Categories
FAR

FAR 11

Hasumiyar Babila

1 A lokacin, harshen mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.

2 Sa’ad da mutane suke ta yin ƙaura daga gabas, sai suka sami fili a ƙasar Shinar, suka zauna a can.

3 Sai suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi aiki da tubali maimakon dutse, katsi kuma maimakon lāka.

4 Sai suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni, da hasumiya wadda ƙwanƙolinta zai kai can cikin sammai domin mu yi wa kanmu suna, domin kada mu warwatsu ko’ina bisa duniya.”

5 Ubangiji kuwa ya sauko ya ga birnin da hasumiyar da ‘yan adam suka gina.

6 Ubangiji kuwa ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne, to fa, ga irin abin da suka fara yi, ba abin da za su shawarta su yi da zai gagare su.

7 Zo mu sauka, mu dagula harshensu, domin kada su fahimci maganar juna.”

8 Haka kuwa daga wurin Ubangiji ya warwatsa su ko’ina bisa duniya, sai suka daina gina birnin.

9 Domin haka aka kira sunan wurin Babila, domin a nan ne Ubangiji ya dagula harshen dukan duniya, daga nan ne kuma Ubangiji ya warwatsa su ko’ina bisa duniya.

Zuriyar Shem

10 Waɗannan su ne zuriyar Shem. Lokacin da Shem yake da shekara ɗari, ya haifi Arfakshad bayan Ruwan Tsufana da shekara biyu.

11 Shem kuwa ya yi shekara ɗari biyar bayan haihuwar Arfakshad, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

12 Sa’ad da Arfakshad yake da shekara talatin da biyar ya haifi Shela.

13 Arfakshad kuwa ya yi shekara arbaminya da uku bayan haihuwar Shela, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

14 Sa’ad da Shela yake da shekara talatin, ya haifi Eber,

15 Shela kuwa ya yi shekara arbaminya da uku bayan haihuwar Eber, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

16 Sa’ad da Eber ya yi shekara talatin da huɗu ya haifi Feleg,

17 Eber kuwa ya yi shekara arbaminya da talatin, bayan haihuwar Feleg, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

18 Sa’ad da Feleg ya yi shekara talatin ya haifi Reyu.

19 Feleg ya yi shekara metan da tara bayan haihuwar Reyu, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

20 Sa’ad da Reyu ya yi shekara talatin da biyu ya haifi Serug.

21 Reyu kuwa ya yi shekara metan da bakwai bayan haihuwar Serug, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

22 Sa’ad da Serug ya yi shekara talatin ya haifi Nahor,

23 Serug kuwa ya yi shekara metan bayan haihuwar Nahor, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

24 Sa’ad da Nahor ya yi shekara ashirin da tara, ya haifi Tera,

25 Nahor kuwa ya yi shekara ɗari da goma sha tara bayan haihuwar Tera, ya kuma haifi ‘ya’ya mata da maza.

26 Sa’ad da Tera ya yi shekara saba’in, ya haifi Abram, da Nahor, da Haran.

27 Yanzu dai waɗannan su ne zuriyar Tera, Tera ya haifi Abram, da Nahor, da Haran, Haran kuwa shi ne ya haifi Lutu.

28 Haran kuwa ya rasu a idon mahaifinsa Tera a ƙasar haihuwarsa, a Ur ta Kaldiyawa.

29 Da Abram da Nahor suka yi aure, sunan matar Abram Saraya, sunan matar Nahor kuwa Milka, ita ‘yar Haran ce, mahaifin Milka da Iskaya.

30 Saraya kuwa ba ta haihuwa, wato ba ta da ɗa.

31 Sai Tera ya ɗauki ɗansa Abram da Lutu ɗan Haran, jikansa, da Saraya surukarsa, wato matar ɗansa Abram, suka tafi tare, daga Ur ta Kalidiyawa zuwa ƙasar Kan’ana, amma da suka isa Haran, suka zauna a can.

32 Kwanakin Tera shekara ce metan da biyar, Tera kuwa ya rasu a Haran.

Categories
FAR

FAR 12

Allah a Kira Abram

1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka fita daga ƙasarka, da danginka, da gidan mahaifinka zuwa ƙasar da zan nuna maka.

2 Zan kuwa maishe ka al’umma mai girma, zan sa maka albarka, in sa ka ka yi suna, domin ka zama sanadin albarka.

3 Waɗanda suka sa maka albarka zan sa musu albarka, amma zan la’anta waɗanda suka la’anta ka. Dukan al’umman duniya za su roƙe ni in sa musu albarka kamar yadda na sa maka.”

4 Abram kuwa ya kama hanya bisa ga faɗar Ubangiji, Lutu kuma ya tafi tare da shi, Abram yana da shekara saba’in da biyar sa’ad da ya yi ƙaura daga Haran.

5 Abram kuwa ya ɗauki matarsa Saraya da Lutu, ɗan ɗan’uwansa, da dukan dukiyarsu, da dukan mallakarsu waɗanda suka tattara a Haran.

