, kada ku ji tsoronsu.”

10 Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutanen Isra’ila daga cikin alfarwa ta sujada.

11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su raina ni? Har yaushe za su ƙi gaskata ni, ko da yake na aikata alamu a tsakiyarsu?

12 Zan kashe su da annoba, in raba su da gādonsu. Zan yi wata al’umma da kai, wadda za ta fi su girma da iko.”

13 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji, gama ka fitar da mutanen daga cikinsu da ƙarfin ikonka.

14 Za su kuwa faɗa wa mutanen wannan ƙasa, gama sun riga sun ji, kai, ya Ubangiji, kana cikin tsakiyar jama’ar nan wadda kake bayyana kanka gare ta fuska da fuska. Girgijenka kuma yana tsaye a kansu, kakan kuma yi musu jagora da al’amudin wuta.

15 Idan kuwa ka kashe jama’ar nan gaba ɗaya, sai al’umman da suka ji labarinka, su ce,

16 ‘Domin Ubangiji ya kāsa kai jama’ar nan zuwa cikin ƙasar da ya rantse zai ba su, don haka ya kashe su a cikin jeji.’

17 Yanzu fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka sa ikonka ya zama da girma kamar yadda ka alkawarta cewa,

18 ‘Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai yawan ƙauna, kana gafarta mugunta da laifi, amma ba za ka ƙyale mai laifi ba, gama kakan ɗora wa ‘ya’ya alhakin muguntar iyaye, har tsara ta uku da ta huɗu.’

19 Ina roƙonka ka gafarta muguntar wannan jama’a saboda ƙaunarka mai girma, kamar yadda kake gafarta musu tun daga Masar har zuwa yanzu.”

20 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda maganarka na gafarta.

21 Amma, hakika, na rantse da zatina, kamar yadda ɗaukakata za ta cika duniya duka,

22 dukan mutanen da suka ga ɗaukakata da alamuna waɗanda na aikata a Masar, da kuma a jejin, suka kuwa jarraba ni har sau goma, ba su kuma yi biyayya da maganata ba,

23 ba za su ga ƙasar da na rantse zan ba kakanninsu ba. Duk waɗanda suka raina ni, ba za su ga ƙasar ba,

24 sai dai bawana Kalibu da yake ruhunsa dabam ne, gama ya bi ni sosai.

25 Yanzu fa, tun da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zaune a kwarin, gobe sai ku juya ku nufi wajen jejin ta hanyar Bahar Maliya.”

Ubangiji ya Hukunta Jama’ar saboda Gunaguni

26 Ubangiji kuma ya ce wa Musa da Haruna,

27 “Har yaushe wannan mugun taron jama’a zai yi ta gunaguni a kaina? Na ji gunagunin da Isra’ilawa suka yi a kaina.

28 Sai ka faɗa musu cewa, ‘Ni Ubangiji na rantse da zatina, abin da kuka sanar da ni zan yi muku.

29 Gawawwakin waɗanda suka yi gunaguni a kaina za su fādi cikin jejin nan. Dukan waɗanda aka ƙidaya, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba,

30 ba wanda zai shiga ƙasar da na rantse ta zama wurin zamanku, sai Kalibu, ɗan Yefunne, da Joshuwa ɗan Nun.

31 Amma ‘yan ƙanananku, waɗanda kuka ce za su zama ganima, su ne zan kai su cikin ƙasar, za su san ƙasar da kuka raina.

32 Amma ku, gawawwakinku za su fāɗi a jejin.

33 ‘Ya’yanku za su yi yawo a jeji shekara arba’in, za su sha wahala saboda rashin bangaskiyarku, har mutuminku na ƙarshe ya mutu a jejin.

34 Bisa ga kwanakin nan arba’in da kuka leƙi asirin ƙasar, haka za ku ɗauki alhakin zunubanku shekara arba’in, gama kowane kwana a maimakon shekara yake. Ta haka za ku sani ban ji daɗin abin da kuka yi ba.

35 Ni Ubangiji na faɗa, hakika, haka zan yi da wannan mugun taron jama’ar da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su ƙare ƙaƙaf a wannan jeji, a nan za su mutu.’ ”

36 Mutanen da Musa ya aika su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,

37 mutanen nan da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta kashe su a gaban Ubangiji.

38 Sai dai Joshuwa, ɗan Nun, da Kalibu, ɗan Yefunne, kaɗai ne ba za su mutu ba daga cikin waɗanda suka tafi leƙen asirin ƙasar.

Ƙoƙarin Cin Ƙasar na Farko ya Kāsa

39 Da Musa ya faɗa wa Isra’ilawa abin da Ubangiji ya ce, sai jama’a suka yi baƙin ciki ƙwarai.

40 Suka tashi da sassafe, suka hau kan tudu, suna cewa, “Ga shi, a shirye muke mu tafi wurin da Ubangiji ya ambata, gama mun yi kuskure.”

41 Amma Musa ya ce, “Me ya sa kuke karya umarnin Ubangiji? Yin haka ba zai kawo nasara ba.

42 Kada ku haura domin kada ku sha ɗibga a gaban maƙiyanku, gama Ubangiji ba ya tare da ku.

43 Gama akwai Amalekawa da Kan’aniyawa a gabanku, za su kashe ku da takobi domin kun bar bin Ubangiji, don haka Ubangiji ba zai kasance tare da ku ba.”

44 Amma sai suka yi izgili, suka haura kan tudun, amma akwatin alkawari da Musa ba su bar zangon ba.

45 Sai Amalekawa da Kan’aniyawa, mazauna a kan tudun, suka gangaro, suka ci su, suka runtume su har Harma, wato hallakarwa.

Categories
L. KID

L. KID 15

Ka’idodin Yin Hadayu

1 Ubangiji ya ba Musa

2 waɗannan ka’idodi domin Isra’ilawa su kiyaye su a ƙasar da zai ba su.

3 Sa’ad da za su yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji daga cikin garken shanu, ko na tumaki da awaki, ko hadaya ta ƙonawa ce, ko ta cika wa’adi ce, ko ta yardar rai ce, ko ta ƙayyadaddun idodinsu ce, don a ba da ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji,

4 sai shi wanda ya kawo hadayar ga Ubangiji, ya kuma kawo hadaya ta gari, humushin garwa guda kwaɓaɓɓe da rubu’in moɗa na mai.

5 Ya kuma shirya hadaya ta sha, rubu’in moɗa ta ruwan inabi domin kowane ɗan rago na hadaya ta ƙonawa.

6 Idan kuwa da rago ne, a shirya hadaya ta gari humushi biyu na garwa, a kwaɓa da sulusin moɗa na mai.

7 Za a kuma miƙa hadaya ta sha da sulusin moɗa na ruwan inabi, don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.

8 Idan kuwa da bijimi ne za a yi hadaya ta ƙonawar, ko sadaka domin cika wa’adi, ko ta salama ga Ubangiji,

9 sai a miƙa hadaya ta gari tare da bijimin, humushi uku na garwar gari kwaɓaɓɓe da rabin moɗa na mai.

