Categories
JOSH

JOSH 14

An Rarraba Ƙasar Kan’ana ta Hanyar Kuri’a

1 Waɗannan su ne karkasuwar gādon da Isra’ilawa suka karɓa a ƙasar Kan’ana, wanda Ele’azara, firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin iyalan kabilan Isra’ila suka ba su.

2 Kabilan nan tara da rabi sun karɓi nasu rabon gādo ta hanyar jefa kuri’a, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

3 Gama Musa ya riga ya ba kabilan nan biyu da rabi nasu gādo a wancan hayin Kogin Urdun wajen gabas, amma bai ba Lawiyawa rabon gādo ba.

4 Jama’ar Yusufu kuwa kabila biyu ce, wato Manassa da Ifraimu. Ba a kuma ba Lawiyawa rabon gādo a ƙasar ba, sai dai an ba su biranen da za su zauna, da filayen da za su yi kiwon garkensu.

5 Jama’ar Isra’ila fa suka yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa, suka rarraba ƙasar ta hanyar kuri’a.

An Ba Kalibu Hebron

6 Mutanen Yahuza suka je wurin Joshuwa a Gilgal, sa’an nan Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, ya ce masa, “Ka dai san maganar da Ubangiji ya yi wa Musa, mutumin Allah, a Kadesh-barneya a kaina.

7 Ina da shekara arba’in sa’ad da Musa bawan Ubangiji ya aike ni daga Kadesh-barneya don in leƙi asirin ƙasar. Na kuma kawo masa ainihin rahoton yadda yake a zuciyata.

8 Amma ‘yan’uwana da muka tafi tare, sun karya zukatan jama’ar, amma ni na bi Ubangiji Allahna da aminci.

9 Musa kuwa ya rantse a wannan rana ya ce, ‘Hakika duk inda ƙafafunka suka taka a ƙasan nan zai zama gādonka, kai da ‘ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahnka sosai!’

10 Ga shi kuwa, Ubangiji ya kiyaye ni har wa yau, kamar yadda ya faɗa, shekara arba’in da biyar ke nan, tun lokacin da Ubangiji ya faɗa wa Musa wannan magana, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a jeji. Ga shi yau ni mai shekara tamanin da biyar ne.

11 Ga shi kuwa, har wa yau ina da ƙarfi kamar ran da Musa ya aike ni. Kamar yadda ƙarfina yake a dā, haka yake a yanzu domin yaƙi, da kuma kai da kawowa.

12 Saboda haka sai ka ba ni ƙasar tuddai da Ubangiji ya ambata a ranan nan, gama a wannan rana ka ji yadda gwarzaye suke a can da manyan birane masu garu, mai yiwuwa ne Ubangiji zai kasance tare da ni, in kore su kamar yadda Ubangiji ya faɗa.”

13 Joshuwa ya sa wa Kalibu, ɗan Yefunne, albarka. Ya ba shi Hebron ta zama gādonsa.

14 Domin haka Hebron ta zama gādon Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, har wa yau, domin ya bi Ubangiji Allah na Isra’ila sosai.

15 A dā sunan Hebron Kiriyat-arba ne. Arba kuwa babban mutum ne cikin gwarzayen. Ƙasar kuwa ta shaƙata da yaƙi.

Categories
JOSH

JOSH 15

Yankin Ƙasar da Aka Ba Yahuza

1 Rabon da aka ba jama’ar Yahuza bisa ga iyalansu ya yi kudu, a iyakar Edom zuwa jejin Zin, can kudu nesa.

2 Iyakarsu wajen kudu ta miƙa tun daga ƙarshen Tekun Gishiri, daga wajen gaɓar da ta fuskanci kudu.

3 Ta milla kudanci hawan Akrabbim, ta zarce zuwa Zin, ta haura kudu da Kadesh-barneya, ta wajen Hesruna har zuwa Addar. Sai ta karkata zuwa Karka.

4 Ta zarce zuwa Azemon, ta bi ta rafin Masar zuwa inda ya gangara a teku. Wannan ita ce iyakar mutanen Yahuza wajen kudu.

5 Iyakarsu wajen gabas ta kama daga Tekun Gishiri zuwa bakin Urdun. Wajen arewa kuwa ta miƙa daga bakin teku a inda Kogin Urdun ya gangara a tekun.

6 Iyakar ta bi zuwa Bet-hogla, ta zarce zuwa arewa da Bet-araba, ta haura zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ra’ubainu.

7 Daga kwarin Akor ta wuce zuwa Debir ta yi wajen arewa, sa’an nan ta juya zuwa Gilgal wadda take daura da hawan Adummim wanda yake kudancin gefen kwarin. Sai ta zarce zuwa ruwan En-shemesh, ta ƙare a En-rogel.

8 Daga nan iyakar ta bi ta kwarin ɗan Hinnom a wajen kudancin kafaɗar Yebus, wato Urushalima. Ta kuwa bi ta dutsen da yake shimfiɗe daura da kwarin Hinnom wajen yamma, a arewacin ƙarshen kwarin Refayawa.

9 Ta kuma milla daga kan dutsen zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa, daga can zuwa biranen Dutsen Efron. Daga can kuma ta karkata zuwa Ba’ala, wato Kiriyat-yeyarim.

10 Ta kuma kewaye kudancin Ba’ala zuwa Dutsen Seyir. Ta zarce zuwa arewacin kafaɗar Dutsen Yeyarim, wato Kesalon. Daga nan ta gangara zuwa Bet-shemesh, ta kuma wuce zuwa Timna.

11 Iyakar kuma ta biya wajen kafaɗar tudun, arewa da Ekron, sa’an nan ta karkata zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta tafi zuwa Yabneyel, sa’an nan ta gangara a teku.

12 Bakin Bahar Rum, ita ce iyaka a wajen yamma. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuza bisa ga iyalansu.

