Categories
2 TAR

2 TAR 4

1 Ya yi bagade na tagulla, tsawonsa kamu ashirin ne, fāɗinsa kuma kamu ashirin, tsayinsa kuwa kamu goma.

2 Ya yi kwatarniya kewayayyiya ta zubi, kamu goma daga gāɓa zuwa gāɓa, tsayinsa kuwa kamu biyar ne, da’irarsa kuwa kamu talatin.

3 A ƙashiyar kwatarniya akwai siffofin bijimai kamu goma kewaye da ita har jeji biyu. Gaba ɗaya aka yi zubinsu da na kwatarniya.

4 Kwatarniya tana bisa bijimai goma sha biyu, uku suna fuskantar gabas, uku suna fuskantar yamma, uku suna fuskantar kudu, uku kuma suna fuskantar arewa. Kwatarniya tana bisa bijiman, gindin kowannensu yana daga ciki.

5 Kaurin kwatarniya taƙi guda ne, bakinsa kamar bakin finjali ne, kamar kuma siffar furen bi-rana. Kwatarniya kuwa tana iya ɗaukar fiye da garwa dubu uku na ruwa.

6 Ya kuma yi daro goma na wanki, ya ajiye biyar a wajen kudu, biyar kuma a wajen arewa, don a riƙa ɗauraye abubuwan da ake hadayar ƙonawa da su. Amma kwatarniya don firistoci su riƙa wanka a ciki ne.

7 Sa’an nan ya yi alkuki goma na zinariya kamar yadda aka tsara. Ya sa su cikin Haikali, biyar a sashen dama, biyar kuma a hagu.

8 Ya kuma yi tebur goma, ya ajiye a cikin Haikalin, biyar a dama, biyar kuma a hagu. Ya kuma yi kwanonin zinariya guda ɗari.

9 Sa’an nan ya yi wani shirayi domin firistoci, ya kuma yi wani babban shirayi, ya yi ƙofofi domin shirayun. Ya dalaye ƙyamaren ƙofofin da tagulla.

10 Ya girka kwatarniya a kusurwar kudu maso gabas daura da Haikalin.

11-16 Huram kuma ya yi tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da daruna. Huram kuwa ya gama dukan aikin da ya alkawarta wa sarki Sulemanu a Haikalin Allah:

ginshiƙi biyu

dajiya biyu a kan ginshiƙi biyu

siffar tukakkiyar sarƙa a kan kowane ginshiƙi

Siffar rumman guda ɗari huɗu domin raga don rufe dajiyar ginshiƙan

dakali goma

daro goma

kwatarniya

bijimi goma sha biyu da suke ɗauke da kwatarniya

kwanoni, manyan cokula masu yatsotsi, wato ya yi dukan kayan nan da tagulla domin haikalin Ubangiji

17 Sarki ya yi zubinsu a filin Urdun tsakanin Sukkot da Zaretan a wuri mai yumɓu.

18 Haka Sulemanu ya yi kayayyakin nan da yawa ƙwarai, har ba a iya lissafin yawan nauyin tagullar da aka yi amfani da ita ba.

19-22 Haka kuwa Sulemanu ya yi dukan kayayyakin nan da suke cikin Haikalin Allah, duk da zinariya tsantsa aka yi su.

bagade na zinariya

tebur don ajiye gurasar ajiyewa

alkukai tare da fitilunsu na zinariya tsantsa, domin a kunna su a gaban Wuri Mafi Tsarki na ciki kamar yadda aka tsara

furanni

fitilu

arautaki

hantsuka

daruna

cokula

farantan wuta

ƙofofi na can ciki

ƙofofi na waje

Categories
2 TAR

2 TAR 5

1 Sulemanu ya kammala dukan aikin Haikalin Ubangiji. Sa’an nan ya kawo kayayyakin da tsohonsa Dawuda ya riga ya keɓe, wato azurfa da zinariya, da dukan kayan girke-girke, da tasoshi, ya ajiye su a taskokin Haikalin Allah.

Sulemanu Ya Kawo Akwatin Alkawari a Haikali

2 Sulemanu kuwa ya tattara dattawan Isra’ila, da shugabannin kabilai, da shugabannin gidajen kakannin jama’ar Isra’ila, a Urushalima, domin a yi bikin fito da akwatin alkawari na Ubangiji da yake a alfarwa a birnin Dawuda, wato Sihiyona.