Sa’ad da suka kai ƙasar Kan’ana,

6 Abram ya ratsa ƙasar zuwa Shekem, wurin itacen oak na More. A lokacin nan Kan’aniyawa suke a ƙasar.

7 Sai Ubangiji ya bayyana ga Abram, ya ce, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa.” Sai ya gina bagade ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.

8 Ya zakuɗa daga nan zuwa dutsen da yake gabashin Betel, ya kafa alfarwarsa, Betel tana yamma, Ai tana gabas, a nan ya gina wa Ubangiji bagade, ya kira bisa sunan Ubangiji.

9 Abram kuwa ya ci gaba da tafiya, ya nufi zuwa wajen Negeb.

Abram a Masar

10 A lokacin nan ana yunwa a ƙasar. Sai Abram ya tafi Masar baƙunci, gama yunwa ta tsananta a ƙasar.

11 Sa’ad da yake gab da shiga Masar, ya ce wa matarsa, Saraya, “Na sani ke kyakkyawar mace ce,

12 lokacin da Masarawa suka gan ki za su ce, ‘Wannan matarsa ce,’ za su kashe ni, amma za su bar ki da rai.

13 Ki ce ke ‘yar’uwata ce, domin dalilinki kome sai ya tafi mini daidai a kuma bar ni da raina.”

14 Sa’ad da Abram ya shiga Masar sai Masarawa suka ga matar kyakkyawa ce ƙwarai.

15 Da fādawan Fir’auna suka gan ta, sai suka yabe ta a gaban Fir’auna. Aka ɗauke ta aka kai ta gidan Fir’auna.

16 Saboda ita Fir’auna ya yi wa Abram alheri. Abram yana da tumaki, da takarkarai, da jakai maza, da barori mata da maza, da jakai mata, da raƙuma.

17 Sai Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da manya manyan annobai saboda matar Abram, Saraya.

18 Sai Fir’auna ya kirawo Abram, ya ce, “Mene ne wannan da ka yi mini? Don me ba ka faɗa mini ita matarka ce ba?

19 Don me ka ce ita ‘yar’uwarka ce, har na ɗauke ta ta zama matata? To, ga matarka, ka ɗauke ta ka tafi.”

20 Fir’auna kuma ya umarci mutanensa a kan Abram, su raka shi da matarsa, da dukan abin da yake da shi.

Categories
FAR

FAR 13

Rabuwar Abram da Lutu

1 Domin haka Abram ya bar Masar zuwa Negeb, shi da matarsa, da abin da yake da shi duka tare da Lutu.

2 Yanzu Abram ya arzuta da dabbobi, da azurfa, da zinariya.

3 Ya yi ta tafiya daga Negeb har zuwa Betel, har wurin da ya kafa alfarwarsa da fari, tsakanin Betel da Ai,

4 a inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.

5 Lutu wanda ya tafi tare da Abram, shi kuma yana da garkunan tumaki, da na shanu, da alfarwai,

6 domin haka ƙasar ba ta isa dukansu biyu su zauna tare ba, saboda mallakarsu ta cika yawa, har da ba za su iya zama tare ba.

7 Akwai rashin jituwa kuma a tsakanin makiyayan dabbobin Abram da makiyayan dabbobin Lutu. Mazaunan ƙasar, a lokacin nan Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.

8 Abram ya ce wa Lutu, “Kada rashin jituwa ya shiga tsakanina da kai ko tsakanin makiyayanka da nawa, gama mu ‘yan’uwa ne.

9 Ba ƙasar duka tana gabanka ba? Sai ka ware daga gare ni. In ka ɗauki hagu in ɗauki dama, in kuwa ka ɗauki dama ni sai in ɗauki hagu.”

10 Lutu ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, ga shi kuwa da dausayi mai kyau ƙwarai, sai ka ce gonar Ubangiji, kamar ƙasar Masar wajen Zowar, tun kafin Allah ya hallaka Saduma da Gwamrata.

11 Domin haka, Lutu ya zaɓar wa kansa kwarin Urdun duka, Lutu kuma ya kama hanya ya nufi gabas. Haka fa suka rabu da juna.

12 Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, Lutu kuwa ya zauna a biranen kwari, ya zakuɗar da alfarwarsa har zuwa Saduma.

13 Mutanen Saduma kuwa mugaye ne masu aikata zunubi ƙwarai gāba da Ubangiji.

Abram Ya Yi Ƙaura zuwa Hebron

14 Sai Ubangiji ya ce wa Abram, bayan da Lutu ya rabu da shi, “Ɗaga idanunka sama, daga inda kake, ka dubi kusurwoyin nan huɗu,

15 gama dukan ƙasan nan da kake gani kai zan ba, da zuriyarka har abada.

16 Zan mai da zuriyarka kamar turɓayar ƙasa, har in mutum ya iya ƙidaya turɓayar ƙasa, to, a iya ƙidaya zuriyarka.

17 Tashi, ka yi tafiya cikin ratar ƙasar da fāɗinta, gama zan ba ka ita.”

18 Sai Abram ya cire alfarwarsa, ya zo ya zauna kusa da itatuwan oak na Mamre, waɗanda suke Hebron. A can ya gina wa Ubangiji bagade.

