Categories
1 TAR

1 TAR 3

‘Ya’yan Dawuda

1-3 Waɗannan su ne ‘ya’yan Dawuda, maza, waɗanda aka haifa masa a Hebron.

Amnon wanda Ahinowam Bayezreyeliya ta haifa masa.

Kileyab wanda Abigail Bakarmeliya ta haifa masa.

Absalom ɗan Ma’aka ‘yar Talmai, Sarkin Geshur.

Adonaija ɗan Haggit.

Shefatiya wanda Abital ta haifa.

Itireyam wanda Egla ta haifa.

4 Dukansu shida an haife su ne a Hebron inda ya yi sarauta shekara bakwai da wata shida.

Ya yi sarauta a Urushalima shekara talatin da uku.

5 Waɗanda aka haifa masa a Urushalima, su ne Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu, su huɗu ke nan waɗanda Bat-sheba ‘yar Ammiyel ta haifa masa.

6 Yana da waɗansu ‘ya’ya kuma, su ne Ibhar, da Elishuwa da Elifelet,

7 da Noga, da Nefeg, da Yafiya,

8 da Elishama, da Eliyada, da kuma Elifelet, su tara ke nan.

9 Waɗannan duka su ne ‘ya’yan Dawuda, maza, banda ‘ya’yan ƙwaraƙwarai. Tamar ita ce ‘yar’uwarsu.

Zuriyar Sulemanu

10 Waɗannan su ne zuriyar Sulemanu, daga Rehobowam, sai Abaija, da Asa, da Yehoshafat,

11 da Yoram, da Ahaziya, da Yowash,

12 da Amaziya, da Azariya, da Yotam,

13 da Ahaz, da Hezekiya da Manassa,

14 da Amon, da Yosiya.

15 ‘Ya’yan Yosiya, maza, su ne Yohenan ɗan farinsa, na biyu shi ne Eliyakim, na uku shi ne Zadakiya, na huɗu shi ne Yehowahaz,

16 Eliyakim yana da ‘ya’ya biyu maza, su ne Yekoniya, da Zadakiya.

17 ‘Ya’yan Yekoniya wanda aka kama, su ne Sheyaltiyel,

18 da Malkiram, da Fedaiya, da Shenazzar, da Yekamiya, da Hoshama, da Nedabiya.

19 Fedaiya yana da ‘ya’ya biyu maza, su ne Zarubabel da Shimai. ‘Ya’yan Zarubabel, maza, su ne Meshullam, da Hananiya, da Shelomit ‘yar’uwarsu,

20 da Hashuba, da Ohel, da Berikiya, da Hasadiya, da Yushab-hesed, su biyar ke nan.

21 ‘Ya’yan Hananiya, maza, su ne Felatiya, da Yeshaya, da ‘ya’yan Refaya, maza, da ‘ya’yan Arnan, maza, da ‘ya’yan Obadiya, maza, da ‘ya’yan Shekaniya, maza.

22 Ɗan Shekaniya shi ne Shemaiya. ‘Ya’yan Shemaiya, maza, su ne Hattush, da Igal, da Bariya da Neyariya, da Shafat, su shida ke nan.

23 ‘Ya’yan Neyariya, maza, su ne Eliyehoyenai, da Hezekiya, da Azrikam, su uku ne nan.

24 ‘Ya’yan Eliyehoyenai, maza, su ne Hodawiya, da Eliyashib, da Felaya, da Akkub, da Yohenan, da Dalaya, da Anani, su bakwai ke nan.

Categories
1 TAR

1 TAR 4

Zuriyar Yahuza

1 ‘Ya’yan Yahuza, maza, su ne Feresa, da Hesruna, da Karmi, da Hur, da Shobal.

2 Rewaiya ɗan Shobal, shi ne mahaifin Yahat. Yahat shi ya haifi Ahumai, da Lahad. Waɗannan su ne iyalin Zoratiyawa.

3 Waɗannan kuma su ne ‘ya’yan Itam, Yezreyel, da Ishma, da Idbasha, da ‘ya ɗaya, ita ce Hazzelelfoni.

4 Feniyel shi ne mahaifin Gedor, Ezer kuwa shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne ‘ya’yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, zuriyarsa ne suka kafa Baitalami.

5 Ashur, wanda ya kafa Tekowa, yana da mata biyu, su ne Hela, da Nayara.

6 Nayara ta haifa masa Ahuzzam, da Hefer, da Temeni, da Hayahashtari. Waɗannan su ne ‘ya’yan Nayara, maza.

7 ‘Ya’yan Hela, maza, su ne Zeret, da Izhara, da Etnan.

8 Hakkoz shi ne mahaifin Anub, da Zobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum.

9 Yabez ya fi sauran ‘yan’uwansa kwarjini saboda haka mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, wato da wahala ta haife shi.

10 Yabez ya roƙi Allah na Isra’ila, ya ce, “Ka sa mini albarka, ka faɗaɗa kan iyakata, hannunka kuma ya kasance tare da ni, ka kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni.” Allah kuwa ya biya masa bukatarsa.

11 Kalibu ɗan’uwan Shuwa, shi ne mahaifin Mehir wanda ya haifi Eshton.

12 Eshton kuwa shi ne ya haifi Bet-rafa, da Faseya, da Tehinna wanda ya kafa birnin Ir-nahash, zuriyar waɗannan mutane kuwa su suka zauna a Reka.

13 ‘Ya’yan Kenaz, maza, su ne Otniyel da Seraiya. Yana kuma da waɗansu ‘ya’ya maza, su ne Hatata da Meyonotai.

14 Meyonotai kuwa shi ne mahaifin Ofra.

Seraiya shi ne ya haifi Yowab, Yowab ya kafa kwarin Ge-harashim, saboda su masu sana’a ne.

15 ‘Ya’yan Kalibu, maza, ɗan Yefunne, su ne Airu, da Ila, da Na’am. Ila shi ya haifi Kenaz.

16 ‘Ya’yan Yehallelel, maza, su ne Zif, da Zifa, da Tiriya, da Asarel.

17-18 ‘Ya’yan Ezra, maza, su ne Yeter, da Mered, da Efer, da Yalon. Bitiya ‘yar Fir’auna, wadda Mered ya aura, ta haifi waɗannan, Maryamu, da Shammai, da Ishaba wanda ya haifi Eshtemowa. Mered kuma ya auri wata daga kabilar Yahuza, ta haifi Yered wanda ya kafa garin Gedor. Eber kuma ya kafa garin Soko, Yekutiyel kuwa ya kafa garin Zanowa.

19 ‘Ya’ya maza na matar Hodiya ‘yar’uwar Naham, su ne suka zama kakannin Kaila, Bagarme, da Eshtemowa da suke zaune a Ma’aka.

20 ‘Ya’yan Shimon, maza, su ne Amnon, da Rinna, da Ben-hanan, da Tilon.

‘Ya’yan Ishi, maza kuwa, su ne Zohet da Ben-zohet.

21 ‘Ya’yan Shela, maza, ɗan Yahuza, su ne Er wanda ya kafa garin Leka, da La’ada wanda ya kafa garin Maresha, da iyalan gidan masu aikin lilin da suke zaune a Bet-ashbeya,

22 da Yokim, da mutanen da suke zaune a Kozeba, da Yowash, da Saraf, waɗanda suka yi sarauta a Mowab, sa’an nan suka zauna a Baitalami. (Waɗannan labaru na tun dā ne.)

