Categories
2 SAR

2 SAR 8

An Mayar da Gonakin Mata daga Shunem

1 Elisha kuwa ya ce wa matar da ya ta da ɗanta daga matattu, “Ki tashi, ke da gidanki, ki zauna duk inda kika samu, gama Ubangiji ya sa a yi yunwa a ƙasar har shekara bakwai.”

2 Sai matar ta tashi, ta yi kamar yadda annabi Elisha ya faɗa mata. Ta tafi, ita da iyalinta suka zauna a ƙasar Filistiyawa har shekara bakwai.

3 A ƙarshen shekara bakwai ɗin, matar ta komo daga ƙasar Filistiyawa, ta tafi wurin sarki, ta roƙe shi a mayar mata da gidanta da gonarta.

4 A lokacin kuwa sarki yana tare da Gehazi, wato baran annabi Elisha, ya ce, “Ka faɗa mini dukan mu’ujizan da Elisha ya yi.”

5 A sa’ad da yake faɗa wa sarki yadda Elisha ya ta da matacce, sai ga matar da ya ta da ɗanta daga matattu, ta zo ta roƙi sarki ya mayar mata da gidanta da gonarta. Sai Gehazi ya ce, “Ran sarki ya daɗe, ai, ga matar, ga kuma yaronta wanda Elisha ya tashe shi daga matattu.”

6 Da sarki ya tambayi matar sai ta faɗa masa dukan labarin. Sarki kuwa ya sa wani bafade ya mayar mata da dukan abin da yake nata da dukan amfanin gonakin, tun daga ran da ta bar ƙasar har ranar da ta komo.

Hazayel Ya Ci Sarautar Suriya

7 Elisha kuwa ya tafi Dimashƙu. A lokacin kuwa Ben-hadad, Sarkin Suriya, yana ciwo. Aka faɗa masa cewa, annabi Elisha ya zo, yana nan,

8 sai sarki ya ce wa Hazayel, ɗaya daga cikin fādawansa, “Ka ɗauki kyauta, ka tafi wurin annabin Allah ka sa ya roƙar mini Ubangiji ko zan warke daga wannan cuta.”

9 Hazayel kuwa ya tafi wurin Elisha tare da kyauta iri iri na kayan Dimashƙu. Raƙuma arba’in ne suka ɗauko kayan. Da ya tafi ya tsaya a gabansa, ya ce, “Danka, Ben-hadad Sarkin Suriyawa, ya aiko ni wurinka don yana so ya ji ko zai warke daga wannan cuta.”

10 Elisha kuwa ya ce masa, “Tafi ka faɗa masa zai warke, amma Ubangiji ya nuna mini lalle zai mutu.”

11 Sai Elisha ya kafa wa Hazayel ido, yana kallonsa, har Hazayel ya ji kunya. Elisha kuwa ya fashe da kuka.

12 Hazayel ya ce, “Me ya sa shugabana yake kuka?”

Elisha ya amsa ya ce, “Domin na san irin muguntar da za ka yi wa jama’ar Isra’ila. Za ka ƙone kagaransu da wuta, ka karkashe samarinsu da takobi, za ka kuma fyaffyaɗe ƙananansu a ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”

13 Hazayel kuwa ya ce, “Ni wane ne? Ina na sami wannan iko? Ni ba kome ba ne.”

Elisha ya amsa ya ce, “Ubangiji ya nuna mini za ka zama Sarkin Suriya.”

14 Sa’an nan Hazayel ya tashi daga wurin Elisha ya koma wurin Ben-hadad. Ben-hadad ya tambaye shi, “Me Elisha ya faɗa maka?”

Sai ya ce, “Ya faɗa mini, cewa lalle za ka warke.”

15 Amma kashegari sai Hazayel ya ɗauki bargo, ya tsoma a ruwa, sa’an nan ya rufe fuskar sarki da shi har ya mutu.

Sai ya hau gadon sarautarsa.

Sarki Yehoram na Yahuza

16 A shekara ta biyar ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra’ila, Yoram ɗan Yehoshafat Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

17 Yana da shekara talatin da biyu da haihuwa sa’ad da ya ci sarautar. Ya yi shekara takwas yana sarauta a Urushalima.

18 Ya bi halin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama ya auri ‘yar Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji.

19 Duk da haka Ubangiji bai hallaka Yahuza ba, saboda bawansa Dawuda, tun da yake ya alkawarta zai ba shi haske, shi da ‘ya’yansa har abada.

20 A zamanin Yoram, Edomawa suka tayar wa Yahuza, suka naɗa wa kansu sarki.

21 Sa’an nan Yoram ya haye zuwa Zayar tare da dukan karusansa. Sai ya tashi da dare da shugabannin karusansa, ya bugi Edomawan da suka kewaye shi, amma sojojinsa suka gudu zuwa alfarwansu.

22 Haka kuwa Edom ta tayar wa Yahuza har wa yau. A lokacin kuma Libna ta tayar wa Yahuza.

23 Sauran ayyukan Yoram da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

24 Yoram kuwa ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Ahaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Ahaziya na Yahuza

25 A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yoram Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

26 Ya ci sarauta yana da shekara ashirin da biyu da haihuwa, ya kuwa yi mulki shekara guda a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ataliya jikanyar Omri, Sarkin Isra’ila.

27 Ya ɗauki halin gidan Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama shi surukin gidan Ahab ne.

28 Sarki Ahaziya kuwa ya tafi tare da Yehoram ɗan Ahab don su yi yaƙi da Hazayel, Sarkin Suriya, a Ramot cikin Gileyad. Suriyawa suka yi wa Yehoram rauni.

29 Sai sarki Yehoram ya koma zuwa Yezreyel don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa’ad da yake yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Ahaziya, ɗan Yoram, Sarkin Yahuza ya tafi ya ziyarci Yehoram ɗan Ahab cikin Yezreyel saboda yana ciwo.

Categories
2 SAR

2 SAR 9

An Naɗa Yehu Sarkin Isra’ila

1 Elisha kuwa ya kirawo ɗaya daga cikin annabawa matasa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kurtun mai, ka tafi Ramot-gileyad.

2 Sa’ad da ka isa can, sai ka nemi Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ka shiga, ka sa ya tashi daga wurin abokansa, ka kai shi cikin ɗaki.

3 Sa’an nan ka ɗauki kurtun man, ka zuba masa a ka, ka ce, ‘Ubangiji ya ce ya keɓe ka Sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa, ka gudu, kada ka tsaya.”

4 Sai saurayin nan, annabin, ya tafi Ramot-gileyad.

5 Sa’ad da ya isa, sai ga shugabannin sojoji suna taro. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka, ya shugaba.”

Yehu kuwa ya ce, “Wane ne a cikinmu?”

Sai ya ce, “Kai ne, ya shugaba.”

6 Sai Yehu ya tashi ya shiga ɗaki, saurayin kuwa ya zuba masa mai a ka, ya ce, “Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya keɓe ka sarkin jama’arsa, wato Isra’ila.

7 Za ka hallaka gidan Ahab, maigidanka, domin in ɗau fansar jinin annabawa bayinsa, da fansar jinin sauran bayin Ubangiji a kan Yezebel.