10 Za a kuma miƙa hadaya ta sha da rabin moɗa na ruwan inabi. Hadaya ce da akan yi da wuta, mai yin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.

11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago,ko ɗan rago,ko bunsuru.

12 Bisa ga yawan abin da aka shirya, haka za a yi da kowannensu bisa ga adadinsu.

13 Haka dukan waɗanda suke ‘yan ƙasa za su yi in za su ba da hadayar da akan yi da wuta don yin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.

14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinsu ko ko wane ne da yake tare da su a dukan zamanansu, yana so ya ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, sai ya yi kamar yadda suke yi.

15 Ka’ida ɗaya ce domin taron jama’a da kuma baƙin da yake zaune tare da su. Ka’ida ce madawwamiya a dukan zamanansu. Kamar yadda suke a gaban Ubangiji, haka kuma baƙon da yake baƙunci a cikinsu yake.

16 Ka’ida ɗaya ce umarni kuma ɗaya ne domin su da baƙin da yake baƙunci a cikinsu.

17 Ubangiji ya ba Musa

18 waɗannan ka’idodi domin Isra’ilawa su kiyaye a ƙasar da zai ba su.

19 Sa’ad da suke cin amfaninta, sai su miƙa hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji.

20 Daga cikin ɓarzajjen hatsinsu na nunan fari sai su yi wainar da za su ɗaga don yin hadaya da amfanin masussuka.

21 Daga cikin ɓarzajjen hatsinsu na nunan fari, sai su miƙa wa Ubangiji hadaya ta ɗagawa a dukan zamanansu.

22 Amma idan sun yi kuskure, ba su kiyaye dukan umarnan nan waɗanda Ubangiji ya faɗa wa Musa ba,

23 wato duk dai abin da ubangiji ya umarta ta bakin Musa tun daga ranar da Ubangiji ya ba da umarnan, har zuwa dukan zamanansu,

24 idan jama’a sun yi kuskure da rashin sani, sai su miƙa maraƙi don yin hadaya ta ƙonawa don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Su kuma ba da hadaya ta gari, da hadaya ta sha tare da maraƙin bisa ga ka’idar. Za su kuma miƙa bunsuru ɗaya na yin hadaya don zunubi.

25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuwa gafarta musu kuskuren, domin sun kawo hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi ga Ubangiji saboda kuskurensu.

26 Za a gafarta wa dukan taron jama’ar Isra’ilawa da baƙon da yake baƙunci a cikinsu, kuskuren da suka yi.

27 Idan bisa ga kuskure wani mutum ya yi zunubi, sai ya ba da ‘yar akuya bana ɗaya ta yin hadaya don zunubi.

28 Firist kuwa zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin da ya yi kuskuren, gama ya yi zunubi ba da saninsa ba, za a kuwa gafarta masa.

29 Ka’idarsu ɗaya ce a kan wanda ya yi kuskure, ko Ba’isra’ile ne, ko baƙon da yake baƙunci a cikinsu.

30 Amma mutumin da ya yi laifi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙo ne, ya sāɓi Ubangiji, sai a kashe shi,

31 gama ya raina maganar Ubangiji, ya karya umarninsa. Hakika za a kashe mutumin nan, alhakin zunubinsa, yana wuyansa.

Jajjefewar Wanda ya Ɓata Ranar Asabar

32 Sa’ad da Isra’ilawa suke jeji, sai aka iske wani yana tattara itace a ranar Asabar.

33 Sai suka kai shi wurin Musa, da Haruna, da dukan taron jama’a.

34 Aka sa shi a gidan waƙafi domin ba a bayyana abin da za a yi da shi ba tukuna.

35 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “A kashe mutumin, dukan taron jama’a za su jajjefe shi da duwatsu a bayan zangon.”

36 Dukan taron jama’a suka kai shi bayan zangon, suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Dokoki a kan Tuntayen Riguna

37 Ubangiji ya umarci Musa ya ce,

38 “Ka faɗa wa Isra’ilawa su yi wa shafin rigunansu tuntaye a dukan zamananku. A kan kowane tuntu, su sa shuɗin zare.

39 Tuntu zai zama musu abin dubawa don su riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji su aikata su, don kada su bi son zuciyarsu, da sha’awar idanunsu yadda suka taɓa yi.

40 Da haka za su riƙa tunawa, su aikata dukan umarnaina su zama tsarkakakku gare ni.

41 Gama ni ne Ubangiji Allahnku, na fisshe ku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Categories
L. KID

L. KID 16

Tayarwar Kora, da Datan, da Abiram

1-2 Sai Kora, ɗan Izhara, na kabilar Lawi, iyalin Kohat, ya yi ƙarfin hali ya tayar wa Musa. Waɗansu uku kuma daga kabilar Ra’ubainu suka haɗa kai da shi, su ne Datan da Abiram, ‘ya’yan Eliyab, da On,ɗan Felet, da waɗansu Isra’ilawa su ɗari biyu da hamsin, sanannun shugabanni da jama’a suka zaɓa.

3 Suka taru a gaban Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun cika izgili, gama dukan taron jama’a na Ubangiji ne, Ubangiji kuwa yana tare da su. Me ya sa kai Musa ka aza kanka shugaba a kan taron jama’ar Ubangiji?”

4 Da Musa ya ji wannan, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a.

5 Sa’an nan ya ce wa Kora da ƙungiyarsa, “Da safe Ubangiji zai nuna mana wanda yake nasa, zai sa wanda yake nasa, wato wanda ya zaɓa, ya sadu da shi a bagade.

6 Kai, Kora da ƙungiyarka duka, gobe, sai ku ɗauki farantan ƙona turare.

7 Ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan ne za mu ga wanda Ubangiji ya zaɓa tsakaninmu. Ku Lawiyawa ku ne kuka fi fiffiƙewa!”

8 Musa ya ci gaba da magana da Kora. “Ku Lawiyawa ku kasa kunne!

9 Kuna ganin wannan ƙaramar magana ce, wato cewa Allah na Isra’ila ya keɓe ku daga cikin jama’ar Isra’ila domin ya kawo ku kusa da shi, ku yi aiki a alfarwar sujada ta Ubangiji, ku kuma tsaya a gaban jama’a don ku yi musu aiki?

10 Ya yarda ka zo kusa da shi, kai da dukan ‘yan’uwanka Lawiyawa, a yanzu kuwa sai ƙoƙari kuke ku karɓi aikin firist!

11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji!”