Categories
FAR

FAR 14

Abram Ya ‘Yanto Lutu

1 A zamanin Amrafel Sarkin Shinar, shi da Ariyok Sarkin Ellasar, da Kedarlayomer Sarkin Elam, da Tidal Sarkin Goyim,

2 suka fita suka yi yaƙi da Bera Sarkin Saduma, da Birsha Sarkin Gwamrata, da Shinab Sarkin Adma, da Shemeber Sarkin Zeboyim, da kuma Sarkin Bela, wato Zowar.

3 Waɗannan sarakuna biyar suka haɗa kai don su kai yaƙi, suka haɗa mayaƙansu a kwarin Siddim, inda Tekun Gishiri take.

4 Shekara goma sha biyu suka bauta wa Kedarlayomer, amma suka tayar a shekara ta goma sha uku.

5 A shekara ta goma sha huɗu Kedarlayomer da sarakunan da suke tare da shi suka zo suka cinye Refayawa cikin Ashterotkarnayim, da Zuzawa cikin Ham, da Emawa cikin Filin Kiriyatayim,

6 da kuma Horiyawa cikin dutsen nan nasu, wato Seyir, har zuwa Elfaran a bakin jeji.

7 Sai suka juya suka je Enmishfat, wato Kadesh, suka kuwa cinye ƙasar Amalekawa da kuma ta Amoriyawa waɗanda suka zauna cikin Hazazontamar.

8-9 Sai Sarkin Saduma, da Sarkin Gwamrata, da Sarkin Adma da Sarkin Zeboyim, da Sarkin Bela, wato Zowar, suka fita suka ja dāga da Kedarlayomer Sarkin Elam, da Tidal Sarkin Goyim, da Amrafel Sarkin Shinar, da Ariyok Sarkin Ellasar a kwarin Siddim, sarakuna huɗu gāba da biyar.

10 Akwai ramummukan kalo da yawa a kwarin Siddim. Da Sarkin Saduma da na Gwamrata suka sheƙa da gudu sai waɗansunsu suka fāɗa cikin ramummukan, sauran kuwa suka gudu zuwa dutsen.

11 Sai abokan gāba suka kwashe dukan kayayyakin Saduma da na Gwamrata, da abincinsu duka, suka yi tafiyarsu.

12 Suka kuma kama Lutu ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Saduma, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.

13 Sai wani da ya tsere, ya zo ya faɗa wa Abram Ba’ibrane wanda yake zaune wajen itatuwan oak na Mamre, Ba’amore, ɗan’uwan Eshkol da Aner, waɗanda suke abuta da Abram.

14 Lokacin da Abram ya ji an kama danginsa wurin yaƙi sai ya shugabanci horarrun mutanensa, haifaffun gidansa, su ɗari uku da goma sha takwas, suka bi sawun sarakunan har zuwa Dan.

15 Da dad dare sai ya kasa jarumawansa yadda za su gabza da su, shi da barorinsa, ya kuma ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewacin Dimashƙu.

16 Sai ya washe kayayyakin duka, ya kuma ƙwato ɗan’uwansa Lutu da kayayyakinsa da mata da maza.

Malkisadik ya Sa wa Abram Albarka

17 Sai Sarkin Saduma ya fita ya taryi Abram sa’ad da ya komo daga korar Kedarlayomer da sarakunan da suke tare da shi, a Kwarin Shawe, wato Kwarin Sarki.

18 Sai Malkisadik Sarkin Salem, wato Urushalima, ya kawo gurasa da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Maɗaukaki.

19 Ya kuwa sa wa Abram albarka ya ce, “Shi wanda ya yi sama da ƙasa, Allah Maɗaukaki ya sa wa Abram albarka.

20 Ga Allah Maɗaukaki yabo ya tabbata, shi wanda ya ba ka maƙiyanka a tafin hannunka!” Abram kuwa ya ba shi ushiri na duka.

21 Sai Sarkin Saduma ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanen, amma ka riƙe kayayyakin don kanka.”

22 Amma Abram ya ce wa Sarkin Saduma, “Na riga na rantse wa Ubangiji Allah Maɗaukaki, wanda ya yi sama da ƙasa,

23 cewa ba zan ɗauki ko da zare ɗaya ko maɗaurin takalmi ba, ko kowane abin da yake naka, domin kada ka ce, ‘Na arzuta Abram.’

24 A ni kaina ba zan ɗauki kome ba illa abin da samari suka ci, da rabon mutanen da suka tafi tare da ni. Sai dai kuma Aner, da Eshkol, da Mamre su ɗauki nasu rabo.”

Categories
FAR

FAR 15

Alkawarin da yake Tsakanin Allah da Abram

1 Bayan waɗannan al’amura, maganar Ubangiji ta zo ga Abram cikin wahayi cewa, “Abram, kada ka ji tsoro, ni ne garkuwarka, kana da lada mai yawa.”