Kalibu Ya Ci Hebron da Debir da Yaƙi

13 Kamar yadda Ubangiji ya umarci Joshuwa, ya ba Kalibu, ɗan Yefunne, rabonsa a tsakiyar jama’ar Yahuza. Rabon da aka ba shi, shi ne Kiriyat-arba, wato Hebron. Arba shi ne uban Anak.

14 Daga can sai Kalibu ya kori ‘ya’yan Anak, maza, su uku, da Sheshai, da Ahiman, da Talmai, zuriyar Anak.

15 Daga can kuma ya tafi ya fāɗa wa mazaunan Debir, dā sunan Debir Kiriyat-sefer ne.

16 Kalibu ya ce, “Duk wanda ya bugi Kiriyat-sefer, har ya ci ta, zan ba shi ‘yata Aksa aure.”

17 Otniyel kuwa, ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kalibu, ya ci Kiriyat-sefer. Kalibu kuwa ya ba shi Aksa ‘yarsa aure.

18 Da ta zo wurinsa, ya zuga ta ta roƙi mahaifinta saura. Da ta sauka daga kan jakinta, sai Kalibu ya ce mata, “Me kike so?”

19 Ta kuwa ce masa, “Ka yi mini alheri, da yake ka tura ni a ƙasar Negeb, ina roƙonka ka ba ni maɓuɓɓugar ruwa.” Kalibu kuwa ya ba ta maɓuɓɓugar tuddai da na kwari.

Biranen Kabilar Yahuza

20 Wannan shi ne gādon jama’ar Yahuza bisa ga iyalansu.

21 Biranen jama’ar Yahuza da suke can kudu sosai wajen iyakar Edom, su ne Kabzeyel, da Eder, da Yagur,

22 da Kina, da Dimona, da Adada,

23 da Kedesh, da Hazor, da Yitnan,

24 da Zif, da Telem, da Beyalot,

25 da Hazor-hadatta, da Kiriyot-hesruna, wato Hazor,

26 da Amam, da Shema, da Molada,

27 da Hazar-gadda, da Heshmon, da Bet-felet,

28 da Hazar-shuwal, da Biyer-sheba, da Biziyotaya,

29 da Ba’ala, da Abarim, da Ezem,

30 da Eltola, da Kesil, da Horma,

31 da Ziklag, da Madmanna, da Sansanna,

32 da Labayot, da Shilhim, da Ayin, da Rimmon. Birane ashirin da tara ke nan da ƙauyukansu.

33 Na filayen kwarin kuwa, su ne Eshtawol, da Zora, da Ashna,

34 da Zanowa, da En-ganim, da Taffuwa, da Enayim,

35 da Yarmut, da Adullam, da Soko, da Azeka,

36 da Shayarim, da Aditayim, da Gedera, da Gederotayim. Birane goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.

37 Da kuma Zenan, da Hadasha, da Migdal-gad,

38 da Dileyan, da Mizfa, da Yokteyel,

39 da Lakish, da Bozkat, da Eglon,

40 da Kabbon, da Lahmam, da Kitlish,

41 da Gederot, da Bet-dagon, da Na’ama, da Makkeda, birane goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.

42 Da kuma Libna, da Eter, da Ashan,

43 da Yifta, da Ashna, da Nezib,

44 da Kaila, da Akzib, da Maresha, birane tara ke nan da ƙauyukansu.

45 Da kuma Ekron da garuruwanta da ƙauyukanta.

46 Daga Ekron zuwa tekun, da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.

47 Ashdod da garuruwanta da ƙauyukanta, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta zuwa rafin Masar da Bahar Rum da bakinta.

48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne Shamir, da Yattir, da Soko,

49 da Danna, da Kiriyat-sanna, wato Debir,

50 da Anab, da Eshtemowa, da Anim,

51 da Goshen, da Holon, da Gilo. Birane goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.

52 Da kuma Arab, da Duma, da Eshan,

53 da Yanim, da Bet-taffuwa, da Afeka,

54 da Hunta, da Kiriyat-arba, wato Hebron, da Ziyor, birane tara ke nan da ƙauyukansu.

55 Da kuma Mawon, da Karmel, da Zif, da Yutta,

56 da Yezreyel, da Yokdeyam, da Zanowa,

57 da Kayin, da Gebeya, da Timna, birane goma ke nan da ƙauyukansu.

58 Halhul, da Bet-zur, da Gedor,

59 da Ma’arat, da Bet-anot da Eltekon, birane shida ke nan da ƙauyukansu.

60 Da kuma Kiriyat-ba’al, wato Kiriyat-yeyarim, da Rabba, birane biyu ke nan da ƙauyukansu.

61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne Bet-araba, da Middin, da Sekaka,

62 da Nibshan, da Birnin Gishiri, da En-gedi, birane shida ke nan da ƙauyukansu.

63 Amma jama’ar Yahuza ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zaune a Urushalima ba, don haka Yebusiyawa suka yi zamansu da jama’ar Yahuza cikin Urushalima har wa yau.

Categories
JOSH

JOSH 16

Yankin Ƙasar da Aka Ba Ifraimu da Manassa

1 Rabon zuriyar Yusufu ya milla tun daga Urdun zuwa wajen Yariko, gabas da ruwan Yariko zuwa jejin. Ya haura daga Yariko zuwa ƙasar tuddai zuwa Betel.

2 Daga Betel ya miƙa zuwa Luz, sa’an nan ya zarce zuwa Atarot, karkarar Arkiyawa.

3 Sai ya gangara yamma zuwa karkarar Yafletiyawa har zuwa karkarar Bet-horon wadda take cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, sa’an nan ya gangara a teku.

4 A nan ne jama’ar Yusufu, wato Manassa da Ifraimu, suka sami nasu gādo.

5 Karkarar jama’ar Ifraimu, bisa ga iyalansu, ita ce iyakar gādonsu a wajen gabas, wato ita ce Atarot-addar har zuwa Bet-horon wadda take kan tudu.