3 Sai dukan mutanen Isra’ila suka hallara a gaban sarki, a wurin bikin, a wata na bakwai ke nan.

4 Sa’an nan dukan dattawan Isra’ila suka zo, Lawiyawa kuwa suka ɗauko akwatin.

5 Suka kuma kawo akwatin, da alfarwa ta taruwa, da dukan tsarkakakkun kayayyakin da suke cikin alfarwar. Lawiyawa da firistoci ne suka kawo su.

6 Sarki Sulemanu da dukan taron mutanen Isra’ila waɗanda suka hallara a gaban akwatin suka yi ta miƙa hadayun tumaki da bijimai masu yawan gaske, har ba su ƙidayuwa.

7 Sa’an nan firistoci suka shigar da akwatin alkawari na Ubangiji a wurinsa, wato a Wuri Mafi Tsarki na cikin Haikalin, a ƙarƙashin fikafikan kerubobi.

8 Gama kerubobin sun miƙe fikafikansu bisa a daidai wurin da akwatin yake, wato kerubobin sun yi wa akwatin da sandunansa kamar rumfa ke nan.

9 Sandunan akwatin dogaye ne ƙwarai, har ana ganin kawunansu a gaban Wuri Mafi Tsarki na can ciki. Amma daga waje ba a iya ganinsu. Suna a wannan wuri har yau.

10 Ba kome cikin akwatin sai alluna biyu waɗanda Musa ya sa a ciki sa’ad da suke a Horeb. A Horeb ne Ubangiji ya ƙulla alkawarin da mutanen Isra’ila, sa’ad da suka fito daga Masar.

Ɗaukakar Ubangiji

11 Firistocin suka fito daga Wuri Mai Tsarki na Haikalin Allah, gama dukan firistocin da suka hallara, sun tsarkake kansu ba tare da kula da bambancin matsayi ba.

12 Dukan Lawiyawa mawaƙa, wato su Asaf, da Heman, da Yedutun tare da ‘ya’yansu maza da ‘yan’uwansu, aka sa su su tsaya a gabashin bagade, suna sāye da lilin mai kyau, suna ta kaɗa kuge, da molaye da garayu, ga kuma firistoci ɗari da ashirin masu busa ƙaho tare da su.

13 Ya zama aikin mabusan ƙaho ne, da mawaƙa duka, su haɗa kai, har a ji su suna yabon Ubangiji, suna godiya, sa’ad da suka ɗaga waƙa daidai da muryar ƙaho da ta kuge, da dukan kayan bushe-bushe suka yi ta raira waƙa cewa,

“Yabo ya tabbata ga Ubangiji

Gama shi nagari ne,

Ƙaunarsa kuwa madawwamiya ce.”

Gidan kuwa, wato Haikalin Ubangiji, ya cika da girgije,

14 har ma firistoci ba su iya tsayawa su ci gaba da hidima ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika Haikalin Allah.

Categories
2 TAR

2 TAR 6

Maganar Sulemanu ga Mutane

1 Sulemanu ya ce,

“Ubangiji ya riga ya faɗa zai zauna a cikin girgije mai duhu.

2 Yanzu kuwa na gina maka ƙasaitaccen ɗaki,

Na gina maka wurin da za ka zauna har abada.”

3 Sa’an nan sarki ya juya, ya dudduba, ya sa wa dukan taron jama’ar Isra’ila albarka, dukansu kuwa suka tsaya.

4 Sai ya ce, “Ubangiji Maɗaukaki ne, Allah na Isra’ila wanda ya yi wa tsohona Dawuda alkawari, ga shi kuwa ya cika shi, gama ya ce,

5 ‘Tun daga ranar da na fito da jama’ata daga ƙasar Masar, ban zaɓi wani birni daga cikin dukan kabilan Isra’ila ba, inda zan gina wurin da sunana zai kasance, ban kuma zaɓi wani mutum da zai shugabanci jama’ata Isra’ila ba.

6 Amma na zaɓi Urushalima domin sunana ya kasance a wurin, na kuma zaɓi Dawuda ya zama shugaban jama’ata Isra’ila.’

7 “Ya zama kuwa tsohona Dawuda ya yi niyyar gina Haikali domin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.

8 Amma Ubangiji ya ce wa ubana Dawuda, ya kyauta, tun da yake ya yi niyya a zuciyarsa zai gina ɗaki saboda sunansa.

9 Duk da haka, ba shi zai gina Haikalin ba, ɗansa wanda za a haifa masa, shi ne zai gina Haikalin domin sunansa.

10 “Yanzu fa Ubangiji ya cika alkawarin da ya yi, gama na gāji matsayin ubana Dawuda, na kuwa hau gadon sarautar Isra’ila, yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuwa gina Haikali domin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.