2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, me za ka ba ni, ga shi kuwa, ba ni da ɗa? Ko kuwa Eliyezer na Dimashƙu ne zai gāje ni?”

3 Abram kuma ya ce, “Ga shi, ba ka ba ni zuriya ba, ga shi ma wani yaron gidana ne zai gāje ni.”

4 Sai ga maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Mutumin nan, ba shi zai gāje ka ba, ɗan cikinka shi zai gāje ka.”

5 Sai Ubangiji ya fito da shi waje ya ce, “Ina so ka dubi sararin sama, ka kuma ƙidaya taurari, in kana iya ƙidaya su.” Sai kuma ya ce masa, “Haka zuriyarka za ta zama.”

6 Ya amince da Ubangiji, Ubangiji kuwa ya lasafta wannan adalci ne a gare shi.

7 Ubangiji kuma ya ce masa, “Ni ne Ubangiji wanda ya fisshe ka daga Ur ta Kaldiyawa, don in ba ka wannan ƙasa ka gāje ta.”

8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, yaya zan mallake ta?”

9 Ya ce masa, “Kawo mini karsana bana uku, da burguma bana uku, da rago bana uku, da hazbiya da ɗan tattabara.”

10 Ya kawo masa waɗannan abu duka, ya yanyanka su ya tsattsaga su a tsaka, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.

11 Sa’ad da tsuntsaye masu cin nama suke sauka bisansu sai Abram ya kore su.

12 Sa’ad da rana take faɗuwa, barci mai nauyi ya kwashe Abram, sai ga babban duhu mai bantsoro ya rufe shi.

13 Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani lalle ne zuriyarka za ta yi baƙunci cikin ƙasar da ba tata ba ce, za ta kuwa yi bauta, za a kuma tsananta mata har shekara arbaminya,

14 amma zan hukunta al’ummar da suka bauta wa, daga baya kuma da dukiya mai yawa za ta fita.

15 Kai kuwa, cikin salama za ka koma ga iyayenka, da kyakkyawan tsufa za a binne ka.

16 A tsara ta huɗu kuma, zuriyar za ta komo nan, domin adadin muguntar Amoriyawa bai cika ya kai iyaka ba tukuna.”

17 Sa’ad da rana ta fāɗi aka kuwa yi duhu, sai ga tanderun wuta mai hayaƙi da jiniya mai harshen wuta suka ratsa tsakanin abubuwan nan da aka tsattsaga a tsaka.

18 A wannan rana Ubangiji ya yi wa Abram alkawari ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga Kogin Masar zuwa babban kogi, wato Kogin Yufiretis ke nan,

19 ƙasar Keniyawa, da Kenizziyawa, da Kadmoniyawa,

20 da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Refayawa,

21 da Amoriyawa, da Kan’aniyawa, da Girgashiyawa, da kuma Yebusiyawa.”

Categories
FAR

FAR 16

Hajaratu da Isma’ilu

1 Saraya matar Abram ba ta taɓa haihuwa ba, amma tana da baranya Bamasariya, sunanta Hajaratu.

2 Sai Saraya ta ce wa Abram, “To, ga shi, Ubangiji ya hana mini haihuwar ‘ya’ya. Shiga wurin baranyata, mai yiwuwa ne in sami ‘ya’ya daga gare ta.” Abram kuwa ya saurari murya matarsa Saraya.

3 A lokacin nan kuwa Abram yana da shekara goma da zama a ƙasar Kan’ana sa’ad da Saraya matar Abram ta ɗauki Hajaratu Bamasariya, baranyarta, ta bai wa Abram mijinta ta zama matarsa.

4 Abram kuwa ya shiga wurin Hajaratu, ta kuwa yi ciki. Da ta ga ta sami ciki sai ta dubi uwargijiyarta a raine.

5 Sai Saraya ta ce wa Abram, “Bari cutar da aka cuce ni da ita ta koma kanka! Na ba da baranyata a ƙirjinka, amma da ta ga ta sami ciki, sai tana dubana a raine. Ubangiji ya shara’anta tsakanina da kai.”

6 Amma Abram ya ce wa Saraya, “Ga shi, baranyarki tana cikin ikonki, yi yadda kika ga dama da ita.” Saraya ta ƙanƙanta ta, sai Hajaratu ta gudu daga gare ta.

7 Mala’ikan Ubangiji kuwa ya sami Hajaratu a gefen wata maɓuɓɓugar ruwa a jeji, wato maɓuɓɓugar da take kan hanyar Shur.

8 Sai ya ce, “Ke Hajaratu, baranyar Saraya, ina kika fito, ina kuma za ki?”

Ta ce, “Gudu nake yi daga uwargijiyata Saraya.”

9 Mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki, ki yi mata ladabi.”

10 Mala’ikan Ubangiji kuma ya ce mata, “Zan riɓaɓɓanya zuriyarki ainun har da ba za a iya lasafta su ba saboda yawansu.”

11 Mala’ikan Ubangiji kuma ya ƙara ce mata, “Ga shi, kina da ciki, za ki haifi ɗa, za ki kira sunansa Isma’ilu, domin Ubangiji ya lura da wahalarki.