6 Daga can iyakar ta miƙa zuwa teku ta bar Mikmetat a wajen arewa. A wajen gabas kuwa iyakar ta karkata zuwa Ta’anat-Shilo, daga can sai ta zarce gaba a wajen gabas zuwa Yanowa.

7 Daga Yanowa sai ta gangara zuwa Atarot da Nayaran, ta kuma gegi Yariko, sa’an nan ta gangara a Urdun.

8 Daga Taffuwa, sai iyakar ta yi yamma zuwa rafin Kana, sa’an nan ta gangara a teku. Wannan shi ne gādon Ifraimawa bisa ga iyalansu,

9 tare da garuruwan da ƙauyukan da aka keɓe wa Ifraimawa daga cikin gādon jama’ar Manassa.

10 Amma ba su kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa ka zauna tare da Ifraimawa har wa yau, amma Kan’aniyawa suka zama bayi masu yin aikin dole.

Categories
JOSH

JOSH 17

1 Aka ba kabilar Manassa, ɗan farin Yusufu, nata rabon gādo. Makir ɗan farin Manassa, uban Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan domin shi jarumi ne.

2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manassa nasu rabon gādo bisa ga iyalansu, wato Abiyezer, da Helek, da Asriyel, da Shekem, da Hefer, da Shemida. Waɗannan su ne ‘ya’yan Manassa, maza, bisa ga iyalansu.

3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manassa ba shi da ‘ya’ya maza, sai dai mata. Sunayensu ke nan, Mala, da Nowa, da Hogla, da Milka, da Tirza.

4 Suka zo wurin Ele’azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin, suka ce, “Ubangiji ya umarci Musa ya ba mu gādo tare da ‘yan’uwanmu maza.” Sai ya ba su gādo tare da ‘yan’uwan mahaifinsu bisa ga umarnin Ubangiji.

5 Saboda haka kuwa Manassa ya sami kashi goma banda ƙasar Gileyad da Bashan da yake hayin gabashin Urdun,

6 domin jikokin Manassa mata sun sami gādo tare da jikokinsa maza. Aka ba sauran mutanen kabilar Manassa ƙasar Gileyad.

7 Yankin ƙasar Manassa ya kai daga Ashiru zuwa Mikmetat wadda take gabas da Shekem. Iyakar kuma ta miƙa kudu zuwa mazaunan En-taffuwa.

8 Ƙasar Taffuwa tana hannun mutanen Manassa, amma mutanen Ifraimu ne suke da garin Taffuwa wanda yake iyakar yankin Manassa.

9 Iyakar kuma ta gangara zuwa rafin Kana. Waɗannan birane da suke kudancin rafin, na Ifraimu ne, ko da yake suna cikin biranen Manassa. Iyakar Manassa kuwa ta bi gefen arewacin rafin ta gangara a Bahar Rum.

10 Ƙasar wajen kudu ta Ifraimu ce, ta wajen arewa kuwa ta Manassa. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Mutanen Ashiru suna wajen arewa, mutanen Issaka kuwa wajen gabas.

11 A yankin ƙasar Issaka da na Ashiru, Manassa yana da waɗannan wurare, Bet-sheyan da ƙauyukanta, da Ibleyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Endor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Magiddo da ƙauyukanta, da sulusin Nafat.

12 Amma mutanen Manassa ba su iya su mallaki waɗannan birane ba, don haka Kan’aniyawa suka yi zamansu a wuraren.

13 Amma sa’ad da Isra’ilawa suka yi ƙarfi sai suka tilasta su su yi musu aikin dole, amma ba su iya korarsu ba.

14 Kabilan Yusufu suka ce wa Joshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo guda ɗaya? Ga shi kuwa, muna da jama’a mai yawa, gama Ubangiji ya sa mana albarka.”

15 Joshuwa kuwa ya amsa musu, ya ce, “Idan ku babbar jama’a ce, har ƙasar tuddai ta Ifraimu ta kāsa muku, to, sai ku shiga jeji ku sheme wa kanku wuri a ƙasar Ferizziyawa da ta Refayawa.”

16 Sai mutanen kabilan Yusufu suka ce, “Ƙasar tuddai ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawa da suke zaune a filin, da waɗanda suke a Bet-sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke cikin Kwarin Yezreyel suna da karusan ƙarfe.”

17 Joshuwa kuma ya ce wa jama’ar gidan Yusufu, wato kabilar Ifraimu da ta Manassa, “Ku babbar jama’a ce, ga shi kuma, kuna da ƙarfi, ba kashi ɗaya kaɗai za ku samu ba,

18 amma ƙasar tuddai kuma za ta zama taku, ko da yake jeji ne. Sai ku sheme, ku mallaka duka. Gama za ku kori Kan’aniyawa, ko da yake su ƙarfafa ne, suna kuma da karusan ƙarfe.”

Categories
JOSH

JOSH 18

Rarraba Ƙasa a Shilo

1 Da jama’ar Isra’ila suka ci ƙasar, sai suka tattaru a Shilo inda suka kafa alfarwa ta sujada.

2 Har yanzu akwai sauran kabila bakwai na Isra’ila waɗanda ba su sami gādonsu ba tukuna.

3 Sai Joshuwa ya ce wa jama’ar Isra’ila, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na kakanninku ya ba ku?

4 Ku ba ni mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su auna ƙasar yadda za a raba ta gādo, sa’an nan su komo wurina.

5 Sai su raba ƙasar kashi bakwai. Kabilar Yahuza za ta ci gaba da zama a yankin ƙasarta a wajen kudu, mutanen gidan Yusufu kuwa su zauna a yankin ƙasarsu a wajen arewa.

6 Ku auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sa’an nan ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuwa zan jefa muku kuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.

7 Lawiyawa ba su da rabo tare da ku gama aikin Ubangiji shi ne rabonsu, da rabin ta Manassa sun riga sun sami nasu rabo wanda Musa, bawan Ubangiji, ya ba su a hayin gabashin Urdun.”