8 Gama dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan datse wa Ahab kowane ɗa namiji, bawa ko ‘yantacce, cikin Isra’ila.

9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yeroboam ɗan Nebat, da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahija.

10 Karnuka za su cinye Yezebel a cikin Yezreyel, ba wanda zai binne ta.” Sa’an nan ya buɗe ƙofar, ya gudu.

11 Da Yehu ya fita zuwa wurin sauran shugabannin, sai suka tambaye shi, “Lafiya kuwa, me ya sa mahaukacin nan ya zo wurinka?”

Sai ya ce musu, “Ai, kun san mutumin da irin maganarsa.”

12 Suka ce, “Ba mu sani ba, sai ka faɗa mana.”

Shi kuwa ya ce, “Ya faɗa mini, wai Ubangiji ya ce ya keɓe ni Sarkin Isra’ila.”

13 Sai kowane mutum a cikinsu ya yi maza ya tuɓe rigarsa, ya shimfiɗa a kan matakan, sa’an nan suka busa ƙaho, suna cewa, “Yehu ne sarki.”

Yehu Ya Kashe Yehoram Sarkin Isra’ila

14 Ta haka Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ya tayar wa Yehoram. A lokacin, Yehoram tare da dukan Isra’ila suna tsaron Ramot-gileyad, don kada Hazayel, Sarkin Suriya, ya fāɗa mata.

15 Amma sarki Yehoram ya komo Yezreyel, don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa’ad da ya yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Yehu ya ce, “Idan wannan shi ne nufinku, to, kada kowa ya zurare, ya tafi, ya ba da labari a Yezreyel.”

16 Sa’an nan Yehu ya hau karusarsa ya tafi Yezreyel, gama a can ne Yehoram yake kwance. Ahaziya Sarkin Yahuza ya gangara don ya gai da Yehoram.

17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezreyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.”

Sai Yehoram ya ce, “Ka aiki wani, ya hau doki, ya tafi ya tarye su, ya tambaye su, ko lafiya.”

18 Sai wani mutum ya hau doki ya tafi ya tarye su, ya ce, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?”

Sai Yehu ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.”

Mai tsaro kuma ya ce, “Manzo ya kai wurinsu, amma bai komo ba.”

19 Ya kuma aiki wani, na biyu, a kan doki, ya je wurinsu ya ce musu, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?”

Yehu ya amsa, ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.”

20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma bai komo ba. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa da hauka.”

21 Yehoram kuwa ya ce, “Ku shirya karusa.” Suka shirya masa karusa. Sa’an nan Yehoram Sarkin Isra’ila, da Ahaziya Sarkin Yahuza suka fita, kowa a cikin karusarsa, suka tafi su taryi Yehu. Suka sadu da shi a daidai gonar Nabot mutumin Yezreyel.”

22 Da Yehoram ya ga Yehu, sai ya ce, “Lafiya dai?”

Yehu ya ce, “Ina fa lafiya, tun da karuwanci da sihirin uwarka, Yezebel, sun yi yawa haka?

23 Yehoram kuwa ya juyar da karusarsa baya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Maƙarƙashiya ce, ya Ahaziya!”

24 Sai Yehu ya ja bakansa da iyakar ƙarfinsa ya ɗirka wa Yehoram kibiya, ta sha zarar zuciyarsa, sai ya ɓingire cikin karusarsa.

25 Yehu ya ce wa Bidkar, “Ka ɗauke shi ka jefar a gonar Nabot mutumin Yezreyel, gama ka tuna sa’ad da ni da kai muke kan dawakai muna biye da Ahab, tsohonsa, yadda Ubangiji ya faɗi wannan magana a kansa cewa,

26 ‘Hakika, kamar yadda jiya na ga jinin Nabot da na ‘ya’yansa, ni Ubangiji, zan sāka maka saboda wannan gona.’ Yanzu sai ka ɗauke shi, ka jefar da shi a wannan gona kamar yadda Ubangiji ya faɗa.”

Yehu Ya Kashe Ahaziya

27 Da Ahaziya Sarkin Yahuza, ya ga haka, sai ya gudu ta hanyar Bet-haggan.Yehu kuwa ya bi shi, ya ce, “Shi ma a harbe shi.” Sai suka harbe shi a cikin karusarsa a hawan Gur, wanda yake kusa da Ibleyam. Sai ya gudu zuwa Magiddo, ya mutu a can.

28 Fādawansa suka ɗauke shi a cikin karusar zuwa Urushalima, suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.

29 Ahaziya ya ci sarautar Yahuza a shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Yehoram ɗan Ahab.

Mutuwar Yezebel

30 Da Yezebel ta ji Yehu ya zo Yezreyel, sai ta shafa wa idanunta launi, ta gyara gashin kanta, sa’an nan ta leƙa ta taga.

31 Da Yehu ya shiga ƙofar garin, sai ta ce, “Kai Zimri, mai kashe maigidansa, me kake yi a nan?”

32 Sai ya ɗaga idanunsa wajen tagar, ya ce, “Wa yake wajena?” Sai babani biyu ko uku suka dube shi,

33 shi kuwa ya ce, “Ku wurgo ta ƙasa.” Sai suka wurgo ta ƙasa. Jininta ya fantsama a jikin bangon da jikin dawakan da suka tattake ta.

34 Sa’an nan Yehu ya shiga gida, ya ci ya sha, ya ce, “Ku san yadda za ku yi da wannan la’ananniyar mace, ku binne ta, gama ita ‘yar sarki ce.”

35 Amma da suka tafi don su binne ta, ba su tarar da kome ba sai ƙwaƙwalwa, da ƙafafu, da tafin hannuwanta.

36 Sai suka komo, suka faɗa masa. Sai ya ce musu, “Wannan, ai, faɗar Ubangiji, wadda ya faɗa ta bakin bawansa Iliya Batishbe, ya ce, ‘Karnuka za su cinye naman Yezebel a cikin Yezreyel.

37 Gawar Yezebel za ta zama wa ƙasa taki a Yezreyel don kada wani ya iya cewa wannan ita ce Yezebel.’ ”

Categories
2 SAR

2 SAR 10

An Kashe Zuriyar Ahab

1 Ahab yana da ‘ya’ya maza saba’in a Samariya, sai Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika zuwa Samariya wurin shugabanni da dattawan birni, da masu lura da ‘ya’yan Ahab.

2 Ya ce, “Yanzu dai, da zarar wasiƙun nan sun iso wurinku, da yake kuke lura da ‘ya’yan Ahab, kuna kuma da karusai, da dawakai, da kagara, da makamai,

3 sai ku zaɓi wanda ya fi dacewa duka daga cikin ‘ya’yan Ahab, ku naɗa shi sarki, ku yi yaƙi, domin ku tsare gidan Ahab.”