12 Zai zama mutum ne mai halin jakin jeji, hannunsa zai yi gāba da kowane mutum, hannun kowane mutum kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zaman magabtaka tsakaninsa da ‘yan’uwansa duka.”

13 Sai ta kira sunan Ubangiji wanda ya yi magana da ita, “Kai Allah ne mai gani,” gama ta ce, “Ni! Har na iya ganin Allah in rayu?”

14 Domin haka aka kira sunan rijiyar, Biyer-lahai-royi, tana nan tsakanin Kadesh da Bered.

15 Hajaratu ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya sa wa ɗa da Hajaratu ta haifa suna, Isma’ilu.

16 Abram yana da shekara tamanin da shida sa’ad da Hajaratu ta haifa masa Isma’ilu.

Categories
FAR

FAR 17

Kaciya ita ce Shaidar Alkawarin

1 A lokacin da Abram yake da shekara tasa’in da tara Ubangiji ya bayyana gare shi, ya ce masa, “Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka yi mini biyayya, ka zama kamili.

2 Zan yi maka alkawari, in ba ka zuriya mai yawa.”

3 Sai Abram ya yi ruku’u, Allah kuwa ya ce masa,

4 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi maka, za ka zama uba ga al’ummai masu ɗumbun yawa.

5 Ba za a ƙara kiran sunanka Abram ba, amma sunanka zai zama Ibrahim, gama na sa ka, ka zama uba ga al’ummai masu ɗumbun yawa.

6 Zan arzuta ka ainun, daga gare ka zan yi al’ummai, daga gare ka kuma sarakuna za su fito.

7 “Zan kafa alkawarina da kai, da zuriyarka a bayanka cikin dukan tsararrakinsu, madawwamin alkawari ke nan, in zama Allahnka da na zuriyarka a bayanka.

8 Zan ba ka, kai da zuriyarka a bayanka, ƙasar baƙuncinka, wato dukan ƙasar Kan’ana ta zama mallakarka har abada, ni kuwa zan zama Allahnsu.”

9 Allah kuma ya ce wa Ibrahim, “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, da kai da zuriyarka a bayanka cikin dukan tsararrakinsu.

10 Wannan shi ne alkawarina da za ka kiyaye, da kai da zuriyarka a bayanka. Sai a yi wa kowane ɗa namiji kaciya.

11 Loɓarku za ku yanke, don alamar alkawari a tsakanina da ku.

12 Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan tsararrakinku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.

13 Duka biyu, da wanda aka haifa daga gidanka, da wanda ka saya da kuɗi, za a yi musu kaciya. Da haka alkawarina zai kasance cikin jikinku, madawwamin alkawari ke nan.

14 Kowane ɗa namiji da bai yi kaciya ba, wato wanda bai yi kaciyar loɓarsa ba, za a fitar da shi daga jama’arsa, don ya ta da alkawarina.”

15 Allah ya ce wa Ibrahim, “Ga zancen matarka Saraya, ba za ka kira sunanta Saraya ba, amma Saratu ne sunanta.

16 Zan sa mata albarka, banda haka kuma zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za ta kuwa zama mahaifiyar al’ummai, sarakunan jama’a za su fito daga gare ta.”

17 Sai Ibrahim ya yi ruku’u, ya yi dariya a zuciyarsa, ya ce wa kansa, “Za a haifa wa mai shekara ɗari ɗa? Zai yiwu Saratu mai shekara tasa’in ta haifi ɗa?”

18 Sai Ibrahim ya ce wa Allah, “Da ma dai a bar Isma’ilu kawai ya rayu a gabanka.”

19 Allah ya ce, “A’a, matarka Saratu ita ce za ta haifa maka ɗa, za ka raɗa masa suna Ishaku. A gare shi zan tsai da alkawarina madawwami, da kuma ga zuriyarsa a bayansa.

20 Ga zancen Isma’ilu kuwa, na ji, ga shi, zan sa masa albarka in kuma riɓaɓɓanya shi ainun. Zai zama mahaifin ‘ya’yan sarakuna goma sha biyu, zan maishe shi al’umma mai girma.

21 Amma ga Ishaku ne zan tsai da alkawarina, wato wanda Saratu za ta haifa maka a baɗi war haka.”

22 Sa’ad da Allah ya gama magana da Ibrahim, sai ya tafi ya bar Ibrahim.

23 Ibrahim kuwa ya ɗauki Isma’ilu ɗansa, da dukan bayi, haifaffun gidansa, da waɗanda aka sayo su da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji na jama’ar gidansa kaciyar loɓarsa a wannan rana bisa ga faɗar Allah.