12 Musa kuwa ya aika a kirawo Datan da Abiram, ‘ya’yan Eliyab, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!

13 Kana jin ƙaramin abu ne da ka fitar da mu daga cikin ƙasar mai yalwar abinci, don ka kashe mu a jeji? So kake kuma ka mai da kanka sarki a bisanmu?

14 Banda wannan kuma, ga shi, ba ka kai mu zuwa cikin ƙasa mai yalwar abinci ba, ba ka ba mu gonaki da gonakin inabi domin mu gāda ba, yanzu kuwa kana so ka ruɗe mu, to, ba za mu zo ba sam!”

15 Musa kuwa ya husata ƙawarai da gaske, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace ko jakinsu ba, ban kuwa cuce su ba.”

16 Musa ya ce wa Kora, “Kai da ƙungiyarka duka ku hallara a gaban Ubangiji gobe, da kai, da su, da Haruna.

17 Sa’an nan kowane ɗayanku ya ɗauki farantinsa na ƙona turare, ya zuba turaren wuta a ciki, ya kawo a gaban Ubangiji, wato farantan ƙona turare guda ɗari biyu da hamsin ke nan. Kai kuma da Haruna kowannenku ya kawo nasa faranti.”

18 Sai kowannensu ya ɗauki farantinsa, ya zuba wuta a ciki, sa’an nan ya zuba turaren wuta, suka tsaitsaya a bakin ƙofar alfarwa ta sujada tare da Musa da Haruna.

19 Sai Kora ya tara dukan taron jama’a a bakin alfarwa ta sujada, ya zuga su su tayar wa Musa, da Haruna. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron jama’ar.

20 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna,

21 “Ku ware kanku daga cikin taron jama’ar nan, ni kuwa in hallaka su nan take.”

22 Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki, suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin ‘yan adam duka, za ka yi fushi da dukan taron jama’a saboda zunubin mutum ɗaya?”

23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

24 “Ka faɗa wa jama’a su tashi, su nisanci alfarwar Kora, da ta Datan, da ta Abiram.”

25 Musa kuwa ya tashi ya tafi wurin Datan, da Abiram Dattawan Isra’ilawa suka bi Musa.

26 Sai ya ce wa jama’ar, “Ina roƙonku, ku ƙaurace wa alfarwan waɗannan mugayen mutane, kada ku taɓa kowane abu da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”

27 Sai jama’a suka tashi daga inda Kora, da Datan, da Abiram suke zama.

Datan da Abiram kuwa suka fito suka tsaya a ƙofar alfarwansu tare da matansu da ‘ya’yansu, da ‘yan ƙananansu.

28 Sai Musa ya ce, “Da haka za ku sani Ubangiji ne ya aiko ni, in yi waɗannan ayyuka, ba da nufin kaina na yi su ba.

29 Idan mutanen nan sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, idan abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.

30 Amma idan Ubangiji ya aikata wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara zuwa cikin lahira a raye, sa’an nan za ku sani mutanen nan sun raina Ubangiji.”

31 Musa ya rufe bakinsa ke nan, sai wurin da Datan da Abiram suke tsaye, ƙasar ta dāre

32 ta haɗiye su tare da iyalansu, da dukan mutanen Kora, da dukan mallakarsu.

33 Haka fa, su da dukan abin da yake nasu suka gangara zuwa lahira da rai.

34 Sai Isra’ilawa duka waɗanda suke kewaye da su suka gudu saboda kururuwansu, suka ce. “Mu mā gudu,kada kuma ƙasa ta haɗiye mu.”

35 Wuta kuma ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutum ɗari biyu da hamsin ɗin nan da suke miƙa hadaya da turare.

36 Ubangiji ya ce wa Musa,

37 “Ka faɗa wa Ele’azara, ɗan Haruna firist, ya kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, ka watsar da gawayin daga farantan a wani wuri gama farantan tsarkakakku ne.

38 Waɗannan farantan ƙona turaren sun zama tsarkakakku sa’ad da aka miƙa su a bagaden Ubangiji. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo, musu mutuwa, ka ƙera murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, ta haka za su zama gargaɗi ga jama’ar Isra’ila.”

39 Sai Ele’azara, firist, ya ɗauki farantan tagullar waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo. Aka ƙera murfin bagade da su.

40 Zai zama abin tunawa ga Isra’ilawa domin kada wanda ba firist ba, ba kuwa a cikin zuriyar Haruna ba, ya guso don ya ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada ya zama kamar Kora da ƙungiyarsa. Haka Ubangiji ya faɗa wa Ele’azara ta bakin Musa.

Haruna ya Ceci Jama’a

41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, suna cewa, “Ku ne sanadin mutuwar jama’ar Ubangiji.”

42 Da taron jama’ar suka haɗa kai gāba da Musa da Haruna, sai suka fuskanci alfarwa ta sujada. Ga girgije yana rufe da alfarwar, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta bayyana.

43 Sai Musa da Haruna suka tafi wajen ƙofar alfarwa ta sujada.

44 Ubangiji kuwa ya yi magana da Musa, ya ce,

45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzun nan zan hallaka su.”

Sai suka fāɗi rubda ciki.

46 Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna, “Ɗauki farantin turare, ka cika shi da wuta daga bagade, ka zuba turaren wuta a ciki, ka tafi da sauri wurin taron, ka yi kafara dominsu, gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko, an fara annoba.”

47 Sai Haruna ya ɗauko farantin turaren, ya yi yadda Musa ya ce. Ya sheƙa a guje a tsakiyar taron jama’a. Amma an riga an fara annobar a cikin jama’a. Sai ya zuba turare, ya yi kafara domin jama’a.

48 Ya kuwa tsaya a tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.

49 Waɗanda annoba ta kashe mutum dubu goma sha huɗu ne da ɗari bakwai (14,700), banda waɗanda suka mutu a sanadin Kora.

50 Sai Haruna ya koma wurin Musa a ƙofar alfarwa ta sujada, gama annobar ta ƙare.

Categories
L. KID

L. KID 17

Sandan Haruna

1 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,

2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa su ba ka sanduna, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu, sanduna goma sha biyu ke nan. Ka rubuta sunan kowane mutum a sandansa.

3 Ka rubuta sunan Haruna a kan sandan Lawi, gama akwai sanda guda domin kowane gidan kakanninsu.

4 Sai ka ajiye su a alfarwa ta sujada a gaban akwatin alkawari, inda nakan sadu da kai.

5 Mutumin da sandansa ya yi toho, shi ne na zaɓa, da haka zan sa gunagunin da Isra’ilawa suke yi a kaina ya ƙare.”

6 Musa kuwa ya yi magana da Isra’ilawa. Sai dukan shugabanninsu suka ba shi sanda ɗaya ɗaya, sanda ɗaya daga kowane shugaba bisa ga gidajen kakanninsu, sanduna goma sha biyu ke nan. Sandan Haruna yana cikin sandunan.