4 Amma suka ji tsoro ƙwarai, suka ce, “Ga shi, sarakuna biyu ba su iya karawa da shi ba, balle mu.”

5 Sai wakilin gidan, da wakilin birnin, da dattawa, da masu lura da ‘ya’yan sarki, suka aika wurin Yehu suka ce, “Mu barorinka ne, duk abin da ka umarce mu, za mu yi. Ba za mu naɗa wani sarki ba, sai ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”

6 Sa’an nan Yehu ya rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “Idan kuna goyon bayana, idan kuma kun shirya za ku yi mini biyayya, to, sai ku fille kawunan ‘ya’yan Ahab, sa’an nan ku zo wurina a Yezreyel gobe war haka.”

‘Ya’yan sarki, maza, su saba’in ne, suna a hannun manyan mutanen birni ne waɗanda suke lura da su.

7 Da wasiƙar ta iso wurinsu, sai suka kwashi ‘ya’yan sarki guda saba’in, suka karkashe su. Suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezreyel.

8 Da aka faɗa masa cewa an kawo kawunan ‘ya’yan sarki, sai ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar garin har safiya.”

9 Da safe, sa’ad da ya fita, ya tsaya, sai ya ce wa mutane duka, “Ba ku da laifi, ni ne na tayar wa maigidana har na kashe shi, amma wane ne ya kashe dukan waɗannan?

10 Ku sani fa ba maganar da Ubangiji ya faɗa a kan gidan Ahab da ba za ta cika ba, gama Ubangiji ya aikata abin da ya faɗa ta bakin bawansa Iliya.”

11 Haka kuwa Yehu ya karkashe waɗanda suka ragu na gidan Ahab a Yezreyel, wato dukan manyan mutanensa, da abokansa, da firistocinsa. Bai rage masa ko guda ba.

An Kashe Dangin Ahaziya

12 Yehu kuma ya fita zai tafi Samariya. A hanya, sa’ad da yake a Bet-eked ta makiyaya,

13 sai ya sadu da ‘yan’uwan Ahaziya Sarkin Yahuza, sai ya ce, “Ku su wane ne?”

Sai suka amsa, “Mu ‘yan’uwan Ahaziya ne, mun zo mu gai da ‘ya’yan sarki ne da ‘ya’yan sarauniya.”

14 Yehu kuwa ya ce, “Ku kama su da rai.” Sai suka kama su da rai, suka karkashe su a ramin Bet-eked, su arba’in da biyu ne, ba a rage ko ɗaya a cikinsu ba.

An Kashe Dukan Sauran Dangin Ahab

15 Da ya tashi daga can, sai ya sadu da Yehonadab ɗan Rekab yana zuwa ya tarye shi. Yehu ya gaishe shi, ya tambaye shi, “Zuciyarka ta amince da ni kamar yadda tawa ta amince da kai?”

Yehonadab ya amsa, “I.”

Sai Yehu ya ce, “Idan haka ne, to, miƙo mini hannunka.” Sai ya miƙa masa hannunsa. Yehu kuwa ya ɗauke shi zuwa cikin karusa.

16 Ya ce, “Ka zo tare da ni, ka ga kishin da nake da shi domin Ubangiji.” Sai suka tafi cikin karusarsa.

17 Da suka isa Samariya, sai ya kashe duk wanda ya ragu na gidan Ahab a Samariya. Ya share mutanen gidan Ahab kaf kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin annabi Iliya.

An Kashe Masu Sujada ga Ba’al

18 Yehu kuwa ya tara mutane duka, ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan, amma Yehu zai bauta masa da yawa.

19 Saboda haka, yanzu sai ku kirawo mini dukan annabawan Ba’al, da dukan masu yi masa sujada, da dukan firistocinsa. Kada a manta da wani, gama ina da babbar hadayar da zan miƙa wa Ba’al. Duk wanda bai zo ba, za a kashe shi.” Amma dabara ce Yehu yake yi don ya hallaka waɗanda suke yi wa Ba’al sujada.

20 Yehu kuma ya sa a yi muhimmin taro saboda Ba’al. Aka kuwa kira taron,

21 sai ya aika cikin Isra’ila duka, dukan masu yi wa Ba’al sujada kuwa suka zo, ba wanda bai zo ba. Suka shiga, suka cika haikalin Ba’al makil daga wannan gefe zuwa wancan.

22 Sa’an nan Yehu ya ce wa wanda yake lura da ɗakin tufafi, “Ku fito da tufafi na dukan waɗanda suke yi wa Ba’al sujada.” Shi kuwa ya fito musu da tufafin.

23 Bayan wannan Yehu ya shiga haikalin Ba’al tare da Yehonadab ɗan Rekab, ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku bincike, ku tabbata, ba wani bawan Ubangiji tare da ku, sai dai masu yi wa Ba’al sujada kaɗai.”

24 Sa’an nan Yehu da Yehonadab suka shiga don su miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Yehu ya riga ya sa mutum tamanin a waje, ya ce musu, “Mutumin da ya bar wani daga cikin waɗanda na bashe su a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”

25 Nan da nan da Yehu ya gama miƙa hadaya ta ƙonawa, sai ya ce wa mai tsaro da shugabannin, “Ku shiga, ku karkashe su, kada ku bar wani ya tsere.” Da suka karkashe su, sai suka fitar da su waje, sa’an nan suka shiga can cikin haikalin Ba’al.

26 Suka fitar da gumakan da suke cikin haikalin Ba’al, suka ƙone su.

27 Suka yi kaca kaca da gunkin Ba’al da haikalinsa, suka mai da haikalin ya zama salga har wa yau.

28 Yehu ya kawar da Ba’al daga cikin Isra’ila.

29 Amma bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila su yi zunubi. Siffofin maruƙa biyu suna nan a Betel da Dan.

30 Ubangiji kuwa ya ce wa Yehu, “Da yake ka yi abin da yake daidai a gare ni, ka yi wa gidan ahab bisa ga dukan abin da yake a zuciyata, ‘ya’yanka, har tsara ta huɗu, za su ci sarautar Isra’ila.”

31 Amma Yehu bai mai da hankali ya yi tafiya a tafarkin Ubangiji Allah na Isra’ila da zuciya ɗaya ba. Bai rabu da zunuban Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila su yi zunubi.

Mutuwar Yehu

32 A kwanakin an Ubangiji ya soma rage ƙasar Isra’ila. Hazayel kuwa ya yaƙe su a karkarar Isra’ila,

33 tun daga Urdun har zuwa wajen gabas, da dukan ƙasar Gileyad, da ta Gad, da ta Ra’ubainu, da ta Manassa, tun daga Arower wadda dake kusa da kwarin Arnon haɗe da Gileyad da Bashan.

34 Sauran ayyukan Yehu da dukan abin da ya yi, da dukan ƙarfinsa an rubuta su a littafin tarihin sarakuna Isra’ila.

35 Yehu kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Yehowahaz ɗansa ya gaji sarautarsa.

36 Yehu ya yi mulkin Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

Categories
2 SAR

2 SAR 11

Sarauniya Ataliya ta Yahuza

1 Sa’ad da Ataliya, uwar Ahaziya, ta ga ɗanta ya rasu, sai ta tashi ta hallaka dukan ‘ya’yan sarauta.

2 Amma Yehosheba ‘yar sarki Yoram, ‘yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin ‘ya’yan sarki waɗanda aka kashe, ta ɓoye shi da mai renonsa, an yi ta renonsa cikin ɗaki. Da haka ta tserar da shi daga Ataliya, har ba a kashe shi ba.