8 Joshuwa ya umarci mutanen da za su tafi su auna ƙasar, ya ce, “Ku shiga cikin ƙasar duka, ku auna sa’an nan ku komo wurina, ni kuwa zan jefa muku kuri’a a gaban Ubangiji a nan Shilo.”

9 Sai mutanen suka tafi, suka ratsa ƙasar tudu da ta gangare, suka auna ƙasar, suka raba ta kashi bakwai, suka lasafta garuruwan da suke ciki, sa’an nan suka koma wurin Joshuwa a Shilo.

10 Joshuwa kuwa ya jefa musu kuri’a a gaban Ubangiji a Shilo. Ta haka ya rarraba ƙasar ga jama’ar Isra’ila, kowa ya sami rabonsa.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Biliyaminu

11 Kuri’ar kabilar Biliyaminu bisa ga iyalanta ta fito. Yankin ƙasar da ya faɗo mata ke nan, ya zama a tsakanin yankin ƙasar kabilar Yahuza da na jama’ar Yusufu.

12 A wajen arewa iyakar ta tashi daga Urdun, ta bi ta tsaunin da yake arewa da Yariko, ta kuma haura tudu wajen yamma, har zuwa hamadar Bet-awen inda ta ƙare.

13 Daga can iyakar ta yi kudu, ta nufi cibiyar Luz, wato Betel, ta gangara zuwa Atarot-addar a bisa dutsen da yake kudu da Bet-horon ta kwari.

14 Daga nan iyakar ta nausa ta nufi yammacin kudancin dutse da yake kudu, daura da Bet-horon, sa’an nan ta tsaya a Kiriyat-ba’al, wato Kiriyat-yeyarim, birnin Yahuza. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.

15 A wajen kudu kuwa iyakar ta fara daga karkarar Kiriyat-yeyarim, daga can ta miƙa zuwa Efron a maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.

16 Iyakar kuma ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskar kwarin ɗan Hinnon, wanda yake arewa wajen ƙarshen kwarin Refayawa. Ta kuma gangara zuwa kwarin Hinnom ta yi kudu daura da Yebusiyawa, ta gangara zuwa En-rogel.

17 Sai ta nausa ta yi wajen arewa zuwa En-shemesh, sa’an nan ta tafi Gelilot wanda yake daura da hawan Adummim. Daga nan ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ra’ubainu.

18 Sai ta wuce ta yi arewa daura da gefen Bet-araba, daga nan ta gangara zuwa Araba.

19 Ta kuma zarce zuwa arewa daura da gefen Bet-hogla, ta tsaya a arewacin gaɓar Tekun Gishiri a ƙarshen Urdun wajen kudu.

20 Kogin Urdun shi ne iyakar a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Biliyaminu suka gāda.

21 Biranen iyalan kabilar Biliyaminu ke nan Yariko, da Bet-hogla, da Emekkeziz,

22 da Bet-araba, da Zemarayim, da Betel,

23 da Awwim, da Fara, da Ofra,

24 da Kefar-ammoni, da Ofni, da Geba. Birane goma sha biyu ke nan tare da ƙauyukansu.

25 Akwai kuma Gibeyon, da Rama, da Biyerot,

26 da Mizfa, da Kefira, da Moza,

27 da Rekem, da Irfeyel, da Tarala,

28 da Zela, da Elef, da Yebus, wato Urushalima, da Gebeya, da Kiriyat. Birane goma sha huɗu ke nan tare da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon mutanen Biliyaminu bisa ga iyalansu.

Categories
JOSH

JOSH 19

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Saminu

1 Kuri’a ta biyu ta faɗa kan kabilar Saminu bisa ga iyalanta. Nasu rabon gādon yana tsakiyar rabon gādon kabilar Yahuza.

2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda, Biyer-sheba, da Sheba, da Molada,

3 da Hazar-shuwal, da Bilha, da Ezem,

4 da Eltola, da Betul, da Horma,

5 da Ziklag, da Bet-markabot, da Hazar-susa,

6 da Bet-lebawot, da Sharuhen. Garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.

7 Akwai kuma Ayin, da Rimmon, da Eter, da Ashan. Garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,

8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da waɗannan garuruwa tun daga Ba’alat-biyer, wato Ramot ta Negeb. Wannan shi ne rabon gādon iyalan kabilar Saminu.

9 Gādon kabilar Saminu yana cikin yankin ƙasar rabon kabilar Yahuza domin rabon kabilar Yahuza ya yi mata yawa, don haka kabilar Saminu ta sami gādo daga cikin tsakiyar gādon kabilar Yahuza.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Zabaluna

10 Kuri’a ta uku ta faɗa a kan kabilar Zabaluna bisa ga iyalanta. Yankin ƙasar gādonsu ya kai har Sarid.

11 Iyakar ta hau wajen yamma zuwa Marala, ta kai Dabbeshet da rafin da yake gabas da Yakneyam.

12 Daga Sarid, ta nufi wajen gabas zuwa iyakar Kislotabar, sa’an nan ta bi ta Daberat da Yafiya.

13 Daga can ta miƙa wajen gabas zuwa Gat-hefer da Et-kazin, har zuwa Rimmon inda ta nausa zuwa Neya.

14 Daga wajen arewa iyakar ta juya zuwa Hannaton, sa’an nan ta faɗa a kwarin Iftahel.

15 Waɗannan garuruwa, da Kattat, da Nahalal, da Shimron, da Idala, da Baitalami, suna cikin garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu da suke cikin yankin ƙasar kabilar Zabaluna.

16 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke cikin gādon mutanen Zabaluna bisa ga iyalansu.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Issaka

17 Kuri’a ta huɗu ta faɗo a kan kabilar Issaka bisa ga iyalanta.

18 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar su ne, Yezreyel, da Kesullot, da Shunem,

19 da Hafarayim, da Shiyon, da Anaharat,

20 da Rabbit, da Kishiyon, da Ebez,

21 da Remet da En-ganim, da En-hadda, da Bet-fazzez.