7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji cikin alfarwa ta sujada.

8 Kashegari Musa ya shiga alfarwar, sai ga shi, sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya huda, ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi ‘ya’yan almon nunannu, wato wani irin itace ne mai kama da na yazawa.

9 Musa kuwa ya fito wa Isra’ilawa da dukan sandunan da aka ajiye a gaban Ubangiji. Suka duba, kowanne ya ɗauki sandansa.

10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Mayar da sandan Haruna a akwatin alkawari, alama ce ga masu tawaye ta cewa za su mutu idan ba su daina gunaguninsu ba.”

11 Haka kuwa Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi.

12 Isra’ilawa suka ce wa Musa, “Ba shakka, mun hallaka. Mun lalace, dukanmu mun lalace.

13 Duk wanda ya kusaci alfarwa ta sujada ta Ubangiji, zai mutu. Ashe, dukanmu za mu mutu ke nan!”

Categories
L. KID

L. KID 18

Ayyukan Lawiyawa da Firistoci

1 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da ‘ya’yanka, da gidan mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi alfarwa ta sujada. Kai da ‘ya’yanka kuma za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.

2 Ka kawo ‘yan’uwanka tare da kai, wato kabilar Lawi, kakanka, don su yi muku aiki sa’ad da kai da ‘ya’yanka kuke gaban alfarwa ta sujada.

3 Za su taimake ku, su kuma yi dukan ayyukan alfarwa. Amma fa, ba za su kusaci kayayyakin Wuri Mai Tsarki, ko bagade ba, don kada su, har da ku, ku mutu.

4 Za su haɗa kai da ku su lura da alfarwa ta sujada da dukan aikace-aikace na cikin alfarwar. Kada wani dabam ya kusace ku.

5 Ku lura da ayyukan Wuri Mai Tsarki da na bagade don kada hasala ta sāke fāɗa wa Isra’ilawa.

6 Ga shi, ni na ɗauki ‘yan’uwanku, Lawiyawa, daga cikin mutanen Isra’ila. Kyauta suke a gare ku, waɗanda aka bayar ga Ubangiji don su lura da alfarwa ta sujada.

7 Da kai, da ‘ya’yanka za ku yi aikin firist da duk abin da ya shafi bagade da aiki na bayan labule. Ku ne za ku yi wannan aiki. Na ba ku aikin firist ya zama naku. Duk wani dabam wanda ya zo kuwa, za a kashe shi.”

Rabon Firistoci

8 Ubangiji ya kuma ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayuna na ɗagawa, wato sadakokin Isra’ilawa, na ba ka su su zama rabonka da na ‘ya’yanka har abada.

9 Abin da ya ragu daga cikin hadaya mafi tsarki da ake miƙa mini zai zama rabonka da na ‘ya’yanka, wato daga kowace hadaya, da hadaya ta gari, da hadaya don zunubi, da hadaya don laifi.

10 A wuri mai tsarki za ku ci shi, kowane namiji ya iya ci. Abu mai tsarki ne a gare ka.

11 “Har yanzu kuma duk sadakokin da Isra’ilawa suke bayarwa don hadaya ta ɗagawa da ta kaɗawa, na ba ka, kai da ‘ya’yanka mata da maza, a kowane lokaci. Duk wanda yake da tsarki a gidanka zai iya ci.

12 “Duk mai mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan fari, waɗanda suke bayarwa ga Ubangiji, na ba ku.

13 Nunan fari na dukan amfanin gonarsu wanda suke kawowa ga Ubangiji, zai zama naka. Duk wanda yake da tsarki a gidanka zai iya cinsa.

14 “Iyakar abin da aka keɓe wa Ubangiji a Isra’ila zai zama naka.

15 “Dukan haihuwar fari, ko ta mutum ko ta dabba da sukan bayar ga Ubangiji zai zama naka. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.

16 Sai ka fanshe su suna ‘yan wata ɗaya a bakin shekel biyar biyar, bisa ga ma’aunin kuɗin da ake aiki da shi.

17 Haihuwar fari ta saniya, ko ta tunkiya, ko ta akuya, ba za ka fanshe su ba, gama su halal ne. Sai kayayyafa jininsu a kan bagade, kitsensu kuma ka ƙone a kan bagaden ƙona hadayu, zai zama turare mai ƙanshi, mai daɗi ga Ubangiji.

18 Naman kuwa zai zama naka, duk da ƙirji na kaɗawa da cinyar dama da aka miƙa su hadaya ta kaɗawa.

19 “Duk hadayu na ɗagawa na tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da ‘ya’yanka mata da maza a kowane lokaci. Wannan alkawarin gishiri ne na Ubangiji dominka da zuriyarka.”

20 Ubangiji kuma ya ce wa Haruna, “Ba za ka gāji kome a ƙasar Isra’ilawa ba, ba ka da wani rabo a cikinta. Ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.”

Rabon Lawiyawa

21 Ubangiji ya ce, “Na ba Lawiyawa kowace zaka ta Isra’ilawa gādo saboda aikinsu da suke ya a alfarwa ta sujada.

22 Nan gaba kada Isra’ilawa su zo kusa da alfarwa ta sujada don kada su yi zunubi, su mutu.

23 Gama Lawiyawa ne kaɗai za su yi aikin alfarwa ta sujada, wannan alhakinsu ne. Wajibi ne kuma ga zuriyarsu a kowane lokaci. Lawiyawa ba su da gādo tare da Isra’ilawa.

24 Gama ni Ubangiji na ba su zaka da Isra’ilawa suke kawo mini ta hadaya ta ɗagawa ta zama gādonsu. Saboda haka ne, na ce ba su da gādo tare da Isra’ilawa.”

Zaka

25 Ubangiji ya ce wa Musa,

26 “Har yanzu ka faɗa wa Lawiyawa, cewa sa’ad da suka karɓi zaka daga Isra’ilawa wadda na ba su gādo, sai su fitar da zaka daga cikin zakar, su miƙa wa Ubangiji hadaya ta ɗagawa.

27 Za a lasafta hadayarku ta ɗagawa kamar hatsinku ne da kuka sussuka a masussuka, da kuma kamar cikakken amfanin ruwan inabin da kuka samu a wurin matsewar inabinku.

28 Haka za ku miƙa hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji daga cikin dukan zakar da kuke karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga ciki za ku ba da hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji ta hannun Haruna, firist.

29 Daga dukan kyautar da ake kawo muku, za ku ba Ubangiji hadaya ta ɗagawa daga mafi kyau da kuke samu.

30 Domin haka kuwa sai ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka ɗaga mafi kyau daga cikinta duka, sai ragowar ta zama ta Lawiyawa kamar abin da ya fito daga masussuka, da wurin matsewar inabinsu.