3 Ya zauna tare da ita shekara shida a ɓoye, a cikin Haikalin Ubangiji sa’ad da Ataliya take mulkin ƙasar.

Yehoyada Ya Tayar

4 A shekara ta bakwai sai Yehoyada ya aika ya kawo shugabannin Keretiyawa da na masu tsaro a Haikalin Ubangiji. Ya yi alkawari da su, ya sa suka yi rantsuwa a Haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.

5 Ya kuma umarce su cewa, “Abin da za ku yi ke nan, sai sulusinku da sukan zo aiki a ranar Asabar, su yi tsaron gidan sarki.

6 Sulusinku kuma zai kasance a ƙofar Sur. Ɗaya sulusin kuma zai kasance a bayan masu tsaro, haka za ku yi tsaron gidan, ku tsare shi.

7 Ƙungiyarku biyu kuma waɗanda sukan tashi aiki ran Asabar, za su yi tsaron Haikalin Ubangiji da kuma sarki.

8 Za ku kewaye sarki, kowane mutum ya riƙe makaminsa. Duk wanda ya yi ƙoƙari ya zo kusa, sai a kashe shi. Sai ku kasance tare da sarki duk lokacin da zai fita da duk lokacin da zai shiga.”

9 Shugabannin fa suka aikata bisa ga dukan abin da Yehoyada firist ya umarta. Kowa ya zo duk da mutanensa waɗanda za su huta aiki ran Asabar tare da waɗanda za su yi aiki ran Asabar, suka zo wurin Yehoyada.

10 Firist kuwa ya ba shugabannin māsu da garkuwoyin Dawuda waɗanda suke cikin Haikalin Ubangiji.

11 Matsara suka tsaya, kowa da makaminsa a hannu, daga wajen kudu na Haikalin zuwa wajen arewa. Suka kewaye bagade da Haikali.

12 Sa’an nan ya fito da ɗan sarki, ya sa kambin sarauta a kansa, ya kuma ba shi dokokin. Suka naɗa shi, suka zuba masa man naɗawa, sa’an nan suka yi tāfi suna cewa, “Ran sarki ya daɗe.”

13 Da Ataliya ta ji muryoyin matsara da na jama’a, sai ta zo wurin mutane a Haikalin Ubangiji.

14 Da ta duba, sai ta ga sarki a tsaye kusa da ginshiƙi bisa ga al’ada, shugabanni da masu busa kuwa suna tsaye kusa da sarki. Dukan mutanen ƙasar suna ta murna suna ta busa ƙaho. Sai Ataliya ta kece tufafinta, ta yi ihu, tana cewa, “Tawaye, tawaye!”

15 Yehoyada, firist kuwa, ya umarci shugabannin sojoji, ya ce, “Ku fitar da ita daga nan, duk kuma wanda yake son kāre ta, ku sa takobi ku kashe shi.” Ya kuma ce, “Kada a kashe ta a Haikalin Ubangiji.”

16 Suka kama ta, suka fitar da ita ta ƙofar dawakai zuwa gidan sarki, can suka kashe ta.

Gyare-gyaren Yehoyada

17 Yehoyada kuwa ya yi alkawari tsakanin Ubangiji, da sarki, da jama’a, yadda za su zama jama’ar Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da jama’a.

18 Sai dukan jama’ar ƙasa suka tafi haikalin Ba’al suka farfashe shi, da bagadensa da siffofinsa. Suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagaden.

Yehoyada kuwa ya sa matsara su yi tsaron Haikalin Ubangiji,

19 ya kuma sa shugabanni, da Keretiyawa, da matsara, da dukan jama’ar ƙasar, su fito da sarki daga Haikalin Ubangiji, suka rufa masa baya ta ƙofar matsara zuwa gidan sarki. Suka sa shi a gadon sarautar sarakuna.

20 Dukan jama’ar ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya huta bayan da an kashe Ataliya a gidan sarki.

Sarki Yowash na Yahuza

21 Jowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya ci sarauta.

Categories
2 SAR

2 SAR 12

1 A shekara ta bakwai ta sarautar Yehu, Yowash ya ci sarautar. Ya yi shekara arba’in yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Zibiya ta Biyer-sheba.

2 Yowash kuwa ya yi abin da yake daidai ga Ubangiji dukan kwanakinsa, domin Yehoyaka, firist, ya koya masa.

3 Duk da haka ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba, mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da ƙona turare a kan tuddan.

4 Yowash ya ce wa firistoci, “Dukan kuɗin tsarkakan abubuwa da ake kawowa a Haikalin ubangiji, da kuɗin da aka tsara wa kowane mutum, da kuɗin da aka bayar da yardar rai, da ake kawowa a Haikali,

5 sai ku karɓa daga junanku, don a gyara duk inda ake bukatar gyara a Haikalin.”

6 Amma har a shekara ta ashirin da uku ta sarautar sarki Yowash, firistocin ba su yi wani gyara a Haikalin ba.

7 Saboda haka Yowash ya kirawo Yehoyada, firist, da sauran firistoci, ya ce musu, “Me ya sa ba ku gyara Haikalin? Daga yanzu kada ku karɓi kuɗi daga wurin abokanku, sai in za ku ba da shi domin gyaran Haikalin.”

8 Firistocin kuwa suka yarda, ba za su karɓi kuɗi daga wurin jama’a ba, ba su kuwa gyara Haikalin ba.

9 Sa’an nan Yehoyada, firist, ya ɗauki akwati, ya huda rami a murfin, sa’an nan ya ajiye shi kusa da bagade a sashin dama na shiga Haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka saka dukan kuɗin da aka kawo a Haikalin Ubangiji.

10 Sa’ad da suka gani akwai kuɗi da yawa a cikin akwatin, sai magatakardan sarki, da babban firist suka zo, suka ƙirga kuɗin da yake a Haikalin Ubangiji suka ƙunsa shi a babbar jaka.

11 Sa’an nan suka ba da kuɗin da aka ƙirga a hannun waɗanda suke lura da aikin Haikalin Ubangiji, domin su biya masassaƙan katakai, da masu haɗawa da suke aikin Haikalin Ubangiji,

12 da masu gini, da masu sassaƙa duwatsu, a kuma sayi katako da sassaƙaƙƙun duwatsu don gyaran Haikalin Ubangiji, da kowane irin abu da ake bukata domin gyaran Haikalin.

13 Amma ba a mori kuɗin da aka kawo a Haikalin Ubangiji domin yin kwanonin azurfa, da abin katse fitila, da tasoshi, da ƙahoni, da kwanonin zinariya ko na azurfa ba.