24 Ibrahim na da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciyar loɓarsa.

25 Isma’ilu ɗansa yana ɗan shekara goma sha uku sa’ad da aka yi masa kaciya.

26 A wannan rana, Ibrahim da ɗansa Isma’ilu aka yi musu kaciya,

27 da mazajen gidansa duka, da waɗanda suke haifaffun gidan da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙi, aka yi musu kaciya tare da shi.

Categories
FAR

FAR 18

An Alkawarta Haihuwar Ishaku

1 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ibrahim kusa da itatuwan oak na Mamre, a lokacin da yake zaune a ƙofar alfarwarsa da tsakar rana.

2 Da ya ɗaga idonsa, ya duba sai ga mutum uku suna tsaye a gabansa. Da ya gan su, sai ya sheƙa da gudu daga ƙofar alfarwar, don ya tarye su. Ya yi ruku’u,

3 ya ce, “Ya Ubangiji, in na sami tagomashi a gabanka, kada ka wuce gidana. A shirye nake in yi muku hidima.

4 Bari a kawo ɗan ruwa ku wanke ƙafafunku, ku shaƙata a gindin itace,

5 ni kuwa in tafi in kawo ɗan abinci, don rayukanku su wartsake, bayan haka sai ku wuce, tun da yake kun biyo ta wurin baranku.”

Sai suka ce, “Madalla! Ka aikata bisa ga faɗarka.”

6 Ibrahim kuwa ya gaggauta zuwa cikin alfarwa wurin Saratu, ya ce, “Ki shirya mudu uku na gari mai laushi da sauri, ki cuɗa, ki yi waina.”

7 Sai Ibrahim ya sheƙa zuwa garke, ya ɗauki maraƙi, matashi mai kyau, ya ba baransa, ya kuwa shirya shi nan da nan.

8 Ya ɗauki kindirmo da madara, da maraƙin da ya shirya, ya ajiye a gabansu, ya tsaya kusa da su a gindin itacen a sa’ad da suke ci.

9 Suka ce masa, “Ina Saratu matarka?”

Ya ce, “Tana cikin alfarwa.”

10 Baƙon ya ce, “Na yi maka alkawari matarka Saratu za ta haifi ɗa a wata na tara nan gaba. Zan sāke zuwa a lokacin.” Saratu kuwa tana ƙofar alfarwa, a bayansu, tana kasa kunne.

11 Ga shi kuwa, Ibrahim da Saratu sun tsufa, sun kwana biyu, gama Saratu ta daina al’adar mata.

12 Sai Saratu ta yi dariya a ranta, tana cewa, “Bayan na tsufa mai gidana kuma ya tsufa sa’an nan zan sami wannan gatanci?”

13 Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya, har da ta ce, ‘Ashe zan haifi ɗa, a yanzu da na riga na tsufa?’

14 Akwai abin da zai fi ƙarfin Ubangiji? A ajiyayyen lokaci zan komo wurinka, cikin wata tara, Saratu kuwa za ta haifi ɗa.”

15 Amma Saratu ta yi mūsu, tana cewa, “Ai, ban yi dariya ba,” Gama tana jin tsoro.

Ya ce, “A’a, hakika kin yi dariya.”

Ibrahim ya Yi Roƙo don Saduma

16 Sai mutanen suka tashi daga wurin, suka fuskanci Saduma, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya ya sallame su.

17 Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin aikatawa?

18 Ga shi kuwa, Ibrahim zai ƙasaita ya zama al’umma mai iko, sauran al’umman duniya duka za su sami albarka ta dalilinsa.

19 Gama na zaɓe shi don ya umarci ‘ya’yansa da gidansa domin su kiyaye tafarkin Ubangiji a bayansa, su riƙe adalci da shari’a.” Ubangiji ya tabbatar wa Ibrahim da abin da ya alkawarta masa.

20 Sai kuma Ubangiji ya ce, “Tun da yake kuka a kan Saduma da Gwamrata ya yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni ƙwarai,

21 zan sauka in gani ko sun aikata kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”

22 Sa’an nan mutanen suka juya daga nan, suka nufi Saduma, amma Ibrahim ya tsaya a gaban Ubangiji.

23 Sai Ibrahim ya matso kusa, ya ce, “Ashe, za ka hallaka adali tare da mugun?

24 Da a ce, akwai masu adalci hamsin cikin birnin, za ka hallaka wurin, ba za ka yafe su saboda masu adalcin nan hamsin waɗanda suke cikinsa ba?

25 Wannan ya yi nesa da kai, da ka aikata irin haka, wato da za ka aza mai adalci daidai yake da mugu! Wannan ya yi nesa da kai! Mahukuncin dukan duniya ba zai yi adalci ba?”

26 Sai Ubangiji ya ce, “In na sami adalai hamsin a cikin birnin Saduma, zan yafe wa dukan wurin sabili da su.”

27 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji, ni da nake ba kome ba ne, amma turɓaya ne da toka.

28 Da a ce za a rasa biyar daga cikin adalai hamsin ɗin, za ka hallaka birnin duka saboda rashin biyar ɗin?”

Sai ya ce, “Ba zan hallaka shi ba in na sami arba’in da biyar a wurin.”