22 Iyakar kuma ta bi ta Tabor, da Shahazuma, da Bet-shemesh. Sa’an nan ta gangara a Kogin Urdun. Akwai garuruwa goma sha shida da ƙauyukansu.

23 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke a yankin ƙasar da kabilar Issaka ta gāda bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Ashiru

24 Kuri’a ta biyar ta fāɗo a kan kabilar Ashiru bisa ga iyalanta.

25 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar, su ne Helkat, da Hali, da Beten, da Akshaf,

26 da Alammelek, da Amad, da Mishal. A wajen yamma, iyakar ta bi ta Karmel da Shihor-libnat.

27 Daga nan sai ta nausa wajen gabas, ta bi ta Bet-dagon, da Zabaluna, da kwarin Iftahel a wajen arewa zuwa Bet-emek da Nayil. Ta yi gaba a wajen arewa zuwa Kabul,

28 da Hebron, da Rehob, da Hammon, da Kana, har ta bi ta Sidon Babba.

29 Daga can ta nausa zuwa Rama, ta bi ta garun birnin Taya, sai kuma ta nausa zuwa Hosa, sa’an nan ta gangara Bahar Rum, wajen Mahalab, da Akzib,

30 da Umma, da Afek, da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.

31 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke cikin yankin ƙasar da kabilar Ashiru ta gāda bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Naftali

32 Kuri’a ta shida ta faɗo a kan kabilar Naftali bisa ga iyalanta.

33 Tasu iyaka, ta miƙa daga Helef, daga itacen oak da yake cikin Za’anannim, da Adami-nekeb, da Yabneyel har zuwa Lakkum, sa’an nan ta tsaya a Kogin Urdun.

34 Iyakar kuma ta juya wajen kudu zuwa Aznot-tabor, daga can ta miƙa zuwa Hukkok, sa’an nan ta kai Zabaluna wajen kudu, da Ashiru wajen yamma, da Yahuza wajen gabas wajen Urdun.

35 Garuruwan da yake da garu su ne, Ziddim, da Zer, da Hammat, da Rakkat, da Kinneret,

36 da Adama, da Rama, da Hazor,

37 da Kedesh, da Edirai, da En-hazor,

38 da Iron, da Migdal-el, da Horem, da Bet-anat, da Bet-shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.

39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon gādon kabilar Naftali da iyalanta.

Yankin Ƙasar da Aka Ba Kabilar Dan

40 Kuri’a ta bakwai ta faɗo a kan kabilar Dan bisa ga iyalanta.

41 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar gādonta ke nan, da Zora, da Eshtawol, da Ir-shemesh,

42 da Shalim, da Ayalon, da Itla,

43 da Elon, da Timna, da Ekron,

44 da Elteki, da Gebbeton, da Ba’alat,

45 da Yahud, da Bene-berak, da Gat-rimmon,

46 da Meyarkon, da Rakkon, tare da karkarar da take gefen Yaffa.

47 Sa’ad da Danawa suka rasa karkararsu, suka tafi, suka yaƙi Leshem. Da suka ci ta, sai suka hallaka mutanenta da takobi, suka mallaki ƙasar, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato Dan.

48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da aka Ba Joshuwa

49 Sa’ad da mutanen Isra’ila suka gama rarraba gādon ƙasar, suka ba Joshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikin nasu.

50 Bisa ga umarnin Ubangiji, suka ba shi garin da ya roƙa, wato Timnatsera a ƙasar tudu ta Ifraimu. Ya sāke gina garin, ya kuwa zauna a ciki.

51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Ele’azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin kakannin gidajen kabilan jama’ar Isra’ila, suka rarraba ta hanyar jefa kuri’a a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada a Shilo. Ta haka suka gama rarraba ƙasar.

Categories
JOSH

JOSH 20

An Keɓe Biranen Mafaka

1 Sai Ubangiji ya ce wa Joshuwa,

2 “Ka faɗa wa jama’ar Isra’ila, su keɓe biranen mafaka waɗanda na faɗa wa Musa ya faɗa muku.

3 Domin idan wani mutum ya yi kisankai ba da niyya ba, ba kuma da saninsa ba, sai ya tsere zuwa can. Biranen za su zama muku mafaka daga mai bin hakkin jini.

4 Wanda ya yi kisankan sai ya tsere zuwa ɗaya daga cikin biranen, ya tsaya a bakin ƙofar birnin, ya bayyana wa dattawan garin abin da ya same shi. In sun ji, sai su shigar da shi a birnin, su ba shi wurin zama, ya zauna tare da su.

5 Idan mai bin hakkin jinin ya bi shi, ba za su ba shi wanda ya yi kisankan ba, domin bai kashe maƙwabcinsa da gangan ba, ba kuma ƙiyayya a tsakaninsu dā ma.

6 Zai yi zamansa a birnin har lokacin da aka gabatar da shi gaban dattawa don shari’a, sai kuma bayan rasuwar babban firist na lokacin, sa’an nan wanda ya yi kisankan zai iya komawa garinsu da gidansa daga inda ya tsere.”

7 Saboda haka suka keɓe Kedesh ta Galili a ƙasar tuddai ta Naftali, da Shekem ta ƙasar tuddai ta Ifraimu, da Kiriyat-arba, wato Hebron, ta ƙasar tuddai ta Yahuza.

8 A hayin Urdun, gabas da Yariko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ra’ubainu, da Ramot cikin Gileyad ta kabilar Gad, da Golan cikin Bashan ta kabilar Manassa.

9 Waɗannan su ne biranen mafaka da aka keɓe domin dukan Isra’ilawa, da baƙin da suke baƙuntaka cikinsu. Don duk wanda ya yi kisankai ba da niyya ba zai iya tserewa zuwa can don kada ya mutu ta hannun mai bin hakkin jini. Zai zauna a can har lokacin da za a gabatar da shi a gaban taron jama’a.