31 Za ku iya cinta ko’ina da kuka ga dama, ku da iyalan gidajenku, gama ladanku ke nan saboda aikin da kuke yi a alfarwa ta sujada.

32 Ba kuwa za ta zama muku sanadin zunubi ba, in dai har kuka ɗaga mafi kyau duka. Ba za ku ɓata tsarkakakkun abubuwa na Isra’ilawa ba, don kada ku mutu.’ ”

Categories
L. KID

L. KID 19

Tsarkakewar Marasa Tsarki

1 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna, ya ce,

2 “Wannan ita ce ka’ida wadda Ubangiji ya umarta. Ka faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jar karsana, marar lahani, wadda ba ta da wani aibi, wadda ba a taɓa aza mata karkiya ba.

3 Sai ka ba Ele’azara firist ita, sa’an nan a kai ta bayan sansani, a yanka ta gabansa.

4 Ele’azara, firist, kuwa zai ɗibi jininta da yatsansa, ya yayyafa sau bakwai a wajen alfarwar ta sujada.

5 Sai a ƙone karsanar a idonsa, za a ƙone fatarta, da naman, da jinin, tare da tarosonta.

6 Firist zai ɗauki itacen al’ul, da ɗaɗɗoya, da mulufi, ya jefa a wutar da take ƙone karsanar.

7 Sai firist ɗin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, sa’an nan ya shiga zangon. Firist ɗin zai ƙazantu har zuwa maraice.

8 Shi kuma wanda ya ƙone karsanar, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, shi ma zai ƙazantu har zuwa maraice.

9 Mutumin da yake da tsarki shi zai tara tokar karsanar, ya ajiye a wuri mai tsabta a bayan zangon. Za a adana tokar domin jama’ar Isra’ila, za a riƙa zubawa a ruwa don tsarkakewar zunubi.

10 Shi kuma wanda ya tara tokar karsanar, sai ya wanke tufafinsa zai ƙazantu har maraice. Wannan ka’ida ce ta har abada ga Isra’ilawa da baƙin da yake zama tare da su.”

Taɓa Gawa

11 “Duk wanda ya taɓa gawa zai ƙazantu har kwana bakwai.

12 A rana ta uku da ta bakwai zai tsarkake kansa da ruwa, zai kuwa tsarkaka, amma in a rana ta uku da ta bakwai bai tsarkake kansa ba, to, ba zai tsarkaka ba.

13 Duk wanda ya taɓa gawa, bai kuwa tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da alfarwa ta sujada ta Ubangiji, ba za a lasafta shi cikin mutanen Allah ba, domin ba a yayyafa masa ruwan tsarkakewa ba.

14 “Wannan ita ce ka’ida a kan wanda ya rasu a alfarwa, duk wanda ya shiga alfarwar, da duk wanda yake cikin alfarwar zai ƙazantu har kwana bakwai.

15 Kowace buɗaɗɗiyarsa kuma wadda ba a rufe ba, za ta ƙazantu.

16 Wanda duk yake cikin saura ya taɓa wanda aka kashe da tokobi, ko gawa, ko ƙashin mutum, ko kabari zai ƙazantu har kwana bakwai.

17 “Don a tsarkake ƙazantar, sai a ɗiba daga cikin tokar hadaya don zunubi a cikinsa, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu.

18 Tsarkakakken mutum zai ɗauki ɗaɗɗoya ya tsoma a ruwan, ya yayyafa wa alfarwar, da bisa kan dukan kayayyakin da suke ciki, da a kan mutanen da suke a wurin, da kan wanda ya taɓa ƙashin, ko ya taɓa wanda aka kashe, ko ya taɓa gawa, ko kabari.

19 A kan rana ta uku da ta bakwai kuma, wanda yake da tsarki zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, ya tsarkake shi. Sai mutumin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, da maraice kuwa zai tsarkaka.

20 “Amma mutumin da ba shi da tsarki, bai kuwa tsarkake kansa ba, ba za a lasafta shi cikin jama’ar Allah ba, tun da yake ya ƙazantar da alfarwa ta sujada ta Ubangiji, gama ba a yayyafa masa ruwan da akan yayyafa wa marasa tsarki ba.

21 Wannan zai zama musu ka’ida har abada. Wanda ya yayyafa ruwan tsarkakewa, sai ya wanke tufafinsa, wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa zai zama marar tsarki har maraice.

22 Duk abin da mutumin da ba shi da tsarki ya taɓa zai ƙazantu, duk wanda kuma ya taɓa abin da marar tsarkin ya taɓa zai ƙazantu har maraice.”

Categories
L. KID

L. KID 20

Ruwa daga cikin Dutse

1 Sai dukan taron jama’ar Isra’ilawa suka zo jejin Zin a watan fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Maryamu ta rasu, a nan kuma aka binne ta.

2 Da jama’a suka rasa ruwa, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna.

3 Suka ce wa Musa, “Da ma mun mutu kamar yadda ‘yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji.

4 Don me ka fito da taron jama’ar Ubangiji zuwa cikin wannan jeji don mu mutu a nan, mu da dabbobinmu?

5 Don me kuma ka sa muka fito daga masar, ka kawo mu a wannan mugun wuri inda babu hatsi, ko ɓaure, ko inabi, ko rumman, ko ruwan da za a sha ma?”

6 Sai Musa da Haruna suka bar taron jama’a, suka tafi ƙofar alfarwa ta sujada, suka fāɗi rubda ciki. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta bayyana a gare su.

7 Ubangiji ya ce wa Musa,

8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”

9 Musa kuwa ya ɗauki sanda daga gaban Ubangiji kamar yadda ya umarce shi.

10 Sai Musa da Haruna suka sa jama’a su taru a gaban dutsen, sa’an nan Musa ya ce musu, “Ku kasa kunne, ku ‘yan tawaye, za mu fito muku da ruwa daga cikin dutsen nan?”

11 Musa kuwa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa, sai ruwa mai yawa ya yi ta kwararowa. Taron jama’a tare da garkunansu suka sha.

12 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna, “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’ar nan a ƙasar da na ba su ba.”

13 Wannan ya faru ne a Meriba inda mutanen Isra’ila suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda shi kuma ya nuna musu shi mai tsarki ne.

Sarkin Edom ya Hana Isra’ilawa Wucewa

14 Sai Musa ya aika manzanni daga Kadesh zuwa wurin Sarkin Edom, su ce masa, “In ji ɗan’uwanka, Isra’ila, ka dai san dukan wahalar da ta same mu,

15 yadda kakanninmu suka gangara zuwa Masar, suka zauna a can da daɗewa, da yadda Masarawa suka wahalshe mu, mu da kakanninmu.

16 Sa’ad da muka yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya aiko mala’ikansa, ya fisshe mu daga Masar. Ga mu nan a Kadesh, garin da yake kan iyakar ƙasarka.