23 Su ne maginan tukwane, waɗanda suke zaune a Netayim da Gedera. Sun zauna tare da sarki don su yi masa aiki.

Zuriyar Saminu

24 ‘Ya’yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin, da Zohar, da Shawul,

25 da Shallum ɗansa, da Mibsam jīkansa, da Mishma jīkan ɗansa.

26 ‘Ya’yan Mishma, maza, su ne Hammuwel, da Zakkur, da Shimai.

27 Shimai yana da ‘ya’ya maza goma sha shida, da ‘ya’ya mata shida, amma ‘yan’uwansa ba su da ‘ya’ya da yawa kamarsa. Iyalin Saminu ba su kai yawan na Yahuza ba.

28 Suka zauna a waɗannan garuruwa, wato Biyer-sheba, da Molada, da Hazar-shuwal,

29 da Bilha, da Ezem, da Eltola,

30 da Betuwel, da Horma, da Ziklag,

31 da Bet-markabot, da Hazarsusa, da Bet-biri, da Shayarim. Waɗannan su ne biranensu tun kafin Dawuda ya yi sarauta.

32-33 Sun kuwa zauna a waɗansu wurare guda biyar, wato Itam, da Ayin, da Rimmon, da Token, da Ashan, da ƙauyukan da suke kewaye, har zuwa kudu maso gabas da garin Ba’al: Ga lissafin iyalansu da wuraren da suka zauna.

34-37 Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya,

Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya, wato jīkan Seraiya, ɗan Asiyel,

Eliyehoyenai, da Ya’akoba, da Yeshohaya, da Asaya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benaiya,

Ziza ɗan Shifi, wato jīkan Allon, zuriyar Yedaiya, da Shimri ɗan Shemaiya.

38 Waɗannan da aka jera sunayensu, su ne shugabannin iyalansu da gidajen kakanninsu.

Sun ƙaru ƙwarai.

39 Suka yi tafiya har zuwa mashigin Gedor, zuwa gabashin kwarin don nemar wa garkunansu makiyaya.

40 A can suka sami makiyaya mai kyau mai dausayi. Ƙasar kuwa tana da faɗi, babu fitina, sai salama, gama mazaunan wurin a dā Hamawa ne.

41 Waɗannan da aka lasafta sunayensu, su ne suka zo a kwanakin Hezekiya Sarkin Yahuza, suka fāɗa wa alfarwai da bukkoki waɗanda suka tarar a can, suka hallaka su sarai, sa’an nan suka maye wurinsu saboda akwai makiyaya domin garkunansu a wurin.

42 Waɗansu daga cikinsu, mutum ɗari biyar daga zuriyar Saminu, suka tafi wajen gabashin Edom. Waɗanda suka shugabance su kuwa, su ne ‘ya’yan Ishi, wato Felatiya, da Neyariya, da Refaya, da Uzziyel.

43 A can suka karkashe sauran Amalekawan da suka ragu, sa’an nan suka zauna a can har wa yau.

Categories
1 TAR

1 TAR 5

Zuriyar Ra’ubainu

1 Ra’ubainu shi ne ɗan farin Isra’ila, amma saboda ya ƙazantar da gadon mahaifinsa aka ba ‘ya’yan Yusufu, maza, ɗan Isra’ila, gādonsa na ɗan fari. Don haka ba a lasafta shi a kan matsayin ɗan fari ba.

2 Ko da yake Yahuza ya rinjayi ‘yan’uwansa, har daga gare shi aka sami shugaba, duk da haka matsayin ɗan farin na Yusufu ne.

3 ‘Ya’yan Ra’ubainu, maza, wato ɗan farin Isra’ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi.

4 ‘Ya’yan Yowel, maza, su ne Shemaiya, da Gog, da Shimai,

5 da Mika, da Rewaiya, da Ba’al,

6 da Biyera wanda Tiglat-filesar Sarkin Assuriya ya kai bauta. Shi ne shugaban Ra’ubainawa.

7 Danginsa bisa ga iyalansu da asalinsu a zamaninsu, su ne sarki Yehiyel, da Zakariya,

8 da Bela ɗan Azaz, wato jīkan Shema, ɗan Yowel, wanda ya zauna a Arower har zuwa Nebo da Ba’al-meyon.

9 Ya kuma zauna wajen gabas, har zuwa goshin jejin da yake wajen Kogin Yufiretis, saboda shanunsu sun ƙaru a ƙasar Gileyad.

10 Zuriyar Ra’ubainu suka yi yaƙi da Hagarawa a kwanakin Saul. Suka ci Hagarawa, saboda haka suka zauna a ƙasar da take gabashin Gileyad.

Zuriyar Gad

11 ‘Ya’yan Gad, maza, suka zauna a ƙasar Bashan, daura da Ra’ubainawa har zuwa Salka.

12 Yowel ne sarki, Shafam kuwa shi ne na biyun, da Yanai, da Shafat, su ne tushen Bashan.

13 Danginsu bisa ga gidajen kakanninsu, su ne Maikel, da Meshullam, da Sheba, da Yorai, da Jakan, da Ziya, da Eber, su bakwai ke nan.

14 Waɗannan su ne ‘ya’ya maza na Abihail ɗan Huri. Ga yadda kakanninsu suke, wato Abihail, ɗan Huri ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Maikel, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.

15 Ahi ɗan Abdiyel, wato jīkan Guni, shi ne shugaban gidan kakanninsu.

16 Suka zauna a Gileyad, da Bashan, da garuruwanta, da dukan iyakar makiyayar Sharon.

17 (An rubuta waɗannan duka bisa ga asalinsu a zamanin Yotam, Sarkin Yahuza, da Yerobowam Sarkin Isra’ila.)

Tarihin Kabilai Biyu da Rabi

18 ‘Ya’yan Ra’ubainu, maza, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa suna da jarumawa masu riƙon garkuwa da takobi, masu harbi kuma da baka. Gwanayen yaƙi ne, su dubu arba’in da huɗu, da ɗari bakwai da sittin ne (44,760).

19 Suka yi yaƙi da Hagarawa, da Yetur, da Nafish, da Nodab.

20 Aka taimake su yin yaƙi da abokan gābansu, sai aka ba da Hagarawa da duk waɗanda suke tare da su a hannunsu, saboda suka yi roƙo ga Allah a cikin yaƙin, Allah kuwa ya amsa musu roƙonsu saboda sun dogara gare shi.

21 Sai suka kwashe dabbobinsu, raƙuma dubu hamsin (50,000), da tumaki dubu ɗari biyu da dubu hamsin (250,000), da jakuna dubu biyu (2,000), da kuma mutane dubu ɗari (100,000).

22 Aka karkashe mutane da yawa, domin yaƙin na Allah ne. Sai suka gāje wurin zamansu, har lokacin da aka kai su bauta.

23 Mutanen rabin kabilar Manassa suna da yawa, sun zauna a ƙasar, daga Bashan har zuwa Ba’al-harmon, da Senir, da Dutsen Harmon.

24 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu, Efer, da Ishi, da Eliyel, da Azriyel, da Irmiya, da Hodawiya, da Yadiyel. Su jarumawa ne na gaske, masu suna, su ne shugabannin gidajen kakanninsu.

25 Amma mutanen suka yi rashin gaskiya ga Allah na kakanninsu, suka bi gumakan mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.