14 Gama an ba da kuɗin ga ma’aikatan da suke gyaran Haikalin ubangiji.

15 Ba a nemi lissafin kuɗin a wurin mutanen da aka ba su kuɗin don su biya ma’aikatan ba, gama su amintattu ne.

16 Ba a kawo kuɗi na hadaya don laifi da hadaya don zunubi a cikin Haikalin Ubangiji ba, ya zama na firistoci.

17 Hazayel Sarkin Suriya kuwa ya tafi ya yi yaƙi da Gat har ya cinye ta, ya kuma shirya zai yi yaƙi da Urushalima.

18 Sai Yowash Sarkin Yahuza ya kwashe dukan kyautai na yardar rai waɗanda Yehoshafat, da Yoram, da Ahaziya, kakanninsa, sarakunan Yahuza suka keɓe, ya kuma kwashe kyauta ta yardar rai ta kansa, da dukan zinariya da aka samu a baitulmalin Haikalin Ubangiji da baitulmalin gidan sarki, ya aika wa Hazayel, Sarkin Suriya. Sa’an nan Hazayel ya tashi ya bar Urushalima.

19 Sauran ayyukan Yowash da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

20 Fādawansa suka ƙulla maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidan da yake Millo, a kan hanyar da ta nufi Silla.

21 Yozakar ɗan Shimeyat, da Yehozabad ɗan Shemer su ne fādawansa da suka kashe shi. Aka binne shi a makabartar kakanninsa cikin birnin Dawuda. Amaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 13

Sarki Yehowahaz na Isra’ila

1 A shekara ta ashirin da uku ta sarautar Yowash ɗan Ahaziya Sarkin Yahuza, Yehowahaz ɗan Yehu ya ci sarautar Isra’ila a Samariya. Ya yi mulki shekara goma sha bakwai.

2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, gama ya aikata irin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ilawa su yi zunubi. Bai rabu da zunuban Yerobowam ba.

3 Ubangiji kuwa ya husata da jama’ar Isra’ila, sai ya dinga ba da su a hannun Hazayel Sarkin Suriya, da hannun Ben-hadad ɗan Hazayel.

4 Sai Yehowahaz ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya ji shi, gama ya ga wahalar da Isra’ilawa suke ciki, wato yadda Sarkin Suriya yake musguna musu.

5 Saboda haka Ubangiji ya ba jama’ar Isra’ila maceci, suka kuwa kuɓuta daga ƙangin Suriyawa, suka zauna a gidajensu lafiya kamar dā.

6 Duk da haka ba su rabu da zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi. Sun aikata irin zunuban Yerobowam. Gunkiyan nan mai suna Ashtoret tana nan a Samariya.

7 Rundunar Yehowahaz kuwa ba ta fi mahaya hamsin, da karusai goma, da dakarai dubu goma (10,000) ba, gama Sarkin Suriya ya hallaka rundunar, ya yi kaca kaca da ita kamar ƙura a masussuka.

8 Sauran ayyukan Yehowahaz da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

9 Yehowahaz kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Yehowash ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Yehowash na Isra’ila

10 A shekara ta talatin da bakwai ta sarautar Yowash Sarkin Yahuza, Yehowash ɗan Yehowahaz ya ci sarautar Isra’ila a Samariya. Ya yi shekara goma sha shida yana sarauta.

11 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da dukan zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa jama’ar Isra’ila su yi zunubi. Ya bi halin Yerobowam ɗan Nebat.

12 Sauran ayyukan Yehowash da dukan abin da ya yi, da irin ƙarfin da ya yi yaƙi da Amaziya Sarkin Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.2Sar 14.15; 1Sar 15.31

13 Yehowash kuwa ya mutu, aka binne shi a Samariya, inda ake binne sarakunan Isra’ila, sai Yerobowam na biyu ya gāji gadon sarautarsa.

Annabi Elisha Ya Rasu

14 Da Elisha ya kamu da ciwon ajali, sai Yehowash Sarkin Isra’ila ya tafi wurinsa, ya yi kuka a gabansa, yana cewa, “Ubana, Ubana, karusar Isra’ila da mahayan dawakanta!”

15 Elisha kuwa ya ce masa, “Ka ɗauki baka da kibau.” Shi kuwa ya ɗauka.

16-17 Sa’an nan ya ce, “Ka buɗe tagar da take wajen gabas.” Sai ya buɗe. Elisha ya kuma ce masa, “Ka ja bakan.” Ya kuwa ja. Sai Elisha ya ɗora hannuwansa a bisa hannuwan sarki. Sa’an nan Elisha ya ce, “Harba.” Sai ya harba. Elisha kuwa ya ce, “Kibiyar Ubangiji ta nasara, kibiyar nasara a kan Suriya. Gama za ka yi yaƙi da Suriyawa a Afek har ka ci su.”

18 Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibau.” Shi kuwa ya ɗauka. Sai ya ce wa Sarkin Isra’ila, “Ka caki ƙasa da su.” Sai ya caka har sau uku, sa’an nan ya tsaya.

19 Elisha kuwa ya husata, ya ce, “Da ma ka caka sau biyar ko shida da za ka yi nasara a kan Suriyawa har ka ci su sarai, amma yanzu za ka yi nasara da su sau uku kawai.”

20 Elisha kuwa ya rasu, aka binne shi.

Maharan Mowabawa sukan kawo yaƙi a ƙasar da bazara.

21 Wata rana ana binne gawa, sai aka ga mahara, aka jefar da gawar a cikin kabarin Elisha. Da gawar ta taɓi ƙasusuwan Elisha, sai ya farko ya tashi ya miƙe tsaye.

Yaƙi tsakanin Isra’ila da Suriya

22 Hazayel Sarkin Suriya kuwa ya musguna wa jama’ar Isra’ila a dukan zamanin Yehowahaz.

23 Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, bai ba su baya ba saboda alkawarinsa da Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. Bai yarda ya hallaka su ba, bai kuma yi watsi da su ba har wa yau.

24 Da Hazayel Sarkin Suriya ya rasu, sai Ben-hadad ɗansa ya gāji sarautarsa.

25 Sai Yehowash ɗan Yehowahaz ya ƙwace daga hannun Ben-hadad, ɗan Hazayel, biranen da Ben-hadad ya ci da yaƙi daga hannun Yehowahaz, tsohonsa. Sau uku Yehowash ya ci shi da yaƙi, sa’an nan ya karɓe biranen Isra’ila.

Categories
2 SAR

2 SAR 14

Sarki Amaziya na Yahuza

1 A shekara ta biyu ta sarautar Yehowash ɗan Yehowahaz Sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza ya ci sarauta.

2 Yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Yehowaddin ta Urushalima.

3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma bai kai kamar kakansa Dawuda ba. Ya yi kamar yadda tsohonsa, Yowash ya yi.

4 Amma ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba. Mutane suka yi ta miƙa hadaya, da ƙona turare a matsafai na kan tuddai.

5 Sa’ad da mulkin ya kahu sosai a hannun Amaziya, sai ya kashe fādawan da suka kashe tsohonsa.

6 Amma bai kashe ‘ya’yan masu kisankai ɗin ba, don ya bi abin da aka rubuta a littafin dokokin Musa, inda Ubangiji ya umarta cewa, “Kada a kashe iyaye saboda ‘ya’ya, kada kuma a kashe ‘ya’ya saboda iyaye, amma kowa zai mutu saboda laifin kansa.”

7 Ya kuma kashe Edomawa dubu goma (10,000) a Kwarin Gishiri, sa’an nan ya ƙwace Sela, ya ba ta suna Yokteyel, haka ake kiranta har wa yau.