Categories
JOSH

JOSH 21

Biranen da Aka Ba Lawiyawa

1 Shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa suka zo wurin Ele’azara, firist, da wurin Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan jama’ar Isra’ila.

2 Suka yi magana da su a Shilo a ƙasar Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya umarta ta bakin Musa a ba mu biranen zama da wuraren kiwo domin dabbobinmu.”

3 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai jama’ar Isra’ila suka ba Lawiyawa waɗannan birane da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.

4 Kuri’a ta faɗo a kan iyalan Kohatawa. Sai Lawiyawa na zuriyar Haruna firist suka karɓi birane goma sha uku daga kabilar Yahuza, da kabilar Saminu, da kabilar Biliyaminu.

5 Sauran Kohatawa suka karɓi birane goma daga iyalan kabilar Ifraimu, da kabilar Dan, da rabin kabilar Manassa.

6 Gershonawa kuwa suka karɓi birane goma sha uku ta hanyar jefa kuri’a daga iyalan kabilar Issaka, da kabilar Ashiru, da kabilar Naftali, da rabin kabilar Manassa a Bashan.

7 Sai Merariyawa bisa ga iyalansu suka karɓi birane goma sha biyu daga kabilar Ra’ubainu, da ta Gad, da ta Zabaluna.

8 Waɗannan birane da wuraren kiwo nasu su ne jama’ar Isra’ila suka ba Lawiyawa ta hanyar jefa kuri’a kamar yadda Ubangiji ya umarta ta bakin Musa.

9 Daga cikin kabilar Yahuza da kabilar Saminu aka ba zuriyar Haruna waɗannan birane da aka ambata.

10 Zuriyar Haruna tana cikin iyalan Kohatawa waɗanda suke Lawiyawa. Kuri’arsu ce ta fito da farko.

11 Sai aka ba su Kiriyat-arba, wato Hebron, a ƙasar tuddai ta Yahuza tare da wuraren kiwo nata da suke kewaye. Arba shi ne mahaifin Anak.

12 Amma saurukan birnin da ƙauyukansu an ba Kalibu, ɗan Yefunne, su zama mallakarsa.

13 Biranen da aka ba zuriyar Haruna firist ke nan, Hebron tare da wuraren kiwo nata, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Libna tare da wuraren kiwo nata,

14 da Yattir tare da wuraren kiwo nata, da Eshtemowa tare da wuraren kiwo nata,

15 da Holon tare da wuraren kiwo nata, da Debir tare da wuraren kiwo nata,

16 da Ayin tare da wuraren kiwo nata, da Yutta tare da wuraren kiwo nata, da Bet-shemesh tare da wuraren kiwo nata. Birane tara ke nan daga cikin kabilun nan biyu.

17 Daga cikin kabilar Biliyaminu aka ba su birane huɗu, wato Gibeyon tare da wuraren kiwo nata, da Geba tare da wuraren kiwo nata,

18 da Anatot tare da wuraren kiwo nata, da Almon tare da wuraren kiwo nata.

19 Dukan biranen da aka ba firistoci, wato zuriyar Haruna, guda goma sha uku ne tare da wuraren kiwo nasu.

20-22 Aka ba sauran Kohatiyawa na iyalan Lawiyawa birane huɗu daga kabilar Ifraimu. Aka ba su Shekem tare da wuraren kiwo nata, a ƙasar tuddai ta Ifraimu, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Gezer tare da wuraren kiwo nata, da Yokmeyam tare da wuraren kiwo nata, da Bet-horon tare da wuraren kiwo nata.

23-24 Aka kuma ba su birane huɗu daga kabilar Dan, wato Elteki tare da wuraren kiwo nata, da Gibbeton tare da wuraren kiwo nata, da Ayalon tare da wuraren kiwo nata, da Gat-rimmon tare da wuraren kiwo nata.

25 Daga cikin rabin kabilar Manassa, aka ba su birane biyu, su ne Ta’anak tare da wuraren kiwo nata, da Bileyam tare da wuraren kiwo nata.

26 Dukan birane da wuraren kiwo nasu da aka ba sauran Kohatawa na iyalan Lawiyawa guda goma ne.

27 Aka ba iyalan Gershonawa na cikin Lawiyawa birane biyu daga cikin rabo na rabin kabilar Manassa. Biranen su ne, Golan tare da wuraren kiwo nata, cikin Bashan, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Ashtarot da wuraren kiwo nata.

28-29 Aka kuma ba su birane huɗu daga cikin kabilar Issaka, biranen su ne, Kishiyon da wuraren kiwo nata, da Daberat da wuraren kiwo nata, da Yarmut da wuraren kiwo nata, da Enganim da wuraren kiwo nata.

30-31 Daga cikin rabon kabilar Ashiru aka ba su birane huɗu, su ne Mishal da wuraren kiwo nata, da Abdon da wuraren kiwo nata, da Helkat da wuraren kiwo nata, da Rehob da wuraren kiwo nata.

32 Daga cikin rabon kabilar Naftali aka ba su birane uku, su ne, Kedesh ta Galili da wuraren kiwo nata, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Hammon da wuraren kiwo nata, da Kartan da wuraren kiwo nata.

33 Dukan birane da wuraren kiwo nasu da aka ba iyalan Gershonawa guda goma sha uku ne.

34-35 Aka ba iyalan Merari na cikin Lawiyawa birane huɗu daga cikin rabon kabilar Zabaluna. Biranen ke nan, Yakneyam da wuraren kiwo nata, da Karta da wuraren kiwo nata, da Rimmon da wuraren kiwo nata, da Nahalal da wuraren kiwo nata.