26 Don haka Allah na Isra’ila ya zuga Ful, Sarkin Assuriya, wato Tiglat-filesar, ya zo ya kwashe su, ya kai su bauta, wato su Ra’ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa. Ya kai su Hala, da Habor, da Hara, har zuwa kogin Gozan, can suke har yau.

Categories
1 TAR

1 TAR 6

Zuriyar Manyan Firistoci

1 ‘Ya’yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari.

2 ‘Ya’yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel.

3 ‘Ya’yan Amram kuwa, su ne Haruna, da Musa, da Maryamu.

‘Ya’yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele’azara, da Itamar.

4 Zuriyar Ele’azara daga tsara zuwa tsara, su ne Finehas, da Abishuwa,

5 da Bukki, da Uzzi,

6 da Zarahiya, da Merayot,

7 da Amariya, da Ahitub,

8 da Zadok, da Ahimawaz,

9 da Azariya, da Yohenan,

10 da Azariya wanda ya yi hidimar firist a Haikalin da Sulemanu ya gina a Urushalima.

11 Ga Amariya kuma da Ahitub,

12 da Zakok, da Meshullam,

13 da Hilkiya, da Azariya,

14 da Seraiya, da Yehozadak.

15 Sarki Nebukadnezzar ya kama Yehozadak, ya tafi da shi tare da sauran jama’a zuwa zaman talala, sa’ad da Ubangiji ya ba da su a hannun Nebukadnezzar don su yi zaman talala.

Sauran Zuriyar Lawi

16 ‘Ya’yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari.

17 Waɗannan su ne sunayen ‘ya’yan Gershon, maza, Libni da Shimai.

18 ‘Ya’yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel.

19 ‘Ya’yan Merari, maza kuwa, su ne Mali da Mushi. Waɗannan su ne iyalan Lawiyawa bisa ga gidajen kakanninsu.

20 Zuriyar Gershon bi da bi, su ne Libni, da Yahat, da Zimma,

21 da Yowa, da Iddo, da Zera, da Yewaterai.

22 Zuriyar Kohat bi da bi, su ne Izhara, da Kora, da Assir,

23 da Elkana, da Ebiyasaf, da Assir,

24 da Tahat, da Uriyel, da Azariya, da Shawul.

25 ‘Ya’yan Elkana, maza, su ne Amasai da Ahimot.

26 Zuriyar Ahimot bi da bi, su ne Elkana, da Zofai, da Nahat,

27 da Eliyab, da Yeroham, da Elkana.

28 ‘Ya’yan Sama’ila, maza, su ne Yowel ɗan farinsa, na biyun shi ne Abaija.

29 Zuriyar Merari bi da bi, su ne Mali, da Libni, da Shimai, da Uzza,

30 da Shimeya, da Haggiya, da Asaya.

Masu Bushe-bushe a Haikali da Dawuda Ya Zaɓa

31 Waɗannan su ne waɗanda Dawuda ya sa su su zama mawaƙa a Haikalin Ubangiji, sa’ad da aka kawo akwatin alkawari a cikin Haikalin.

32 Suka yi ta raira waƙoƙi a gaban wurin zama na alfarwa ta taruwa tun kafin Sulemanu ya gina Haikalin Ubangiji a Urushalima. Suka yi hidima bisa ga matsayinsu ta yadda aka tsara.

33 Waɗannan su ne waɗanda suka yi ta raira waƙoƙin, su da ‘ya’yansu maza.

Daga iyalin Kohat, Heman shi ne shugaban ƙungiyar farko ta mawaƙa, shi ɗan Yowel ne, ɗan Sama’ila,

34 ɗan Elkana, ɗan Yeroham, ɗan Eliyab, ɗan Mahat,

35 ɗan Zafai, ɗan Elkana, ɗan Mahat, ɗan Amasai,

36 ɗan Elkana, ɗan Shawul, ɗan Azariya, ɗan Uriyel,

37 ɗan Tahat, ɗan Assir, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora,

38 ɗan Izhara, ɗan Kohat, ɗan Lawi, ɗan Isra’ila.

39 Asaf kuma shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta biyu. Shi ɗan Berikiya ne, ɗan Shimeya,

40 ɗan Maikel, ɗan Ba’aseya, ɗan Malkiya,

41 ɗan Yewaterai, ɗan Zera, ɗan Iddo,

42 ɗan Yowa, ɗan Zimma, ɗan Shimai,

43 ɗan Yahat, ɗan Gershon, ɗan Lawi.

44 Etan na zuriyar Merari, shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta uku, asalinsa shi ɗan Kishi ne, ɗan Abdi, ɗan Malluki,

45 ɗan Hashabiya, ɗan Amaziya, ɗan Hilkiya,

46 ɗan Amzi, ɗan Bani, ɗan Shemer,

47 ɗan Mali, ɗan Mushi, ɗan Merari, ɗan Lawi.

48 Aka sa ‘yan’uwansu, Lawiyawa, su yi dukan hidimomi a cikin Haikalin Ubangiji.

Zuriyar Haruna

49 Amma Haruna da ‘ya’yansa maza suka miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa, da kan bagaden ƙona turare, domin dukan aikin Wuri Mafi Tsarki, da kuma yin kafara domin Isra’ila bisa ga dukan abin da Musa, bawan Allah, ya umarta.

50 Waɗannan su ne zuriyar Haruna, maza, bi da bi, Ele’azara, da Finehas, da Abishuwa,

51 da Bukki, da Uzzi, da Zerahiya,

52 da Merayot, da Amariya, da Ahitub,

53 da Zadok da Ahimawaz.

Inda Zuriyar Haruna Suka Zauna

54 Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna, na iyalin Kohat. Sun karɓi rabo na farko a ƙasar.

55 Rabonsu ya haɗu da Hebron ta yankin ƙasar Yahuza, da makiyayar da suke kewaye da ita.

56 Amma an ba Kalibu ɗan Yefunne saurukan birnin, tare da ƙauyukansa.

57 Suka ba ‘ya’yan Haruna, maza, biranen mafaka, wato Hebron, da Libna tare da makiyayarta, da Yattir, da Eshtemowa tare da makiyayarta,

58 da Holon tare da makiyayarta, da Debir tare da makiyayarta,

59 da Ayin tare da makiyayarta, da Bet-shemesh tare da makiyayarta.

60 Daga kabilar Biliyaminu aka ba su Geba tare da makiyayarta, da Allemet tare da makiyayarta, da Anatot tare da makiyayarta. Dukan biranen iyalansu guda goma sha uku ne.

Inda Sauran Lawiyawa Suka Zauna

61 Aka ba sauran ‘ya’yan Kohat, maza, garuruwa goma daga na rabin kabilar Manassa, ta hanyar kuri’a.

62 Aka kuma ba Gershonawa bisa ga iyalansu, birane goma sha uku daga na kabilar Issaka, da na kabilar Ashiru, da na kabilar Naftali, da na kabilar Manassa da take nan a Bashan.

63 Haka kuma aka ba ‘ya’yan Merari, maza, bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga na kabilar Ra’ubainu, da na kabilar Gad, da na kabilar Zabaluna.

64 Haka fa, jama’ar Isra’ila suka ba Lawiyawa garuruwa duk da makiyayansu.

65 Daga na kabilar Yahuza, da na kabilar Saminu, da na kabilar Biliyaminu kuma aka ba da waɗannan garuruwan da aka ambaci sunayensu ta hanyar kuri’a.