29 Ya kuma sāke yin masa magana, ya ce, “Da a ce za a sami arba’in a wurin fa?”

Ya amsa ya ce, “Sabili da arba’in ɗin ba zan yi ba.”

30 Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan yi magana. Da a ce za a sami talatin a wurin fa?”

Ya amsa, “Ba zan yi ba, in na sami talatin a wurin.”

31 Ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji. Da a ce za a sami ashirin a wurin fa?”

Ya amsa ya ce, “Sabili da ashirin ɗin ba zan hallaka shi ba.”

32 Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan sāke yin magana, sau ɗayan nan kaɗai. Da a ce za a sami goma a wurin fa?”

Ya amsa ya ce, “Sabili da goma ɗin ba zan hallaka shi ba.”

33 Ubangiji kuwa ya yi tafiyarsa, bayan ya gama magana da Ibrahim. Ibrahim kuwa ya koma gida.

Categories
FAR

FAR 19

Zunubin Sadumawa ya Haɓaka

1 Mala’ikun nan biyu kuwa suka isa Saduma da maraice, Lutu kuwa yana zaune a ƙofar Saduma. Sa’ad da Lutu ya gan su sai ya miƙe ya tarye su. Sai ya yi ruku’u a gabansu.

2 ya ce, “Iyayengijina, ina roƙonku ku ratse zuwa gidan baranku, ku kwana, ku wanke ƙafafunku, da sassafe kuma sai ku kama hanyarku.”

Suka ce, “A’a, a titi za mu kwana.”

3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka ratse suka shiga gidansa, ya shirya musu liyafa, ya toya musu abinci marar yisti, suka ci.

4 Amma kafin su shiga barci, mutanen birnin Saduma, samari da tsofaffi, dukan mutane gaba ɗaya suka kewaye gidan.

5 Suka kira Lutu suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka da daren nan? Fito mana da su waje, don mu yi luɗu da su.”

6 Lutu ya fita daga cikin gida ya rufe ƙofar a bayansa ya je wurin mutane,

7 ya ce, “Ina roƙonku ‘yan’uwana, kada ku aikata mugunta haka.

8 Ga shi, ina da ‘ya’ya mata biyu waɗanda ba su san namiji ba, bari in fito muku da su waje, ku yi yadda kuka ga dama da su, sai dai kada ku taɓa mutanen nan ko kaɗan, gama sun shiga ƙarƙashin inuwata.”

9 Amma suka ce, “Ba mu wuri!” Suka kuma ce, “Wannan mutum ya zo baƙunci ne, yanzu kuma zai zama alƙali! Yanzu za mu yi maka fiye da yadda za mu yi musu.” Sai suka tutture Lutu suka matsa kusa don su fasa ƙofar.

10 Amma baƙin suka miƙa hannunsu, suka shigar da Lutu cikin gida inda suke, suka rufe ƙofa.

11 Sai suka bugi mutanen da suke ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu suna laluba inda ƙofa take.

Lutu ya Bar Saduma

12 Mutanen suka ce wa Lutu, “Kana da wani naka a nan? Ko surukai, ko ‘ya’ya mata da maza, ko dai kome naka da yake cikin birnin? Fito da su daga wurin,

13 gama muna gab da hallaka wurin nan, domin kukan da ake yi a kan mutanen ya yi yawa a gaban Ubangiji. Ubangiji kuwa ya aiko mu, mu hallaka birnin.”

14 Sai Lutu ya fita ya faɗa wa surukansa waɗanda za su auri ‘ya’yansa mata, “Tashi, ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma sai surukansa suka aza wasa yake yi.

15 Sa’ad da safiya ta gabato, mala’ikun suka hanzarta Lutu, suna cewa, “Tashi, ka ɗauki matarka da ‘ya’yanka biyu mata da suke nan, don kada a shafe ku saboda zunubin birnin.”

16 Amma da ya yi ta ja musu rai, sai mutanen suka kama hannunsa, da na matarsa, da na ‘ya’yansa biyu mata, saboda jinƙan da Ubangiji ya yi masa, suka fitar da shi suka kai shi a bayan birnin.

17 Sa’ad da suka fitar da shi, suka ce, “Ka gudu domin ranka, kada ka waiwaya baya, ko ka tsaya ko’ina cikin kwari, gudu zuwa tuddai domin kada a hallaka ka.”

18 Sai Lutu ya ce musu, “A’a, ba haka ba ne iyayengijina,

19 ga shi, baranka ya sami tagomashi a idonka, ka kuwa nuna mini babban alheri da ka ceci raina, amma ba zan iya in kai tuddan ba, kada hatsarin ya same ni a hanya, in mutu.

20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”

21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.

22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa wurin.” Domin haka aka kira sunan garin Zowar.

Halakar Saduma da Gwamrata

23 Da hantsi Lutu ya isa Zowar.

24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba wa Saduma da Gwamrata wutar kibritu daga sama,

25 ya hallakar da waɗannan birane, da dukan kwarin, da dukan mazaunan biranen, da tsire-tsire.