36-37 Aka kuma ba su birane huɗu daga cikin rabon kabilar Ra’ubainu. Biranen ke nan, Bezer da wuraren kiwo nata, da Yahaza da wuraren kiwo nata da Kedemot da wuraren kiwo nata, da Mefayat da wuraren kiwo nata.,

38-39 Daga cikin kabilar Gad aka ba su birane huɗu, su ne Ramot ta Gileyad da wuraren kiwo nata, wannan birnin mafaka ne domin wanda ya yi kisankai, da Mahanayim da wuraren kiwo nata, da Heshbon da wuraren kiwo nata, da Yazar da wuraren kiwo nata.

40 Dukan biranen da aka ba iyalan Merari na Lawiyawa guda goma sha biyu ne.

41 Jimillar biranen da wuraren kiwo nasu da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.

42 Kowane birni yana da wuraren kiwo nasa kewaye da shi.

Isra’ilawa Sun Mallaki Ƙasar

43 Haka kuwa Ubangiji ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya rantse zai ba kakanninsu. Suka ci ƙasar, suka zauna a ciki.

44 Ubangiji kuma ya ba da hutawa ko’ina kamar yadda ya rantse wa kakanninsu. Babu wani daga cikin abokan gābansu da ya iya ta da kai da su, gama Ubangiji ya ba da abokan gābansu duka a hannunsu.

45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alheri da ya yi wa gidan Isra’ila.

Categories
JOSH

JOSH 22

Bagade a Bakin Urdun

1 Sa’an nan Joshuwa ya kira mutanen kabilar Ra’ubainu, da na Gad, da rabin kabilar Manassa.

2 Ya ce musu, “Kun aikata dukan abin da Musa, bawan Ubangiji, ya umarce ku, kun kuma yi biyayya da dukan abin da na umarce ku.

3 Ba ku yar da ‘yan’uwanku dukan waɗannan yawan kwanaki, har wa yau ba. Amma kuka kiyaye umarnin Ubangiji Allahnku sosai.

4 Yanzu Ubangiji Allahnku ya ba ‘yan’uwanku hutawa kamar yadda ya faɗa, yanzu dai sai ku koma, ku tafi gida a ƙasarku ta gādo wadda Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku a hayin Urdun.

5 Sai dai ku kiyaye umarnai da dokokin da Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa, ku kiyaye dokokinsa, ku manne masa, ku bauta masa da zuciya ɗaya da dukan ranku.”

6 To, Joshuwa ya sa musu albarka, sa’an nan ya sallame su, suka koma gida.

7 Musa ya riga ya ba rabin kabilar Manassa gādo a Bashan, sauran rabin kabilar kuwa Joshuwa ya ba su gādo tare da ‘yan’uwansu a yammacin hayin Urdun. Sa’ad da Joshuwa ya sallame su zuwa gida, ya sa musu albarka,

8 ya ce musu, “Ku koma gidajenku da wadata mai yawa, da dabbobi masu yawa, da azurfa, da zinariya, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da tufafi masu yawa. Ku raba da ‘yan’uwanku ganimar da kuka kwaso daga abokan gabanku.”

9 Sai Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka koma gida. Suka yi bankwana da sauran ‘yan’uwansu Isra’ilawa a Shilo ta ƙasar Kan’ana. Suka koma ƙasar Gileyad, ƙasar da suka gāda bisa ga umarnin Ubangiji ta bakin Musa.

10 Sa’ad da suka kai Gelilot, kusa da Urdun, a gefen da yake wajen ƙasar Kan’ana, suka gina babban bagade a wurin.

11 Sauran Isra’ilawa kuwa suka ji labari cewa, “Ga shi, Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa sun gina bagade a Gelilot a kan iyakar ƙasar Kan’ana, a wajen hayinsu na yammacin Urdun.”

12 Da Isra’ilawa suka ji haka sai dukansu suka tattaru a Shilo don su kai musu yaƙi.

13 Mutanen Isra’ila kuwa suka aiki Finehas, ɗan Ele’azara, firist, wurin Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa a ƙasar Gileyad.

14 Shugabanni goma suka tafi tare da shi, shugaba ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila. Kowane ɗayansu shugaba ne a danginsa a kabilar Isra’ila.

15 Da suka zo wurin Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa a ƙasar Gileyad, ya ce musu,

16 “In ji dukan taron jama’ar Ubangiji, ‘Wane irin cin amana ne wannan da kuka yi wa Allah na Isra’ila har da kuka bar bin Ubangiji yau?’ Kun tayar wa Ubangiji yau da kuka gina wa kanku bagade.

17 Zunubin da aka yi a Feyor, ashe, bai ishe mu ba, har annoba ta wahalar da taron jama’ar Ubangiji? Ga shi, har yanzu ma ba mu gama tsarkakewa daga wannan zunubi ba.

18 Za ku kuma daina bin Ubangiji ne yau? Idan kuka tayar masa yau, gobe zai yi fushi da dukan jama’ar Isra’ila.

19 Idan ƙasar mallakarku ƙazantacciya ce, sai ku haye zuwa ƙasar Ubangiji inda alfarwa ta sujada take, ku sami abin mallaka a tsakaninmu, amma kada ku tayar wa Ubangiji, ku kuma tayar mana ta wurin gina wa kanku wani bagade dabam da bagaden Allahnmu.

20 Lokacin da Akan, ɗan Zera, ya yi rashin aminci cikin abubuwan da aka haramta, ai, dukan Isra’ilawa aka hukunta. Ba shi kaɗai ya hallaka don zunubinsa ba.”

21 Sai Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka amsa wa shugabannin iyalan Isra’ilawa suka ce,

22 “Allah Maɗaukaki, Allah Ubangiji ya sani, bari Isra’ilawa kuma da kansu su sani. Idan tayarwa ce, ko kuwa mun yi wa Ubangiji rashin aminci ne, to, kada ku bar mu da rai yau.

23 Idan mun bar bin Ubangiji, muka gina wa kanmu bagade don mu miƙa hadayun ƙonawa, ko kuwa hadayun gari, ko kuwa hadayun salama, to, bari Ubangiji kansa ya sāka mana.