66 Waɗansu daga cikin iyalan ‘ya’yan Kohat, maza, sun sami garuruwa na yankinsu daga cikin kabilar Ifraimu.

67 Sai suka ba su waɗannan biranen mafaka, wato Shekem a ƙasar tudu ta Ifraimu duk da makiyayarta, da Gezer tare da makiyayarta,

68 da Yokmeyam duk da makiyayarta, da Bet-horon duk da makiyayarta,

69 da Ayalon duk da makiyayarta, da Gatrimmon duk da makiyayarta.

70 Daga cikin rabin kabilar Manassa kuma an ba su Ta’anak duk da makiyayarta, da Bileyam duk da makiyayarta. An ba da waɗannan ga sauran iyalai na ‘ya’yan Kohat, maza.

71 Daga na rabin kabilar Manassa na gabas, an ba ‘ya’yan Gershon, maza, Golan ta Bashan tare da makiyayarta, da Ashtarot duk da makiyayarta.

72 Daga na kabilar Issaka kuma an ba su Kishiyon duk da makiyayarta, da Daberat duk da makiyayarta,

73 da Ramot duk da makiyayarta, da Enganin duk da makiyayarta.

74 Daga cikin kabilar Ashiru kuma an ba da Mishal duk da makiyayarta, da Abdon duk da makiyayarta,

75 da Helkat duk da makiyayarta, da Rehob duk da makiyayarta.

76 Daga na kabilar Naftali kuma an ba da Kedesh ta Galili duk da makiyayarta, da Hammon duk da makiyayarta, da Kartan duk da makiyayarta.

77 Daga na kabilar Zabaluna, an ba sauran Lawiyawa, wato ‘ya’yan Merari, maza, Rimmon duk da makiyayarta, da Tabor duk da makiyayarta.

78 Daga na kabilar Ra’ubainu a hayin Urdun a Yariko, wato gabashin Urdun, an ba da Bezer ta cikin jeji duk da makiyayarta, da Yahaza duk da makiyayarta,

79 da Kedemot duk da makiyayarta, da Mefayat duk da makiyayarta.

80 Daga na kabilar Gad kuma an ba da Ramot ta Gileyad duk da makiyayarta, da Mahanayim duk da makiyayarta,

81 da Heshbon duk da makiyayarta, da Yazar duk da makiyayarta.

Categories
1 TAR

1 TAR 7

Zuriyar Issaka

1 ‘Ya’yan Issaka, maza, su huɗu ne, wato Tola, da Fuwa, da Yashub, da Shimron.

2 ‘Ya’yan Tola, maza, su ne Uzzi, da Refaya, da Yeriyel, da Yamai, da Ibsam, da Sama’ila, su ne shugabannin gidajen kakanninsu. ‘Ya’yan Tola kuwa manyan mayaƙa ne a zamaninsu. Yawansu a zamanin Dawuda, su dubu ashirin da biyu ne da ɗari shida (22,600).

3 Ɗan Uzzi, shi ne Izrahiya. ‘Ya’yan Izrahiya, maza, su ne Maikel, da Obadiya, da Yowel, da Isshiya. Su biyar duka manyan mutane ne.

4 A zamaninsu, bisa ga gidajen kakanninsu suna da sojoji dubu talatin da dubu shida (36,000) gama suna da mata da yara da yawa.

5 Mayaƙan da aka lasafta bisa ga asalinsu na dukan iyalan Issaka, su dubu tamanin da dubu bakwai ne (87,000), jarumawa ne sosai.

Zuriyar Biliyaminu

6 ‘Ya’yan Biliyaminu su uku ne, wato Bela, da Beker, da Yediyayel.

7 ‘Ya’yan Bela, maza, su biyar ne, wato Ezbon, da Uzzi, da Uzziyel, da Yerimot, da Iri. Su ne shugabannin gidajen kakanninsu, jarumawa ne su. An lasafta su bisa ga asalinsu, su dubu ashirin da biyu ne da talatin da huɗu (22,034).

8 ‘Ya’yan Beker, maza, su ne Zemira, da Yowash, da Eliyezer, da Eliyehoyenai, da Omri, da Yerimot, da Abaija da Anatot, da Alamet. Waɗannan duka ‘ya’yan Beker ne, maza.

9 An lasafta su bisa ga asalinsu a zamaninsu, su dubu ashirin ne da ɗari biyu (20,200), jarumawa ne su sosai. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu.

10 Ɗan Yediyayel shi ne Bilhan. ‘Ya’yan Bilhan, maza, su ne Yewush, da Biliyaminu, da Ehud, da Kena’ana, da Zetan, da Tarshish, da Ahishahar.

11 Duk waɗannan ‘ya’yan Yediyayel, maza ne, bisa ga shugabannin gidajen kakanninsu. Su dubu goma sha bakwai ne da ɗari biyu (17,200), jarumawa ne sosai, shiryayyu don yaƙi.

12 Shuffim da Huffim su ne ‘ya’yan Iri, maza.

Hushim shi ne ɗan Ahiram.

Zuriyar Naftali

13 Naftali yana da ‘ya’ya huɗu, su ne Yazeyel, da Guni, da Yezer, da Shallum. Su ne zuriya daga Bilha.

Zuriyar Manassa

14 ‘Ya’yan Manassa, maza, su ne Asriyel, wanda ƙwarƙwararsa Ba’aramiya ta haifa masa. Ta kuma haifi Makir mahaifin Gileyad.

15 Makir ya auro wa Huffim da Shuffim mata. Sunan ‘yar’uwarsa Ma’aka, sunan ɗan’uwansa kuwa Zelofehad, Zelofehad yana da ‘ya’ya mata kaɗai.

16 Sai Ma’aka matar Makir ta haifi ɗa, ta sa masa suna Feres, sunan ɗan’uwansa kuwa Sheres. ‘Ya’yan Feres maza, su ne Ulam da Rakem.

17 Ɗan Ulam shi ne Bedan. Waɗannan su ne ‘ya’ya maza na Gileyad ɗan Makir, jīkan Manassa.

18 ‘Yar’uwarsa, Hammoleket ta haifi Ishodi, da Abiyezer, da Mala.

19 ‘Ya’yan Shemida, maza, su ne Ahiyan, da Shekem, da Liki, da Aniyam.

Zuriyar Ifraimu

20 ‘Ya’yan Ifraimu, maza, daga tsara zuwa tsara, su ne Shutela, da Bered, da Tahat, da Eleyada, da Tahat,

21 da Zabad, da Shutela, da Ezer, da Eleyad waɗanda mutanen Gat, haifaffun ƙasar, suka kashe sa’ad da suka kai hari don su kwashe dabbobinsu.

22 Sai mahaifinsu, Ifraimu, ya yi ta makoki kwanaki da yawa. ‘Yan’uwansu kuwa suka zo don su yi masa ta’aziyya.

23 Sa’an nan ya shiga wurin matarsa, ta kuwa sami juna biyu, ta haifi ɗa, ya raɗa masa suna Beriya saboda masifar da ta auko wa gidansa.

24 ‘Yarsa kuma ita ce Sheyera, wadda ta gina garin Bet-horon na kwari da na tudu, ta kuma gina Uzzen-sheyera.

25 Waɗansu zuriyarsa bi da bi, su ne Refa, da Reshe, da Tela, da Tahan,

26 da Ladan, da Ammihud, da Elishama,

27 da Nun, da Joshuwa.