26 Amma matar Lutu da take bin bayansa ta waiwaya, sai ta zama surin gishiri.

27 Da sassafe kuwa sai Ibrahim ya tafi wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji,

28 ya duba wajen Saduma da Gwamrata, da wajen dukan ƙasar kwari, sai ya hangi, hayaƙi yana tashi kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya a bisa ƙasar.

29 Amma sa’ad da Allah ya hallaka biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya fid da Lutu daga halakar.

Asalin Mowabawa da Ammonawa

30 Lutu ya fita daga Zowar, ya zauna cikin tuddai da ‘ya’yansa biyu mata, gama yana jin tsoro ya zauna a Zowar. Ya zauna a cikin kogo da ‘ya’yansa biyu mata.

31 Sai ‘yar farin ta ce wa ƙaramar, “Mahaifinmu ya tsufa, ba wanda zai aure mu yadda aka saba yi ko’ina a duniya.

32 Zo dai, mu sa mahaifinmu ya sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”

33 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi. Da daren nan kuwa ‘yar farin ta shiga ta kwana da mahaifinta, shi kuwa bai san da kwanciyarta ba balle fa tashinta.

34 Kashegari kuma, ‘yar farin ta ce wa ƙaramar, “Ga shi, daren jiya na kwana da mahaifina, bari daren yau kuma, mu sa shi ya sha ruwan inabi, ke ma sai ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”

35 Saboda haka suka sa shi ya bugu da ruwan inabi a wannan dare kuma, ƙaramar ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san da kwanciyarta ba balle fa tashinta.

36 Haka nan kuwa, ‘ya’yan Lutu biyu ɗin nan suka sami ciki daga mahaifinsu.

37 Ta farin, ta haifi ɗa namiji, ta sa masa suna Mowab. Shi ne asalin Mowabawa har yau.

38 Ƙaramar kuma ta haifi ɗa namiji, ta sa masa suna Benammi, shi ne asalin Ammonawa har yau.

Categories
FAR

FAR 20

Ibrahim da Abimelek

1 Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi zuwa wajen karkarar Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. A lokacin da Ibrahim yake baƙunci a Gerar,

2 ya ce, matarsa Saratu ‘yar’uwarsa ce. Sai Abimelek Sarkin Gerar ya aika, aka ɗauko masa Saratu.

3 Amma Allah ya zo wurin Abimelek cikin mafarki da dad dare ya ce masa, “Mutuwa za ka yi saboda matar da ka ɗauko, gama ita matar wani ce.”

4 Abimelek bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ubangiji, za ka hallaka marar laifi?

5 Ba shi ya faɗa mini, ‘Ita ‘yar’uwata ce’ ba? Ba ita kanta kuma ta ce, ‘Shi ɗan’uwana ne’ ba? Cikin mutunci da kyakkyawan nufi na aikata wannan.”

6 Allah ya ce masa cikin mafarki, “I, na sani ka yi wannan cikin mutunci, ai, ni na hana ka ka aikata zunubin, don haka ban yarda maka ka shafe ta ba.

7 Yanzu fa, sai ka mayar wa mutumin da matarsa, gama shi annabi ne, zai yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In kuwa ba ka mayar da ita ba, ka sani hakika za ka mutu, kai, da dukan abin da yake naka.”

8 Abimelek ya tashi da sassafe, ya kira barorinsa duka ya kuma faɗa musu waɗannan abubuwa duka. Mutanen kuwa suka ji tsoro ƙwarai.

9 Abimelek kuwa ya kira Ibrahim, ya ce masa, “Me ke nan ka yi mana? Wane laifi na yi maka, da za ka jawo bala’i mai girma haka a kaina da mulkina? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba.”

10 Abimelek kuma ya ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan abu?”

11 Ibrahim ya ce, “Na yi haka, domin ina zaton babu tsoron Allah ko kaɗan a wannan wuri, shi ya sa na zaci, kashe ni za a yi saboda matata.

12 Banda haka nan ma, hakika ita ‘yar’uwata ce, ‘yar mahaifina amma ba ta mahaifiyata ba ce. Na kuwa aure ta.

13 A lokacin da Allah ya raba ni da gidan mahaifina, ya sa ni yawace yawace, na ce mata, ‘Wannan shi ne alherin da za ki yi mini a duk inda muka je, ki ce da ni ɗan’uwanki ne.’ ”

14 Abimelek ya ɗauki tumaki da takarkarai, da bayi mata da maza, ya ba Ibrahim, ya kuma mayar masa da matarsa Saratu.

15 Abimelek kuwa ya ce, “Ga shi, ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda ya yi maka daɗi.”

16 Ga Saratu kuwa ya ce, “Ga shi, na ba ɗan’uwanki azurfa guda dubu, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa, cewa ba ki da laifi.”

17 Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuwa ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata, har kuma suka sami haihuwa.

18 Gama dā Allah ya kulle mahaifar dukan gidan Abimelek saboda Saratu matar Ibrahim.