17 Ka yarda mana mu ratsa ƙasarka, ba za mu bi ta cikin gona, ko gonar inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba. Mu dai za mu bi gwadaben sarki, ba za mu kauce dama ko hagu ba, har mu wuce ƙasarka.”

18 Amma Edomawa suka ce masa, “Ba za ku ratsa ta ƙasarmu ba! Idan kuwa kun ce za ku gwada, za mu fita mu ci ku da yaƙi.”

19 Amma mutanen Isra’ila suka amsa musu suka ce, “Ai, za mu bi gwadabe ne kawai, idan kuwa mu da dabbobinmu mun sha ruwanku, sai mu biya, mu dai, a yardar mana mu wuce kawai.”

20 Amma Edomawa suka sāke cewa, “Ba mu yarda ba.” Sai suka fito da runduna mai yawa su yi yaƙi da su.

21 Da haka Edomawa suka hana Isra’ilawa ratsa ƙasarsu. Sai Isra’ilawa suka kauce musu.

Haruna ya Rasu

22-23 Sai taron jama’ar Isra’ila suka kama tafiya daga Kadesh, suka je Dutsen Hor, a kan iyakar ƙasar Edom. Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna a can,

24 “Haruna ba zai shiga ƙasar da na alkawarta zan ba Isra’ila ba, zai mutu, gama ku biyun nan kuka tayar wa umarnina a Meriba.

25 Ka kawo Haruna da ɗansa, Ele’azara, bisa Dutsen Hor.

26 Ka tuɓe wa Haruna rigunansa na firist, ka sa wa ɗansa, Ele’azara. Haruna zai mutu can.”

27 Musa kuwa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau bisa Dutsen Hor a idon dukan taron jama’a.

28 Sai Musa ya tuɓe wa Haruna rigunansa na firist ya sa wa Ele’azara ɗan Haruna. Haruna kuwa ya rasu a kan dutsen. Sa’an nan Musa da Ele’azara suka sauko daga kan dutsen.

29 Sa’ad da dukan jama’a suka ga Haruna ya rasu, sai duka suka yi makoki dominsa har kwana talatin.

Categories
L. KID

L. KID 21

An ci Kan’aniyawa da Yaƙi

1 Da Sarkin Arad, Bakan’ane, wanda yake zaune a Negeb, ya ji Isra’ilawa suna zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fita ya yi yaƙi da Isra’ilawa, ya kama waɗansu daga cikinsu.

2 Sai Isra’ilawa suka yi wa’adi ga Ubangiji, suka ce, “In hakika, za ka ba da mutanen nan a hannunmu, lalle za mu hallaka biranensu ƙaƙaf.”

3 Ubangiji kuwa ya ji wa’adin Isra’ilawa, ya kuwa ba su Kan’aniyawa, suka hallaka su da biranensu ƙaƙaf. Don haka aka sa wa wurin suna Horma, wato hallakarwa.

Macijin da aka Yi da Tagulla

4 Isra’ilawa suka kama hanya daga Dutsen Hor zuwa Bahar Maliya don su kauce wa ƙasar Edom. Sai jama’a suka ƙosa da hanyar.

5 Suka yi wa Allah gunaguni, da Musa kuma, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu cikin jeji mu mutu? Gama ba abinci, ba ruwa, mu kuwa mun gundura da wannan abinci marar amfani.”

6 Sai Ubangiji ya aiko macizai masu zafin dafi a cikin jama’a, suka sassari Isra’ilawa, da yawa kuwa suka mutu.

7 Jama’a kuwa suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi gama mun yi wa Ubangiji gunaguni, mun kuma yi maka. Ka roƙi Ubangiji ya kawar mana da macizan.” Musa kuwa ya yi roƙo domin jama’ar.

8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera maciji da tagulla, ka sarƙafa shi a bisa dirka, duk wanda maciji ya sare shi, idan ya dubi maciji na tagullar, zai rayu.”

9 Musa kuwa ya yi maciji na tagulla, ya sarƙafa shi a bisa dirka, idan kuwa maciji ya sari mutum, in ya dubi macijin tagullar, zai warke.

Tafiya zuwa Kwarin Mowabawa

10 Sai mutanen Isra’ila suka kama hanya, suka yi zango a Obot.

11 Suka kama hanya daga Obot, suka yi zango a kufafen Abarim a cikin jeji daura da Mowab wajen gabas.

12 Daga can suka tashi suka sauka a Kwarin Zered.

13 Daga can kuma suka tashi suka sauka hayin Kogin Arnon, wanda yake cikin jeji wanda ya nausa zuwa iyakar Amoriyawa. Gama Arnon shi ne kan iyakar Mowabawa da Amoriyawa.

14 Saboda haka aka faɗa a Littafin Yaƙoƙi na Ubangiji cewa, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na Kogin Arnon,

15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”

16 Daga can suka ci gaba da tafiya zuwa Biyer, wato rijiya wadda Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane wuri ɗaya, zan kuwa ba su ruwa.”

17 Sai Isra’ilawa suka raira waƙa, suka ce,

“Rijiya, ki ɓuɓɓugo da ruwa

Mu kuwa za mu raira waƙa mu gaishe ta!

18 Rijiyar da hakimai suka haƙa,

Shugabannin jama’a suka haƙa,

Da sandan sarauta,

Da kuma sandunansu.”

Daga cikin jejin suka tafi har zuwa Mattana.

19 Daga Mattana suka tafi Nahaliyel suka tafi Bamot.

20 Daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake a ƙasar Mowab wajen ƙwanƙolin Dutsen Fisga wanda yake fuskantar hamada.

Mutanen Isra’ila sun Ci Sihon

21 Mutanen suka aiki manzanni zuwa wurin Sihon, Sarkin Amoriyawa, suka ce masa,

22 “Ka yarda mana mu ratsa ta ƙasarka, ba za mu ratsa ta cikin gonaki, ko cikin gonakin inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba, gwadaben sarki za mu bi sosai, har mu fita daga karkararka.”

23 Amma Sihon bai yarda wa Isra’ilawa su ratsa ta karkararsa ba. Sai ya tattara mazajensa, suka fita don su yi yaƙi da Isra’ilawa a jejin. Suka tafi Yahaza suka yi yaƙi da Isra’ilawa.

24 Isra’ilawa kuwa suka karkashe su da takobi, suka mallaki ƙasarsa tun daga Kogin Arnon zuwa Kogin Yabbok, har zuwa kan iyakar Ammonawa, gama Yahaza ita ce kan iyakar Ammonawa.

25 Isra’ilawa kuwa suka ci dukan waɗannan birane, suka zauna a biranen Amoriyawa, wato a Heshbon da ƙauyukanta duka.

26 Gama Heshbon ita ce birnin Sihon,Sarkin Amoriyawa, wanda ya yi yaƙi da Sarkin Mowab na dā. Ya ƙwace ƙasarsa duka daga hannunsa har zuwa Kogin Arnon.