28 Mallakarsu da wuraren zamansu, su ne Betel duk da garuruwanta, da Nayaran wajen gabas, da Gezer wajen yamma duk da garuruwanta, da Shekem duk da garuruwanta, har zuwa Ayya duk da garuruwanta.

29 Zuriyar Manassa sun mallaki Bet-sheyan, da Ta’anak, da Magiddo, da Dor duk da garuruwan da suke kewaye da su. A nan ne zuriyar Yusufu, ɗan Isra’ila, suka zauna.

Zuriyar Ashiru

30 ‘Ya’yan Ashiru, maza, su ne Yimna, da Yishuwa, da Yishwi, da Beriya, da ‘yar’uwarsu Sera.

31 ‘Ya’yan Beriya, maza, su ne Eber, da Malkiyel wanda ya kafa garin Birzayit.

32 Eber shi ne mahaifin Yaflet, da Shemer, da Helem, da ‘yar’uwarsu Shuwa.

33 ‘Ya’yan Yaflet, maza, su ne Fasak, da Bimhal, da Ashewat.

34 ‘Ya’yan Shemer maza, su ne Ahi, da Roga, da Yehubba, da Aram.

35 ‘Ya’ya maza na ɗan’uwansa Helem, su ne Zofa, da Imna, da Sheles da Amal.

36 ‘Ya’yan Zofa, su ne Suwa, da Harnefer, da Shuwal, da Beri, da Imra,

37 da Bezer, da Hod, da Shamma, da Shilsha, da Yeter, da Biyera.

38 ‘Ya’yan Yeter, su ne Yefunne, da Fisfa, da Ara.

39 ‘Ya’yan Ulla, maza, su ne Ara, da Haniyel, da Riziya.

40 Waɗannan duka su ne zuriyar Ashiru, su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu. Zaɓaɓɓun jarumawa ne su, manyan sarakuni. Yawansu da aka lasafta bisa ga asalinsu don yaƙi su dubu ashirin da dubu shida ne (26,000).

Categories
1 TAR

1 TAR 8

Zuriyar Biliyaminu

1 Biliyaminu yana da ‘ya’ya biyar, su ne Bela, da Ashbel, da Ahiram,

2 da Noha, da Rafa.

3 Bela kuma yana da ‘ya’ya maza, su ne Adar, da Gera da Abihud,

4 da Abishuwa, da Na’aman, da Ahowa,

5 da Gera, da Shuffim, da Huram.

6 Waɗannan kuma su ne ‘ya’yan Ehud, maza. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Geba, waɗanda aka kai su bauta a Manahat.

7 Ga sunayensu, Na’aman, da Ahaija, da Gera wanda yake shugabansu lokacin da aka kai su bauta. Shi ne kuma mahaifin Uzza da Ahihud.

8 Shaharayim kuma yana da ‘ya’ya maza a ƙasar Mowab bayan da ya saki matansa biyu, wato Hushim da Ba’ara.

9 Matarsa Hodesh ta haifa masa ‘ya’ya maza, su ne Yobab, da Zibiya, da Mesha, da Malkam,

10 da Yuz, da Sakiya, da Mirma. Waɗannan su ne ‘ya’yansa maza, shugabannin gidajen kakanninsu.

11 Hushim kuma ta haifa masa waɗansu ‘ya’ya maza, su ne Abitub da Elfayal.

12 ‘Ya’yan Elfayal, su ne Eber, da Misham, da Shemed wanda ya gina Ono da Lod da ƙauyukansu, da

13 Beriya, da Shimai, su ne shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Ayalon waɗanda suka kori mazaunan Gat,

14 da Ahiyo, da Shashak, da Yeremot.

15 Zabadiya, da Arad, da Eder,

16 da Maikel, da Ishfa, da Yoha, su ne ‘ya’yan Beriya, maza.

17 Zabadiya, da Meshullam, da Hizki, da Eber,

18 da Ishmerai, da Izliya, da Yobab, su ne zuriyar Elfayal.

19 Zuriyar Shimai, su ne Yakim, da Zikri, da Zabdi,

20 da Eliyenai, da Zilletai, da Eliyel,

21 da Adaya, da Beraiya, da Shimrat.

22 Zuriyar Shashak, su ne Isfan, da Eber, da Eliyel,

23 da Abdon, da Zikri, da Hanan,

24 da Hananiya, da Elam, da Antotiya,

25 da Ifediya, da Feniyel.

26 Zuriyar Yeroham, su ne Shemsherai, da Shehariya, da Ataliya,

27 da Yawareshiya, da Eliya, da Zikri.

28 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakanninsu a zamaninsu, waɗanda suka zauna a Urushalima.

Zuriyar Saul

29 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a can. Sunan matarsa Ma’aka.

30 Abdon ne ɗansa na fari, sa’an nan Zur, da Kish, da Ba’al, da Nadab,

31 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya,

32 da Miklot, mahaifin Shimeya. Waɗannan su ne suka zauna daura da ‘yan’uwansu a Urushalima.

33 Ner shi ne mahaifin Kish, Kish kuma shi ne mahaifin Saul, Saul shi ne mahaifin Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet.

34 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika.

35 ‘Ya’yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz.

36 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza.

37 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel.

38 Azel ya haifi ‘ya’ya maza su shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Ismayel, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.

39 ‘Ya’ya maza na Esheke ɗan’uwansa su ne, Ulam, da Yewush, da Elifelet.

40 ‘Ya’yan Ulam, maza, jarumawa ne sosai, ‘yan baka, suna da ‘ya’ya maza, da jikoki maza da yawa. Su ɗari da hamsin ne. Waɗannan duka mutanen Biliyaminu ne.

Categories
1 TAR

1 TAR 9

Waɗanda Suka Komo daga Babila

1 Haka kuwa aka lasafta Isra’ilawa bisa ga asalinsu. An rubuta su a littafin sarakunan Isra’ila.

Sai aka kai mutanen Yahuza zaman talala a Babila saboda rashin amincinsu ga Ubangiji.

2 Waɗanda suka fara zama a biranen mallakarsu, su ne Isra’ilawa da firistoci, da Lawiyawa, da kuma ma’aikatan Haikali.

3 Waɗansu mutanen Yahuza, da na Biliyaminu, da na Ifraimu, da na Manassa suka zauna a Urushalima.

4-6 Iyalin Yahuza guda ɗari shida da tasa’in suka zauna a Urushalima, shugabansu kuwa shi ne Utai ɗan Ammihud, jīkan Omri daga wajen Feresa. Waɗansu kakanninsu kuwa su ne Imri da Bani. Zuriyar Shela ɗan Yahuza suna da shugaba mai suna Asaya. Zuriyar Zera ɗan Yahuza kuwa, shugabansu Yuwel.

7 Ga zuriyar Biliyaminu a Urushalima bi da bi, da Sallai ɗan Meshullam, da Hodawiya, da Hassenuwa,

8 da kuma Ibneya ɗan Yeroham, da Ila ɗan Uzzi, wato jīkan Mikri, da Meshullam ɗan Shefatiya, da Reyuwel, da Ibnija.