8 Amaziya kuwa ya aiki manzanni wurin Yehowash, ɗan Yehowahaz, ɗan Yehu, Sarkin Isra’ila, yana nemansa da yaƙi.

9 Yehowash Sarkin Isra’ila ya mayar wa Amaziya Sarkin Yahuza da amsa cewa, “A dutsen Lebanon ƙaya ta aika wurin itacen al’ul ta ce, ‘Ka ba ɗana ‘yarka ya aura.’ Sai mugun naman jeji na Lebanon ya wuce, ya tattake ƙayar.

10 Yanzu kai, Amaziya, ka bugi Edomawa don haka zuciyarka ta kumbura. To ka gode da darajar da ka samu, ka tsaya a gida, gama don me kake tonon rikici da zai jawo maka fāduwa, kai da mutanen Yahuza?”

11 Amma Amaziya bai ji ba. Sai Yehowash Sarkin Isra’ila ya tafi, ya shiga yaƙi da Amaziya, Sarkin Yahuza a Bet-shemesh ta Yahuza.

12 Mutanen Isra’ila suka ci na Yahuza. Sai kowane mutum ya gudu gida.

13 Yehowash Sarkin Isra’ila kuwa ya kama Amaziya, Sarkin Yahuza, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-shemesh. Ya kuma zo Urushalima ya rushe garun Urushalima kamu ɗari huɗu daga Ƙofar Ifraimu zuwa Ƙofar Kusurwa.

14 Ya kwashe dukan zinariya, da azurfa, da dukan kwanonin da suke cikin Haikalin Ubangiji, da na baitulmalin gidan sarki, da mutanen da aka ba da su jingina, sa’an nan ya koma Samariya.

15 Sauran ayyukan Yehowash da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, da yadda ya yi yaƙi da Amaziya, Sarkin Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

16 Yehowash ya mutu, aka binne shi a Samariya a makabartar sarakunan Isra’ila, Ɗansa Yerobowam na biyu ya gāji sarautarsa.

Mutuwar Sarki Amaziya na Yahuza

17 Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza, ya yi shekara goma sha biyar bayan rasuwar Yehowash ɗan Yehowahaz Sarkin Isra’ila.

18 Sauran ayyukan da Amaziya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

19 Aka ƙulla makirci a kansa a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma aka aika zuwa Lakish, aka kashe shi a can.

20 Aka kawo gawar a kan dawakai, aka binne a Urushalima a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda.

21 Sai dukan mutanen Yahuza suka ɗauki Azariya mai shekara goma sha shida, suka sarautar da shi don ya gāji tsohonsa Amaziya.

22 Shi ne ya gina Elat, ya mai da ita ta Yahuza bayan rasuwar tsohonsa.

Sarki Yerobowam na biyu na Isra’ila

23 A shekara goma sha biyar ta sarautar Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza, Yerobowam ɗan Yehowash Sarkin Isra’ila, ya ci sarauta a Samariya. Ya yi mulki shekara arba’in da ɗaya.

24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da dukan zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

25 Ya kafa iyakar Isra’ila daga ƙofar Hamat har zuwa tekun Araba. Wannan kuwa shi ne abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa ta bakin bawansa annabi Yunana, ɗan amittai, daga Gathefer.

26 Gama Ubangiji ya ga Isra’ila tana shan azaba mai tsanani, gama ba bawa ko ɗa wanda zai taimaki Isra’ila.

27 Ubangiji kuwa bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga duniya ba, saboda haka ya cece su ta hannun Yerobowam na biyu.

28 Sauran ayyukan Yerobowam na biyu, da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, da yaƙi da ya yi, da yadda ya ƙwato wa Isra’ila Dimashƙu da Hamat waɗanda suke na Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

29 Yerobowam na biyu kuwa ya mutu, kamar kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa ya gaji sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 15

Sarki Azariya na Yahuza

1 A shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Yerobowam na biyu Sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki shekara hamsin da biyu a Urushalima. Sunan tsohuwarsa, Yekoliya ta Urushalima.

3 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda Amaziya, tsohonsa, ya yi.

4 Duk da haka ba a kawar da wuraren tsafi na kan tuddai ba. Mutane suka yi ta miƙa hadayu da ƙona turare a wuraren tsafi na kan tuddai.

5 Sai Ubangiji ya buge shi da kuturta, ya kuwa zama kuturu har ran da ya rasu. Ya zauna a wani gida a ware. Sai Yotam ɗansa ya zama wakilin gidan, yana kuma mulkin jama’ar ƙasar.

6 Sauran ayyukan Azariya, da dukan abin da ya yi an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

7 Azariya ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda. Yotam ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Zakariya na Isra’ila

8 A shekara ta talatin da takwas ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Zakariya ɗan Yerobowam na biyu, ya ci sarautar Isra’ila a Samariya wata shida.

9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda kakanninsa suka yi. Bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

10 Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla masa maƙarƙashiya, ya buge shi a Ibleyam, ya kashe shi, sa’an nan ya hau gadon sarautarsa.

11 Sauran ayyukan da Zakariya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

12 Wannan shi ne alkawarin da Ubangiji ya yi wa Yehu, cewa ‘ya’yansa maza za su zauna a gadon sarautar Isra’ila har tsara ta huɗu. Haka kuwa ya zama.

Sarki Shallum na Isra’ila

13 Shallum ɗan Yabesh ya ci sarauta a shekara ta talatin da tara ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza. Ya yi mulki wata ɗaya a Samariya.

14 Menahem ɗan Gadi daga Tirza ya zo Samariya ya bugi Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya hau gadon sarautarsa.

15 Sauran ayyukan Shallum duk da makircin da ya ƙulla, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

16 A lokacin nan sai Menahem ya hallaka Tifsa da dukan waɗanda suke cikinta, da karkararta tun daga Tirza, domin ba su karɓe shi ba, saboda haka ya hallaka ta, ya tsattsage dukan matan da suke da juna biyu.

Sarki Menahem na Isra’ila

17 A shekara ta talatin da tara ta sarautar Azariya, Sarkin Yahuza, Menahem ɗan Gadi, ya ci sarautar. Ya yi shekara goma a Samariya.

18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A dukan kwanakinsa bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

19 Tiglatfilesar, mai mulkin Assuriya, ya kawo wa ƙasar yaƙi, Menahem kuwa ya ba Tiglat-filesar talanti dubu (1,000) na azurfa, don dai ya taimake shi yadda sarautarsa za ta kahu sosai.

20 Menahem ya karɓi kuɗin daga mutanen Isra’ila, wato daga attajirai. Ya tilasta wa kowannensu ya ba da azurfa hamsin. Saboda haka Tiglat-filesar mai mulkin Assuriya ya koma ƙasarsa.

21 Sauran ayyukan Menahem, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

22 Menahem ya mutu, ɗansa Fekahiya ya gaji sarautarsa.

Sarki Fekahiya na Isra’ila

23 A shekara ta hamsin ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Fekahiya ɗan Menahem, ya ci sarautar Isra’ila a Samariya. Ya yi mulki shekara biyu.