24 Saboda gudun gaba ne muka yi haka, domin kada wata rana ‘ya’yanku su ce wa ‘ya’yanmu, ‘Ba ruwanku da Ubangiji, Allah na Isra’ila.

25 Gama Ubangiji ya sa Kogin Urdun ya zama iyaka tsakaninmu da ku Ra’ubainawa da Gadawa domin haka ba ku da wani rabo a cikin Ubangiji.’ To, da haka ‘ya’yanku su hana ‘ya’yanmu yi wa Ubangiji sujada.

26 Don haka muka ce, ‘Bari mu gina bagade, ba domin miƙa hadayu na ƙonawa, ko na sadaka ba,

27 amma domin ya zama shaida tsakaninmu da ku, da tsakanin zuriyarmu da taku, don mu ci gaba da bautar Ubangiji da hadayunmu na ƙonawa, da na sadaka, da na salama.’ ‘Ya’yanku kuma ba za su ce wa ‘ya’yanmu, ‘Ba ku da wani rabo a cikin Ubangiji.’

28 Mun yi tunani, cewa idan wata rana aka ce mana, ko aka ce wa zuriyarmu haka, sai mu ce, ‘Ku dubi bagaden Ubangiji wanda iyayenmu suka gina, ba domin miƙa hadayu na ƙonawa, ko na sadaka ba, amma domin shaida a tsakaninmu da ku.’

29 Allah ya sawwaƙa mana mu tayar wa Ubangiji, mu bar bin Ubangiji, har mu gina wani bagade don miƙa hadayu na ƙonawa, da na gari, da na sadaka, banda bagaden Ubangiji Allahnmu, wanda yake a gaban mazauninsa.”

30 Sa’ad da Finehas, firist, da shugabannin jama’a, wato shugabannin iyalan Isra’ila, suka ji maganar da Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka faɗa, suka ji daɗi a rai.

31 Sa’an nan Finehas, ɗan Ele’azara, firist, ya ce wa Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa, “Yau mun sani Ubangiji yana tare da mu domin ba ku ci amanar Ubangiji ba.”

32 Sa’an nan Finehas, ɗan Ele’azara, firist, da shugabannin suka komo daga wurin Ra’ubainawa da Gadawa a ƙasar Gileyad, zuwa ƙasar Kan’ana wurin mutanen Isra’ila, suka ba su rahoton abin da suka ji.

33 Mutanen Isra’ila suka ji daɗin rahoton da aka ba su, suka yabi Allah, ba su sāke yin maganar zuwa yaƙi don su hallaka ƙasar da Ra’ubainawa da Gadawa suke zaune ba.

34 Ra’ubainawa da Gadawa suka sa wa bagaden suna Shaida, domin in ji su, “Shi shaida ne a tsakaninmu, cewa Ubangiji shi ne Allah.”

Categories
JOSH

JOSH 23

Joshuwa Ya Yi wa Jama’a Jawabi

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya hutar da Isra’ilawa daga abokan gābansu waɗanda suke kewaye da su. Joshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa.

2 Sai Joshuwa ya kira Isra’ilawa duka, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, da jarumawansu, ya ce musu, “Yanzu na tsufa, shekaruna sun yi yawa,

3 kun dai ga abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan al’ummai duka saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.

4 Ga shi kuma, na rarraba wa kabilanku ƙasashen al’umman da suka ragu, da na waɗanda na shafe su tsakanin Urdun da Bahar Rum wajen yamma.

5 Ubangiji Allahnku ne zai sa su gudu a gabanku, ya kore su daga ƙasar. Za ku mallaki ƙasarsu kamar yadda Ubangiji Allahnku ya alkawarta muku.

6 Domin haka sai ku yi ƙarfin hali ƙwarai, ku riƙe, ku aikata dukan abin da aka rubuta a littafin dokokin Musa, kada ku kauce dama ko hagu,

7 domin kada ku yi cuɗanya da sauran al’umman da take zaune tare da ku, kada ku ambaci sunayen gumakansu, ko ku rantse da su, ko ku bauta musu, ko ku sunkuya musu.

8 Amma ku manne wa Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi har wa yau.

9 Gama Ubangiji ya kori manyan al’ummai ƙarfafa daga gabanku, har wa yau ba mutumin da ya isa ya yi hamayya da ku.

10 Mutuminku guda zai runtumi mutum dubu nasu, tun da yake Ubangiji Allahnku ne yake yaƙi dominku, kamar yadda ya alkawarta muku.

11 Ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.

12 Gama idan kun kauce, kun koma da baya, kun haɗa kai da sauran al’umman nan da take tare da ku, har kuka yi aurayya da juna,

13 to, sai ku tabbata Ubangiji Allahnku ba zai dinga korar al’umman nan daga gabanku ba, za su zama muku azargiya, da tarko, da bulala a kwiyaɓunku, da ƙayayuwa a idanunku. Da haka za ku ƙare sarai daga cikin kyakkyawar ƙasan nan da Ubangiji Allahnku ya ba ku.

14 “A yanzu ina gaba da bin hanyar da kowa a duniya yakan bi, ku duka kuwa, a zukatanku da rayukanku, kun sani dukan abubuwan alheri da Ubangiji Allahnku ya alkawarta muku sun tabbata, ba ɗayan da bai tabbata ba.

15 Amma kamar yadda Ubangiji Allahnku ya cika alkawaran da ya yi muku, haka nan kuma Ubangiji zai aukar muku da masifu, har ya hallaka ku daga ƙasan nan mai albarka da Ubangiji Allahnku ya ba ku.

16 Lokacin da kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku da ya umarce ku, kuka tafi kuka bauta wa gumaka, kuka sunkuya musu, to, Ubangiji zai yi fushi da ku, zai kuwa hallaka ku daga ƙasa mai albarka da aka ba ku.”