9 Tare da danginsu a zamaninsu, sun kai ɗari tara da hamsin da shida ne. Duk waɗannan shugabannin gidajen kakanninsu ne.

Firistocin da Suke a Urushalima

10 Daga cikin firistoci masu zama a Urushalima su ne Yedaiya, da Yehoyarib, da Yakin,

11 da Azariya ɗan Hilkiya, shi ne jami’in Haikalin Ubangiji, kakanninsa sun haɗu da Shallum ɗan Zadok, da Merayot, da Ahitub,

12 da Adaya ɗan Yeroham, kakanninsa sun haɗu da Fashur, da Malkiya, da Ma’asai ɗan Adiyel, kakanninsa sun haɗu da Yazera, da Meshullam, da Meshillemot, da Immer.

13 Firistacin da suke shugabannin gidajen kakanninsu, sun kai mutum dubu da ɗari bakwai da sittin (1,760). Ƙwararru ne cikin hidimar Haikalin Ubangiji.

14 Lawiyawa masu zama a Urushalima kuma, su ne Shemaiya ɗan Hasshub, wanda kakanninsa suka haɗu da Azrikam da Hashabiya daga ‘ya’yan Merari, maza,

15 da kuma Bakbakkar, da Heresh, da Galal, da Mattaniya ɗan Mika wanda kakanninsa su ne Zikri da Asaf,

16 da kuma Obadiya ɗan Shemaiya, kakanninsa su ne Galal da Yedutun, da Berikiya ɗan Asa, wato jīkan Elkana, wanda ya zauna a garin Netofa.

17 Masu tsaron Haikalin, su ne Shallum, da Akkub, da Talmon, da Ahiman, da ‘yan’uwansu. Shallum shi ne shugaba.

18 Har zuwa yau, iyalinsu suke tsaron ƙofar sarki a wajen gabas. A dā su ne suke tsaron sauran ƙofofin zangon Lawiyawa.

19 Shallum ɗan Kore, wato jīkan Ebiyasaf, tare da ‘yan’uwansa na zuriyar Kora, suke lura da masu tsaron ƙofofin alfarwa kamar dai yadda kakanninsu suka lura da zangon Ubangiji.

20 A dā Finehas ɗan Ele’azara shi ne shugabansu, Ubangiji kuwa yana tare da shi.

21 Zakariya ɗan Shallum yake tsaron ƙofar alfarwa ta sujada.

22 Dukan waɗanda aka zaɓa domin su zama masu tsaron ƙofofi, su ɗari biyu ne da goma sha biyu. An lasafta su bisa ga asalinsu da garuruwansu. Dawuda da Sama’ila annabi, su ne suka sa su a matsayinsu na riƙon amana.

23 Saboda haka su da ‘ya’yansu maza suke tsaron ƙofofin Ubangiji, wato alfarwa ta sujada.

24 Matsaran ƙofofi suka tsaya a kusurwoyi huɗu, wato gabas da yamma, kudu da arewa.

25 ‘Yan’uwansu waɗanda suke a ƙauyuka kuwa, ya zamar musu wajibi su zo wurinsu kowane kwana bakwai, domin su karɓe su tsaron.

26 Su shugabanni huɗu na matsaran ƙofar Lawiyawa ne waɗanda suke da matsayi na riƙon amana, su ne masu lura da ɗakunan Haikalin Allah da dukiyarsa.

27 Sukan kwana suna tsaro kewaye da Haikalin Allah, gama hakkin yana kansu. Su ne sukan buɗe shi kowace safiya.

28 Waɗansunsu suna lura da kayayyakin aiki na cikin Haikali. Sukan ƙidaya su sa’ad da aka shigo da su, da sa’ad da aka fitar da su.

29 Aka sa waɗansu su zama masu lura da kayayyakin Haikalin, da kayayyakin aiki na cikin Wuri Mai Tsarki, da lallausan gari, da ruwan inabi, da mai, da turare, da kayan yaji.

30 Waɗansu ‘ya’yan firistoci, maza, suke harhaɗa kayan yaji.

31 Mattitiya, ɗaya daga cikin Lawiyawa, ɗan farin Shallum na iyalin Kora, shi ne mai lura da toya waina.

32 Waɗansu ‘yan’uwansu Kohatawa suke lura da gurasar ajiyewa. Sukan shirya ta kowace Asabar.

33 Waɗannan su ne mawaƙa, da shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa, waɗanda suka zauna a ɗakunan Haikali, ba su yin wani aiki dabam, gama dare da rana suke yin aikinsu.

34 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa a zamaninsu, wato waɗanda suka zauna a Urushalima.

Kakannin Sarki Saul da Zuriyarsa

35 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a ciki, sunan matarsa Ma’aka,

36 ɗan farinsa kuma shi ne Abdon. Sa’an nan ga Zur, da Kish, da Ba’al, da Ner, da Nadab,

37 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya, da Miklot,

38 mahaifin Shimeya. Zuriyarsu ne suka zauna a Urushalima daura da ‘yan’uwansu.

39 Ner ya haifi Kish, Kish kuma ya haifi Saul, Saul ya haifi Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet.

40 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika.

41 ‘Ya’yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz.

42 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza,

43 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel.

44 Azel yana da ‘ya’ya maza guda shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Isma’ilu, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.

Categories
1 TAR

1 TAR 10

Mutuwar Sarki Saul da ta ‘Ya’yansa

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa.

2 Filistiyawa suka kama Saul da ‘ya’yansa maza, suka kashe Jonatan da Yishwi, da Malkishuwa.

3 Yaƙin ya tsananta wa Saul, maharba suka rutsa Saul, suka yi masa rauni.

4 Sai Saul ya ce wa mai ɗaukar makamansa, “Zare takobinka, ka kashe ni, don kada marasa kaciyan nan su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar makamai nasa bai yarda ba, gama yana jin tsoro ƙwarai. Saboda haka sai Saul ya zare takobinsa ya fāɗi a kansa.

5 Sa’ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya faɗi a kan takobinsa ya mutu.

6 Ta haka Saul ya mutu, shi da ‘ya’yansa maza guda uku tare da dukan gidansa.

7 Sa’ad da dukan Isra’ilawa waɗanda suke zaune a kwari suka ga sojojin sun gudu, Saul kuma da ‘ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa suka zo suka zauna a wurin.

8 Kashegari, sa’ad da Filistiyawa suka tafi su kwashe waɗanda aka kashe, sai suka tarar da Saul da ‘ya’yansa maza matattu a Dutsen Gilbowa.

9 Suka kuwa tuɓe tufafinsa, suka datse kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka aiki manzanni ko’ina a ƙasar Filistiyawa don su ba gumakansu da jama’arsu wannan albishir.

10 Sai suka ajiye kayan yaƙin Saul a gidan gumakansu, suka kuma rataye kansa a gidan gunkin nan, wato Dagon.

11 Sa’ad da mutanen Yabesh-gileyad suka ji irin abin da Filistiyawa suka yi wa Saul,

12 sai dukan ƙarfafan mutanensu suka tafi suka ɗauki gawar Saul, da gawawwakin ‘ya’yansa, suka kawo a Yabesh suka binne ƙasusuwansu a ƙarƙashin itacen oak cikin Yabesh. Suka yi azumi har kwana bakwai.

13 Haka nan Saul ya mutu saboda laifin da ya yi wa Ubangiji, gama bai kiyaye maganar Ubangiji ba, saboda kuma ya nemi shawara wurin masu mabiya.