27 Domin haka mawaƙa sukan ce,

“Ku zo Heshbon, bārin sarki Sihon!

Muna so mu ga an sāke gina an kuma fanso shi.

28 Gama sojojin Sihon sun shiga kamar wuta,

A wannan birni na Heshbon,

Sun cinye Ar ta Mowab,

Ta murƙushe tuddan Arnon.

29 Kaitonku, ku mutanen Mowab!

Ku masu sujada ga Kemosh kun lalace!

Gumakanku sun sa mutane su zama ‘yan gudun hijira,

Mata kuwa, Sihon, Sarkin Amoriyawa ya kama su.

30 Amma yanzu an hallaka zuriyarsu,

Tun daga Heshbon har zuwa Dibon,

Har da Nofa kusa da Medeba.”

Isra’ilawa sun Ci Og

31 Haka fa Isra’ilawa suka zauna a ƙasar Amoriyawa.

32 Sai Musa ya aika a leƙo asirin ƙasar Yazar. Suka tafi suka ci ƙauyukanta, suka kori Amoriyawan da suke can.

33 Suka juya suka haura ta hanyar Bashan. Sai Og, Sarkin Bashan, da dukan jama’arsa suka fita, suka yi yaƙi da su a Edirai.

34 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na bashe shi a hannunka duk da jama’arsa, da ƙasarsa. Za ka yi masa yadda ka yi wa Sihon, Sarkin Amoriyawa wanda ya zauna a Heshbon.”

35 Haka fa suka kashe shi, shi da ‘ya’yansa maza, da dukan jama’arsa, har ba wanda ya tsira, suka kuwa mallaki ƙasarsa.

Categories
L. KID

L. KID 22

Balak ya Sa a Kirawo masa Bal’amu

1 Isra’ilawa suka kama tafiya, suka yi zango a filayen Mowab a hayin Urdun daura da Yariko.

2 Balak ɗan Ziffor ya ga abin da Isra’ilawa suka yi wa Amoriyawa.

3 Sai Mowabawa suka firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra’ilawa ya kama su.

4 Mowabawa kuwa suka ce wa dattawan Madayanawa, “Yanzun nan wannan taro zai lashe dukan abin da yake kewaye da mu kamar yadda sā yakan lashe ciyawar saura.” Don haka Balak ɗan Ziffor wanda yake sarautar Mowab a lokacin,

5 ya aiki manzanni zuwa wurin Bal’amu ɗan Beyor a Fetor, a ƙasar danginsa, wadda take kusa da kogin, su kirawo shi, su ce, “Ga mutane sun fito daga ƙasar Masar, sun mamaye ƙasar, ga shi, suna zaune daura da ni.

6 Ina roƙonka, ka zo yanzu, ka la’anta mini mutanen nan, gama sun fi ƙarfina, ko ya yiwu in ci su, in kore su daga ƙasar, gama na sani duk wanda ka sa wa albarka zai albarkatu,wanda kuwa ka la’anta, zai la’antu.”

7 Dattawan Mowab da na Madayana suka ɗauki kafin alkalami suka tafi wurin Bal’amu suka faɗa masa saƙon Balak.

8 Ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan shaida muku abin da Ubangiji zai faɗa mini.” Sai dattawan Mowab suka zauna wurin Bal’amu.

9 Allah kuwa ya zo wurin Bal’amu ya ce masa, “Suwane ne mutanen da suke tare da kai?”

10 Sai Bal’amu ya ce wa Allah, “Ai, Balak ne ɗan Ziffor, Sarkin Mowab, ya aiko ya ce mini,

11 ‘Ga jama’a sun fito daga Masar, sun mamaye ƙasar, ka zo, ka la’anta mini su, watakila zan iya yin yaƙi da su, in kore su!’ ”

12 Allah kuwa ya ce wa Bal’amu, “Ba za ka tafi tare da su ba, ba kuwa za ka la’anta su ba, gama albarkatattu ne su.”

13 Da safe Bal’amu ya tashi, ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, gama Ubangiji bai yarda mini in tafi tare da ku ba.”

14 Domin haka dattawan Mowab suka tashi, suka koma wurin Balak, suka ce masa, “Bal’amu bai yarda ya biyo mu ba.”

15 Sai Balak ya sāke aiken dattawa da yawa masu daraja fiye da na dā.

16 Suka je wurin Bal’amu, suka ce masa, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, ‘Kada ka bar wani abu ya hana ka zuwa wurina,

17 gama zan ɗaukaka ka ƙwarai, kome kuwa ka faɗa mini in yi, zan yi, ka zo ka la’anta mini wannan jama’a.’ ”

18 Amma Bal’amu ya amsa ya ce wa barorin Balak, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba.

19 Amma ina roƙonku ku kwana a nan yau har in san abin da Ubangiji zai faɗa mini.”

20 Sal Allah ya je wurin Bal’amu da dare, ya ce masa, “Idan mutanen nan sun zo kiranka ne, sai ka tashi, ka tafi tare da su, amma abin da na umarce ka kaɗai za ka yi.”

Mala’ika da Jakar Bal’amu

21 Da safe sai Bal’amu ya tashi ya yi wa jakarsa shimfiɗa, ya tafi tare da dattawan Mowab.

22 Allah kuwa ya husata don ya tafi, mala’ikan Ubangiji ya tsaya a hanya ya tarye shi. Shi kuwa yana tafe a bisa jakarsa tare da barorinsa biyu.

23 Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji yana tsaye kan hanya da takobi zare a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga saura. Bal’amu kuwa ya buge ta don ya komar da ita a hanyar.

24 Sai mala’ikan Ubangiji ya je, ya tsaya a inda hanyar ta yi matsatsi a tsakanin bangayen gonakin inabi.

25 Sa’ad da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, ta matsa a jikin bango, ta goge ƙafar Bal’amu ga bangon, sai ya sāke bugunta.

26 Mala’ikan Ubangiji kuma ya sha kanta, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa zuwa dama ko hagu.

27 Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙafafun Bal’amu. Sai Bal’amu ya husata, ya bugi jakar da sandansa.

28 Ubangiji kuwa ya buɗe bakin jakar, ta ce wa Bal’amu, “Me na yi maka, da ka buge ni har sau uku?”

29 Bal’amu ya ce mata, “Domin kin shashantar da ni, da a ce ina da takobi a hannuna, da na kashe ki.”

30 Sai jakar ta ce wa Bal’amu, “Ba ni ce jakarka ba wadda kake ta hawa dukan lokacin nan har zuwa yau? Na taɓa yi maka haka?”

Ya ce, “A’a.”

31 Ubangiji kuwa ya buɗe idanun Bal’amu, ya ga mala’ikan Ubangiji yana tsaye a hanya da takobi zāre a hannunsa. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki.