24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

25 Sai shugaban sojojinsa, wato Feka, ɗan Remaliya daga Gileyad, tare da mutum hamsin suka ƙulla maƙarƙashiya, suka kashe Fekahiya tare da Argob da Ariye a Samariya a fādarsa. Da suka kashe shi, sai Feka ya zama sarki.

26 Sauran ayyukan Fekahiya, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

Sarki Feka na Isra’ila

27 A shekara ta hamsin da biyu ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Feka ɗan Remaliya ya ci sarautar Isra’ila a Samariya. Ya yi mulki shekara ashirin.

28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra’ila su yi zunubi.

29 A zamanin Feka Sarkin Isra’ila, sai Tiglat-filesar mai mulkin Assuriya, ya zo ya ci Iyon, da Abel-bet-ma’aka, da Yanowa, da Kedesh, da Hazor, da Gileyad, da Galili, da dukan ƙasar Naftali. Sa’an nan ya kwashe mutane zuwa bauta a Assuriya.

30 Hosheya ɗan Ila kuwa ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya, ya buge shi ya kashe shi, sa’an nan ya ci sarauta a shekara ta ashirin ta sarautar Yotam ɗan Azariya.

31 Sauran ayyukan Feka da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra’ila.

Sarki Yotam na Yahuza

32 A shekara ta biyu ta sarautar Feka ɗan Remaliya Sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Azariya Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

33 Yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya ci sarautar. Ya yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yerusha, ‘yar Zadok.

34 Yotam ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa, Azariya, ya yi.

35 Duk da haka ba a kawar da wuraren tsafi na kan tuddai ba, amma mutane suka yi ta miƙa hadayu da ƙona turare a matsafai na kan tuddai. Shi ne ya gina ƙofa ta bisa ta Haikalin Ubangiji.

36 Sauran ayyukan Yotam, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

37 A kwanakin nan Ubangiji ya fara aiken Rezin Sarkin Suriya da Feka ɗan Remaliya su yi yaƙi da Yahuza.

38 Yotam ya rasu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin kakansa Dawuda. Sai Ahaz ɗansa ya gaji sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 16

Sarki Ahaz na Yahuza

1 A shekara ta goma sha bakwai ta sarautar Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam Sarkin Yahuza, ya ci sarauta.

2 Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya ci sarautar, ya kuwa yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima. Bai yi abin da yake da kyau a gaban Ubangiji Allahnsa ba, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.

3 Ya bi halin sarakunan Isra’ila. Har ma ya yi hadaya ta ƙonawa da ɗansa, kamar mugayen ayyukan al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban mutanen Isra’ila.

4 Ya kuma miƙa hadaya da turaren ƙonawa a wuraren tsafi na kan tuddai da ƙarƙashin itatuwa masu duhuwa.

5 Rezin Sarkin Suriya kuwa, da Feka ɗan Remaliya Sarkin Isra’ila, suka kawo wa Urushalima yaƙi. Suka kewaye Ahaz da yaƙi, amma ba su ci shi ba.

6 A lokacin nan kuma Sarkin Edom ya sāke ƙwace Elat, ya kori Yahudawa daga cikinta, Edomawa suka zo suka zauna a ciki har wa yau.

7 Ahaz kuwa ya aiki manzanni wurin Tiglat-filesar, mai mulkin Assuriya, ya ce, “Ni baranka ne, ɗanka kuma, ka zo ka cece ni daga hannun Sarkin Suriya da Sarkin Isra’ila, waɗanda suke yaƙi da ni.”

8 Ahaz kuma ya kwashe azurfa da zinariya da suke cikin Haikalin Ubangiji, da wadda take cikin baitulmalin sarki, ya aika wa mai mulkin Assuriya kyauta.

9 Tiglat-filesar ya ji roƙonsa, sai ya zo ya faɗa wa Dimashƙu da yaƙi, ya ci ta. Sa’an nan ya kwashe mutane zuwa Kir. Ya kuma kashe sarki Rezin.

10 Sa’ad da sarki Ahaz ya tafi Dimashƙu don ya sadu da Tiglat-filesar, Sarkin Assuriya, ya ga bagaden da yake a Dimashƙu, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayaninsa.

11 Uriya firist kuwa, ya gina bagaden bisa ga yadda sarki Ahaz ya aika masa daga Dimashƙu. Uriya firist, ya gina bagaden kafin sarki Ahaz ya komo daga Dimashƙu.

12 Da sarki ya komo daga Dimashƙu, ya hango bagaden, sai ya tafi kusa da shi.

13 Sa’an nan ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa, da hadayarsa ta gari, da hadayarsa ta sha, ya yayyafa jinin hadayarsa ta salama a bisa bagaden.

14 Sai ya kawar da bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi arewacin sabon bagadensa.

15 Sarki Ahaz ya umarci Uriya firist cewa, “Sai ka miƙa hadaya ta ƙonawa ta safe, da hadaya ta gari ta maraice, da hadaya ta ƙonawa ta sarki, da hadayarsa ta gari, da hadaya ta ƙonawa ta dukan jama’ar ƙasar, da hadayarsu ta gari, da hadayarsu ta sha, ka yayyafa dukan jinin hadaya ta ƙonawa, da dukan jinin hadayu a bisa babban bagaden. Amma bagaden tagulla zai zama nawa don yin ibada.”

16 Uriya firist kuwa, ya yi dukan abin da sarki Ahaz ya umarta.

17 Sarki Ahaz kuwa ya yanke sassan dakalan, ya ɗauke daruna da suke bisansu, ya kuma ɗauke kwatarniya da take bisa bijimai na tagulla, ya ajiye kwatarniya a daɓen dutse.

18 Hanyar da aka killace ta Asabar, wadda suka yi a cikin gidan, da ƙofar waje ta shigar sarki, Ahaz ya kawar da su daga Haikalin Ubangiji saboda Sarkin Assuriya.

19 Sauran ayyukan Ahaz waɗanda ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.

20 Ahaz ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Sai ɗansa, Hezekiya, ya gaji sarautarsa.

Categories
2 SAR

2 SAR 17

Faɗuwar Samariya da Bautar Isra’ila

1 A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Ahaz Samariya Yahuza, Hosheya ɗan Ila ya ci sarautar Isra’ila a Samariya. Ya yi mulki shekara tara.

2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar sauran sarakunan Isra’ila da suka riga shi ba.

3 Sai Shalmanesar Sarkin Assuriya, ya kawo masa yaƙi, Hosheya kuwa ya zama talakansa, yana kai masa haraji.

4 Amma Sarkin Assuriya ya gane Hosheya ya tayar masa, gama ya aiki manzanni wurin So, wato Sarkin Masar, ya kuma ƙi ya kai wa Sarkin Assuriya haraji kamar yadda ya saba yi kowace shekara, Saboda haka sai Sarkin Assuriya ya kama shi ya sa shi a kurkuku.

5 Sa’an nan Sarkin Assuriya ya kai wa dukan ƙasar yaƙi, har ya kai Samariya. Ya kewaye Samariya da yaƙi shekara uku.

6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, Sarkin Assuriya ya ci Samariya, ya kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa.