14 Amma bai nemi Ubangiji ba. Domin haka Ubangiji ya kashe shi, ya ɗauki sarautar, ya ba Dawuda ɗan Yesse.

Categories
1 TAR

1 TAR 11

Dawuda Ya Zama Sarkin Isra’ila da Yahuza

1 Dukan Isra’ilawa kuwa suka taru wurin Dawuda a Hebron, suka ce masa, “Mu ɗaya ne da kai.

2 Ko dā can lokacin da Saul yake sarauta, kai ne kake yi wa Isra’ilawa jagora zuwa yaƙi da komowa. Ubangiji Allahnka kuwa ya ce maka, ‘Za ka yi kiwon jama’ata, wato Isra’ilawa, ka kuma shugabance su.’ ”

3 Sai dattawan Isra’ilawa suka zo wurin sarki Dawuda a Hebron. Dawuda kuwa ya yi alkawari da su a Hebron a gaban Ubangiji, ake kuwa naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra’ila bisa ga faɗar Ubangiji ta bakin Sama’ila.

Dawuda Ya Ci Sihiyona

4 Sarki Dawuda kuwa, tare da dukan Isra’ilawa, suka tafi Urushalima, wato Yebus inda Yebusiyawa suke zaune.

5 Sai mazaunan Yebus, suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka Dawuda ya ci Sihiyona, gari mai kagara, wato birnin Dawuda ke nan.

6 Sai Dawuda ya ce, “Duk wanda ya ci Yebusiyawa da fari shi ne zai zama babban shugaban sojoji.” Yowab ɗan Zeruya ne ya fara tafiya, domin wannan aka maishe shi shugaba.

7 Sa’an nan Dawuda ya zauna a kagara, don haka aka kira birnin, birnin Dawuda.

8 Sai ya rutsa birnin da gini tun daga Millo. Yowab kuma ya gyaggyara sauran birnin.

9 Dawuda ya yi ta ƙasaita gaba gaba saboda Ubangiji Mai Runduna yana tare da shi.

Jarumawan Dawuda

10 Waɗannan su ne shugabanni, wato manyan jarumawan Dawuda waɗanda suka goyi bayansa sosai a mulkinsa, tare da dukan Isra’ilawa waɗanda suka naɗa shi sarki bisa ga maganar Ubangiji a kan Isra’ilawa.

11 Wannan shi ne labarin manyan jarumawan Dawuda. Yashobeyam ɗan Bahakmone shi ne shugaban jarumawa talatin. Ya karkashe mutum ɗari uku da māshinsa baki ɗaya.

12 Na biye da shi shi ne Ele’azara ɗan Dodo, Ba’ahohiye, wanda yake ɗaya daga cikin manyan jarumawan nan uku.

13 Yana tare da Dawuda a Efes-dammin sa’ad da Filistiyawa suka taru wuri ɗaya don su yi yaƙi. Akwai wata gonar sha’ir a wurin, sai jama’a suka gudu daga gaban Filistiyawa.

14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya cece su, ya ba su babbar nasara.

15 Wata rana sai uku daga cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara zuwa dutsen Dawuda, a kogon Adullam, sa’ad da rundunar sojojin Filistiyawa suka kafa sansani a kwarin Refayawa.

16 Dawuda yana cikin kagara, sojojin Filistiyawa kuwa suna a Baitalami.

17 Sai Dawuda ya yi marmarin gida, ya ce, “Dā ma wani ya kawo mini ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami in sha!”

18 Sai uku ɗin suka kutsa kai, suka shiga sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami, suka ɗauka, suka kawo wa Dawuda, Dawuda kuwa bai sha ba, amma ya kwarara ruwan a ƙasa domin sadaka ga Ubangiji.

19 Sa’an nan ya ce, “Allah ya sawwaƙe mini da zan yi wannan abu a gabansa, da zan sha jinin waɗannan da suka sadaukar da rayukansu, gama sai da suka yi kasai da ransu, sa’an nan suka ɗebo ruwan.” Saboda haka bai sha ruwan ba. Manyan jarumawan nan uku ne suka aikata waɗannan abubuwa.

20 Abishai ɗan’uwan Yowab kuwa shi ne shugaban jarumawa talatin ɗin. Ya girgiza mashinsa, ya kashe mutum ɗari uku. Ya yi suna a cikin jarumawan nan talatin.

21 Cikin jarumawa talatin ɗin, shi ya shahara har ya zama shugabansu. Amma duk da haka bai kai ga jarumawan nan uku ba.

22 Benaiya ɗan Yehoyada, ɗan wani jarumi ne daga Kabzeyel, ya yi manyan ayyuka, ya kashe jarumawa biyu na Mowabawa. Sai ya gangara ya kashe zaki a cikin rami a ranar da ake yin dusar ƙanƙara.

23 Sai kuma ya kashe wani dogon Bamasare mai tsayi kamu biyar. Bamasaren yana da māshi mai kama da dirkar masaƙa a hannunsa, amma sai ya gangaro wurinsa da kulki a hannu, ya ƙwace māshin daga hannun Bamasaren, ya kashe shi da shi.

24 Waɗannan abubuwa Benaiya ɗan Yehoyada ya yi su, ya kuwa yi suna kamar manyan jarumawan nan uku.

25 Ya yi suna a cikin jarumawa talatin ɗin, amma bai kai ga jarumawan nan uku ba. Sai Dawuda ya sa shi ya zama shugaban matsaransa.

26-47 Waɗannan su ne manyan jarumawan sojoji.

Asahel ɗan’uwan Yowab

Elhanan ɗan Dodo daga Baitalami

Shamma daga Harod

Helez daga Felet

Aira ɗan Ikkesha daga Tekowa

Abiyezer daga Anatot

Sibbekai daga Husha

Ilai daga Aho

Maharai daga Netofa

Heled ɗan Ba’ana daga Netofa

Ittayi ɗan Ribai daga Gibeya ta Biliyaminu

Benaiya na Firaton

Hurai daga rafuffuka kusa da Ga’ash

Abiyel daga Araba

Azmawet daga Bahurim

Eliyaba daga Shalim

‘Ya’yan Yashen, maza, daga Gizon

Jonatan ɗan Shimeya daga Harod

Ahiyam ɗan Sharar daga Harod

Elifelet ɗan Ahasbai

Hefer daga Mekara

Ahaija daga Felet

Hezro daga Karmel

Nayarai ɗan Ezbai

Yowel ɗan’uwan Natan

Mibhar ɗan Hagri

Zelek daga Ammon

Naharai daga Biyerot (Mai riƙe wa Yowab ɗan Zeruya makamai)

Aira da Gareb daga Yattir

Uriya Bahitte

Zabad ɗan Alai

Adina ɗan Shiza (Shi ne shugaba a kabilar Ra’ubainu, yana da ƙungiyarsa mai soja talatin tare da shi)

Hanan ɗan Ma’aka

Yoshafat daga Mitna

Uzziya daga Ashtera

Shama da Yehiyel ‘ya’yan Hotam, maza, daga Arower

Yediyel da Yoha ‘ya’yan Shimri, maza, daga Tiz

Eliyel daga Mahawa

Yeribai, da Yoshawiya ‘ya’yan Elna’am, maza

Itma daga Mowab

Eliyel, da Obida, da Yawasiyel daga Zoba,

Categories
1 TAR

1 TAR 12

Mataimakan Dawuda a Ziklag

1 Mutane da yawa suka haɗa kai da Dawuda lokacin da yake a Ziklag, sa’ad da yake a takure saboda Saul ɗan Kish. Su ma suna cikin manyan jarumawan da suka taimake shi yaƙi. Dukansu gwanayen sojoji ne, suna iya su harba kibiya, ko su yi jifa da majajjawa da hannun dama ko da na hagu.