32 Mala’ikan Ubangiji kuwa ya ce masa, “Me ya sa ka bugi jakarka har sau uku? Na fito ne don inhana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana.

33 Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da ba ta kakuce mini ba, lalle da na kashe ka, in bar ta da rai.”

34 Sai Bal’amu ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Na yi zunubi, gama ban sa ka tsaya a hanya don ka tarye ni ba. Yanzu fa, idan ka ga mugun abu ne, to, sai in koma.”

35 Ubangiji kuwa ya ce wa Bal’amu, “Tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka shi kaɗai za ka faɗa.” Sai Bal’amu ya tafi tare da dattawan Balak.

Balak ya Marabci Bal’amu

36 Sa’ad da Balak ya ji Bal’amu ya zo, sai ya fito ya tarye shi a Ar, wato wani birni a bakin Kogin Arnon, a kan iyakar Mowab.

37 Sai Balak ya ce wa Bal’amu, “Ashe, ban aika a kirawo ka ba? Me ya sa ba ka zo wurina ba, sai yanzu? Ko ban isa in ɗaukaka ka ba ne?”

38 Bal’amu ya amsa wa Balak ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu! Ina da wani ikon yin wata magana ne? Maganar da Allah ya sa a bakina, ita zan faɗa, tilas.”

39 Sai Bal’amu ya tafi tare da Balak suka je Kiriyat-huzot.

40 Can Balak ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bal’amu da dattawan da suke tare da shi.

41 Kashegari, sai Balak ya ɗauki Bal’amu ya kai shi kan Bamotba’al, daga can ya ga rubu’in mutanen.

Categories
L. KID

L. KID 23

1 Sai Bal’amu ya ce wa Balak, “Ka gina mini bagadai guda bakwai a nan, ka kawo mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”

2 Balak ya yi yadda Bal’amu ya faɗa masa. Balak da Bal’amu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

3 Sai Bal’amu ya ce wa Balak, “Tsaya kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa zan tafi can, in ga ko Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Ya kuwa tafi wani faƙo a kan tudu.

Bal’amu ya sa wa Isra’ila Albarka

4 Da Ubangiji ya sadu da Bal’amu, sai Bal’amu ya ce wa Ubangiji, “Na riga na shirya bagadai bakwai, na kuwa miƙa bijimi guda da rago guda a kan kowane bagade.”

5 Ubangiji kuwa ya sa magana a bakin Bal’amu ya ce, “Koma wurin Balak, ka faɗa masa abin da na faɗa maka.”

6 Sai ya koma wurin Balak, ya same shi da dukan dattawan Mowab suna tsaye kusa da hadayarsa ta ƙonawa.

7 Bal’amu kuwa ya faɗi jawabinsa, ya ce

“Tun daga Aram Balak ya kawo ni,

Shi Sarkin Mowab ne daga gabashin duwatsu.

‘Zo, la’anta mini Yakubu,

Zo, ka tsine wa Isra’ila!’

8 Ƙaƙa zan iya la’anta wanda Allah bai la’antar ba?

Ƙaƙa zan iya tsine wa wanda Ubangiji bai tsine wa ba?

9 Gama daga kan duwatsu na gan su,

Daga bisa kan tuddai na hange su,

Jama’a ce wadda take zaune ita kaɗai,

Sun sani sun sami albarka fiye da sauran al’ummai.

10 Wa zai iya ƙidaya yawan Isra’ilawa da suke kamar ƙura?

Yawansu ya fi gaban lasaftawa.

Bari ƙarshena ya zama kamar ɗaya daga cikin mutane Allah,

Bari in mutu cikin salama kamar adalai.”

11 Sai Balak ya ce wa Bal’amu, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka domin ka la’anta abokan gābana, ga shi, sai albarka kake sa musu!”

12 Bal’amu kuwa ya ce, “Ai, ba tilas ne in hurta abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”

13 Sai Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su. Waɗanda suka fi kusa kaɗai ne za ka gani, amma ba za ka iya ganinsu duka ba. Ka la’anta mini su daga can.”

14 Ya kuwa kai shi saurar Zofim a bisa Dutsen Fisga. Sa’an nan ya gina bagadai bakwai, ya miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

15 Sai Bal’amu ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa in tafi in sadu da Ubangiji a can.”

16 Ubangiji kuwa ya sadu da Bal’amu ya sa masa magana a baka, ya ce, “Koma wurin Balak ka faɗa masa abin da na faɗa maka.”

17 Sai Bal’amu ya koma wurin Balak ya same shi yana tsaye kusa da hadayarsa ta ƙonawa tare da dattawan Mowab. Balak kuwa ya ce masa, “Me Ubangiji ya faɗa?”

18 Sai Bal’amu ya faɗi jawabinsa, ya ce,

“Tashi, Balak, ka ji,

Ka kasa kunne gare ni, ya ɗan Ziffor.

19 Allah ba kamar mutum ba ne, da zai yi ƙarya,

Ba kuwa ɗan mutum ba ne, da zai tuba.

Zai cika dukan abin da ya alkawarta,

Ya hurta, ya kuwa cika.

20 Ga shi, an umarce ni in sa albarka.

Ya sa albarka, ba zan iya janye ta ba.

21 Bai ga mugunta ga Yakubu ba,

Bai kuma ga wahala a Isra’ilawa ba.

Ubangiji Allahnsu yana tare da su,

Suna sowar murna domin shi sarkinsu ne.

22 Allah ne ya fisshe shi daga Masar,

Ya yi yaƙi dominsu kamar kutunkun ɓauna.

23 Ba wata maitar da za ta cuci Yakubu,

Ba kuwa sihirin da zai cuci Isra’ilawa.

Yanzu za a ce, ‘Duba irin abin da Allah ya yi domin Yakubu, wato Isra’ilawa!’

24 Ga shi, jama’ar Isra’ila tana kama da ƙaƙƙarfan zaki,

Ba zai kwanta ba sai ya cinye ganimarsa.

Ya lashe jinin waɗanda ya kashe.”

25 Sai Balak ya ce wa Bal’amu, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka.”

26 Bal’amu kuwa ya amsa wa Balak, ya ce, “Ban faɗa maka ba, duk abin da Ubangiji ya faɗa, shi ne zan yi?”

27 Sai Balak ya ce wa Bal’amu, “In ka yarda ka zo in kai ka wani wuri, watakila Allah zai yarda ka la’anta mini su a can.”

28 Balak kuwa ya kai Bal’amu a ƙwanƙolin Dutsen Feyor wanda yake fuskantar hamada.

29 Sai Bal’amu ya ce wa Balak, “Ka gina mini bagadai bakwai, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”

30 Balak ya yi yadda Bal’amu ya faɗa masa. Ya miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.