7 Wannan abu ya sami Isra’ila saboda sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fito da su daga ƙasar Masar, daga hannun Fir’auna, Sarkin Masar. Suka bauta wa gumaka.

8 Suka bi al’adun al’ummai waɗanda Ubangiji ya kora a gabansu, da al’adun da sarakunan Isra’ila suka kawo.

9 Jama’ar Isra’ila kuma suka yi wa Ubangiji Allahnsu abubuwan da ba daidai ba, daga ɓoye. Sun gina wa kansu matsafai a dukan garuruwansu daga hasumiya zuwa birni mai garu.

10 Suka kuma kafa wa kansu ginshiƙai da siffofin gumakan Ashtarot a kowane tudu da a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa.

11 Suka ƙona turare a kan wuraren tsafi na kan tuddai kamar yadda al’ummar da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka aikata mugayen abubuwa, suka su Ubangiji ya yi fushi.

12 Suka bauta wa gumaka waɗanda Ubangiji ya ce musu kada su bauta musu.

13 Amma Ubangiji ya faɗakar da jama’ar Isra’ila da jama’ar Yahuza ta bakin annabawa da kowane maigani, cewa su bar mugayen hanyoyinsu, su kiyaye umarnansa da dukan dokokinsa waɗanda ya umarci kakanninsu da su, waɗanda kuma ya aiko musu ta wurin bayinsa annabawa.

14 Duk da haka suka ƙi kasa kunne, suka taurare zuciyarsu kamar yadda kakanninsu suka yi, waɗanda ba su yi imani da Ubangiji Allahnsu ba.

15 Suka yi watsi da dokokinsa, da alkawarinsa da ya yi wa kakanninsu, da kuma faɗakarwar da ya yi musu. Suka bi gumakan banza, suka zama banza, suka bi halin al’ummai da suke kewaye da su, waɗanda Ubangiji ya umarce su kada su yi kamarsu.

16 Suka bar dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu siffofin zubi na ‘yan maruƙa biyu, suka yi gunkiyan nan, Ashtoret, suka yi wa taurari sujada, suka bauta wa Ba’al.

17 Suka yi hadaya ta ƙonawa da ‘ya’yansu mata da maza. Suka yi duba, suka yi sihiri, suka duƙufa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji, suka sa shi ya yi fushi.

18 Saboda wannan Ubangiji ya husata da jama’ar Isra’ila, ya kawar da su daga gabansa, ba wanda aka rage, sai dai kabilar Yahuza.

19 Jama’ar Yahuza kuma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba, sai suka bi al’adun da mutanen Isra’ila suka kawo.

20 Ubangiji kuwa ya ƙi dukan zuriyar Isra’ila, ya wahalshe su, ya kuma bashe su a hannun mugayen abokan gāba, ta haka ya kawar da su daga gabansa.

21 Sa’ad da Ubangiji ya ɓalle Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat ya zama sarki. Yerobowam kuwa ya karkatar da jama’ar Isra’ila daga bin Ubangiji. Ya sa su suka aikata babban zunubi.

22 Jama’ar Isra’ila suka yi ta aikata dukan zunuban da Yerobowam ya yi, ba su daina aikata su ba.

23 har lokacin da Ubangiji ya kawar da su daga gabansa kamar yadda ya faɗa ta bakin bayinsa, annabawa. Saboda haka aka fitar da jama’ar Isra’ila daga ƙasarsu zuwa Assuriya har wa yau.

An Zaunar da Assuriyawa cikin Isra’ilawa

24 Sarkin Assuriya kuwa ya kawo mutane daga Babila, da Kuta, da Awwa, da Hamat, da Sefarwayim, ya zaunar da su a garuruwan Samariya a maimakon jama’ar Isra’ila. Sai suka mallaki Samariya, suka zauna a garuruwanta.

25 A farkon zamansu a can, ba su yi tsoron Ubangiji ba saboda haka Ubangiji ya aika da zakoki a cikinsu, suka karkashe waɗansu daga cikinsu.

26 Sai aka faɗa wa Sarkin Assuriya cewa, “Al’umman da ka kwashe ka zaunar da su a garuruwan Samariya ba su san shari’ar Allahn ƙasar ba, domin haka ya aiki zakoki a cikinsu, suna ta karkashe su.”

27 Sa’an nan Sarkin Assuriya ya umarta a aiki firist ɗaya daga cikin firistocin da aka kwashe daga can, ya tafi, ya zauna can domin ya koya musu shari’ar Allahn ƙasar.

28 Sai firist ɗaya daga cikin firistocin da suka kwashe daga Samariya, ya zo, ya zauna a Betel. Shi kuwa ya koya musu yadda za su yi tsoron Ubangiji.

29 Amma duk da haka kowace al’umma ta riƙa yin gumakanta, tana ajiye su a wuraren yin tsafin na kan tuddai waɗanda Samariyawa suka gina. Kowace al’umma kuma ta yi haka a garin da ta zauna.

30 Mutanen Babila suka yi Sukkot-benot, mutanen Kuta suka yi Nergal, mutanen Hamat suka yi Ashima.

31 Awwiyawa suka yi Nibhaz da Tartak, mutanen Sefarwayim suka miƙa ‘ya’yansu hadaya ta ƙonawa ga Adrammelek da Anammelek, gumakansu.

32 Su ma suka yi tsoron Ubangiji, suka sa mutane iri dabam dabam su zama firistocin wuraren tsafinsu na kan tuddai. Firistocin nan suka miƙa hadayu dominsu a ɗakunan tsafinsu na kan tuddai.

33 Waɗannan mutane su ma suka yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka bauta wa gumakansu ta hanyar da al’umman da aka kwaso su daga cikinsu suke yi.

34 Har wa yau suna yin yadda suka yi a dā. Ba su yi tsoron Ubangiji ba, ba su bi dokoki, ko ka’idodi, ko shari’a, ko umarnan Ubangiji ba, waɗanda ya umarci ‘ya’yan Yakubu, wanda ya sa wa suna Isra’ila.

35 Ubangiji ya yi alkawari da ‘ya’yan Yakubu, ya kuma umarce su kada su yi wa gumaka sujada ko su durƙusa musu, ko su bauta musu, ko su miƙa musu hadayu.

36 Amma su yi tsoron Ubangiji, wanda ya fisshe su daga ƙasar Masar da iko mai girma da ƙarfi, shi za su yi wa sujada, shi kuma za su miƙa wa hadayu.

37 Sai su yi biyayya da dokokinsa da umarnansa da ya rubuta musu. Kada su ji tsoron waɗansu alloli.

38 Kada su manta da alkawarin da ya yi da su, kada kuma su ji tsoron gumaka.

39 Amma su yi tsoron Ubangiji Allahnsu, shi kuwa zai cece su daga hannun dukan abokan gābansu.

40 Duk da haka ba su kasa kunne ba, amma suka yi kamar yadda suka saba yi tun dā.

41 Waɗannan al’ummai suka yi wa Ubangiji sujada, amma suka kuma yi ta bauta wa gumakansu. Haka kuma ‘ya’yansu da jikokinsu suka yi kamar yadda kakanninsu suka yi. Haka suke yi har wa yau.