2 Su daga kabilar Biliyaminu ne, dangin Saul.

3-7 Waɗannan su ne shugabannin sojoji,

Ahiyezer, da Yowash, ‘ya’yan Shemaiya, maza, daga Gibeya

Yeziyel, da Felet, ‘ya’yan Azmawet, maza

Beraka, da Yehu daga Anatot

Ismaya daga Gibeyon babban jarumi

ne a cikin jarumawan nan talatin,

yana daga cikin shugabannin

jarumawa talatin ɗin

Irmiya, da Yahaziyel

Yohenan, da Yozabad daga Gedera

Eluzai, da Yerimot, da Be’aliya

Shemariya, da Shefatiya daga Harif

Elkana, da Isshiya, da Azarel

Yowezer, da Yashobeyam daga iyalin

Kora

Yowela, da Zabadiya ‘ya’ya maza na

Yeroham na Gedor

8 Waɗannan su ne sunayen shahararru, ƙwararrun mayaƙa daga kabilar Gad, waɗanda suka haɗa kai da sojojin Dawuda, sa’ad da yake a kagara a hamada. Su gwanayen yaƙi da garkuwa da mashi ne. Fuskokinsu kamar na zakoki, saurinsu kamar bareyi a kan dutse.

9-13 Ga yadda aka lasafta su bisa ga matsayinsu, da Ezer, da Obadiya, da Eliyab, da Mishmanna, da Irmiya, da Attai, da Eliyel, da Yohenan, da Elzabad, da Irmiya, da Makbannai.

14 Waɗannan daga kabilar Gad shugabannin sojoji ne, waɗansu na mutum dubu, sauransu kuma ƙananan shugabanni ne waɗanda suke shugabancin sojoji ɗari.

15 Su ne waɗanda suka haye Urdun a watan fari na shekara, sa’ad da Kogin Urdun ɗin ya yi ambaliya. Suka kori waɗanda suke zaune a kwaruruka, na wajen gabas da yamma da kogin.

16 Sa’an nan waɗansu daga cikin mazajen Biliyaminu da na Yahuza, suka zo wurin Dawuda a kagararsa.

17 Sai Dawuda ya fito don ya tarye su, ya ce musu, “Idan da salama kuka zo wurina don ku taimake ni, to, zuciyata za ta zama ɗaya da taku, amma idan kun zo ne don ku bashe ni ga maƙiyana, to, Allah na kakanninmu ya duba ya shara’anta, da yake ba ni da laifi.”

18 Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Amasa wanda daga baya ya zama shugaban talatin ɗin, sai ya ce,

“Muna tare da kai, ya Dawuda ɗan Yesse!

Allah ya ba ka nasara tare da waɗanda suke tare da kai!

Allah yana wajenka!”

Sa’an nan Dawuda ya marabce su, ya maishe su shugabanni a sojojinsa.

19 Waɗansu sojoji daga Manassa, suka tafi wurin Dawuda sa’ad da yake fita tare da Filistiyawa don su yi yaƙi da Saul. Amma Dawuda bai tafi tare da su ba, domin sarakunan Filistiyawa sun yi shawara, suka sallame shi, don kada ya juya musu gindin baka, ya nemi sulhu a wurin shugabansu Saul, da kawunansu.

20 Sa’ad da yake komawa Ziklag sai sojojin Manassa suka zo wurinsa, wato su Adana, da Yozabad, da Yediyayel, da Maikel, da Yozabad, da Elihu, da Zilletai. A sojojin kabilar Manassa, waɗannan shugabannin sojoji ne na dubu dubu.

21 Suka kuwa taimaki Dawuda sa’ad da mahara take tasar masa, gama dukansu jarumawa ne sosai, su kuma shugabannin sojoji ne.

22 Kowace rana mutane suna ta zuwa wurin Dawuda don su taimake shi, har suka zama babbar runduna.

Jerin Sojojin Dawuda a Hebron

23 Horarrun sojoji da yawa suka haɗa kai da sojojin Dawuda a Hebron domin su taimaki Dawuda da yaƙi, su mai da shi sarki maimakon Saul, kamar yadda Ubangiji ya alkawarta. Ga yadda yawansu yake.

24 Mutanen Yahuza waɗanda suke riƙe da garkuwoyi da māsu don yaƙi, mutum dubu shida da ɗari takwas (6,800).

25 Na kabilar Saminu jarumawa mayaƙa mutum dubu bakwai da ɗari (7,100).

26 Na kabilar Lawi akwai mutum dubu huɗu da ɗari shida (4,600).

27 Akwai kuma Yehoyada wanda shi ne shugaban gidan Haruna, yana da mutum dubu uku da ɗari bakwai (3,700).

28 Na dangin Zadok wanda yake jarumi, saurayi, akwai shugabannin sojoji ashirin da biyu.

29 Na kabilar Biliyaminu, wato kabilar Saul, akwai mutum dubu uku (3,000). (Har yanzu yawancin mutanen Biliyaminu ba su daina bin gidan Saul ba.)

30 Na kabilar Ifraimu akwai mutum dubu ashirin da ɗari takwas (20,800), jarumawa ne sosai, waɗanda suka shahara a danginsu.

31 Na rabin kabilar Manassa wajen yamma akwai mutum dubu goma sha takwas (18,000) waɗanda aka zaɓa domin su zo su naɗa Dawuda ya zama sarki.

32 Na kabilar Issaka akwai shugabanni ɗari biyu, waɗanda suka gane da halin da ake ciki, da abin da ya kamata Isra’ila ya yi. Su ne suke shugabancin ‘yan’uwansu.

33 Na kabilar Zabaluna akwai mutum dubu hamsin (50,000) suna da kowane irin kayan yaƙi. Suka zo domin su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya.

34 Na kabilar Naftali akwai shugabannin sojoji dubu ɗaya (1,000) tare da sojoji dubu talatin da dubu bakwai (37,000) masu garkuwoyi da māsu.

35 Na kabilar Dan mutum dubu ashirin da takwas da ɗari shida (28,600).

36 Na kabilar Ashiru, sojoji dubu arba’in (40,000) suka fito da shirin yaƙi.

37 Kabilan gabashin Urdun, wato kabilar Ra’ubainu, da Gad, da rabin kabilar Manassa, su dubu ɗari da dubu ashirin ne (120,000), suna da kowane irin kayan yaƙi.

38 Duk waɗannan mayaƙa sun zo Hebron a shirye, da zuciya ɗaya don su naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra’ila duka. Haka kuma dukan sauran Isra’ilawa suka goyi baya da zuciya ɗaya a naɗa Dawuda ya zama sarki.

39 Suka yi kwana uku tare da Dawuda, suka yi ta ci suna sha, gama ‘yan garin sun shirya wata liyafa dominsu.

40 Waɗanda kuma suke kusa da su har zuwa Issaka, da Zabaluna da Naftali, sun kawo abinci a kan jakuna, da raƙuma, da alfadarai, da takarkarai. Suka kawo abinci mai yawa, wato gāri da kauɗar ɓaure da nonnan busassun ‘ya’yan inabi, da ruwan inabi, da man zaitun. Suka kuma kawo shanu da tumaki domin yanka a ci. Duk an yi wannan domin a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.