11 A can na ajiye akwati inda aka sa alkawarin da Ubangiji ya yi wa jama’ar Isra’ila.”

Addu’ar Sulemanu

12 Sulemanu ya miƙe a gaban bagaden Ubangiji a idon dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa.

13 Sulemanu ya riga ya yi dakali na tagulla, tsawonsa kamu biyar, fāɗinsa kamu biyar, tsayinsa kamu uku, ya ajiye shi a tsakiyar filin, ya tsaya a kai. Ya durƙusa a gwiwoyinsa, a idon dukan taron jama’ar Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,

14 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ba wani Allah kamarka a sama ko a duniya, wanda yake cika alkawari, kana nuna madawwamiyar ƙauna ga bayinka masu tafiya a gabanka da zuciya ɗaya.

15 Kai ka cika alkawarin da ka yi wa bawanka, tsohona Dawuda. Abin da ka faɗa ka kuma aikata.

16 Yanzu fa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka cika alkawarin da ka yi wa bawanka tsohona cewa, ‘Daɗai, ba za a rasa wanda zai hau gadon sarautar Isra’ila ba, in dai ‘ya’yanka maza za su lura da al’amuransu, don su yi tafiya bisa ga shari’ata, yadda kai ka yi tafiya a gabana.’

17 Saboda haka, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka tabbatar da maganarka wadda ka yi wa bawanka Dawuda.

18 “Ashe kuwa Allah zai zauna tare da ɗan adam a duniya? Ga shi kuwa, sama da saman sammai ba su iya ɗaukarka ba, balle fa ɗakin da na gina.

19 Duk da haka ka kula da addu’ar bawanka da roƙe-roƙensa. Ya Ubangiji Allahna, ka kasa kunne ga kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.

20 Ka dubi wajen Haikalin nan dare da rana, wurin da ka yi alkawari za ka sa sunanka, ka kasa kunne ga addu’ar da bawanka zai yi wajen wannan wuri,

21 ka ji roƙe-roƙen bawanka da na jama’ar Isra’ila, sa’ad da suke addu’a suna fuskantar wannan wuri, ka ji daga wurin da kake zaune a Sama, sa’ad da ka ji, ka gafarta.

22 “Idan wani ya yi wa maƙwabcinsa laifi, har aka sa shi ya rantse, ya kuwa zo ya rantse a gaban bagaden a wannan Haikali,

23 sai ka ji ka yi wa bayinka shari’a daga Sama, ka hukunta wa mugun, ka ɗora masa alhakinsa, ka baratar da adalin, ka ba shi sakayyar adalcinsa.

24 “Idan abokan gāba sun kori jama’arka, wato Isra’ila, saboda laifin da suka yi maka, sa’an nan suka juyo suka shaida sunanka, suka yi addu’a, suka yi roƙo a gabanka a wannan Haikali,

25 sai ka ji daga Sama ka gafarta zunubin jama’arka Isra’ila, ka komo da su ƙasar da ka ba su, su da kakanninsu.

26 “Sa’ad da aka kulle sammai, ba ruwan sama saboda sun yi maka zunubi, sa’an nan suka fuskanci wurin nan suka yi addu’a, suka shaida sunanka, suka juyo suka daina zunubinsu a sa’ad da ka hukunta su,

27 sai ka ji daga Sama ka gafarta zunubin bayinka, wato jama’arka Isra’ila, lokacin da ka koya musu kyakkyawar hanya da za su bi. Sai ka sa a yi ruwa a ƙasarka, wadda ka ba jama’arka gādo.

28 “Idan ana yunwa a ƙasar, ko annoba, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fārā, ko gamzari, ko da maƙiyansu za su kewaye biranensu da yaƙi, ko kowace irin annoba, da kowace irin cuta da take akwai,

29 kowace irin addu’a, kowane irin roƙo da kowane mutum, ko jama’ar Isra’ila suka yi, ko wannensu yana sane da irin wahalarsa, da baƙin cikinsa, ya kuwa ɗaga hannunsa wajen wannan Haikali,

30 sa’an nan za ka ji daga wurin zamanka a Sama, ka yi gafara, ka kuwa sāka wa kowa bisa ga al’amuransa, wanda ka san zuciyarsa, gama kai kaɗai ne ka san zukatan mutane,

31 don su yi tsoronka su yi tafiya bisa ga dokokinka muddin ransu, a ƙasar da ka ba kakanninmu.

32 “Haka kuma baƙo wanda ba cikin jama’arka Isra’ila yake ba, idan ya taho daga wata ƙasa mai nisa saboda girman sunanka da ƙarfin ikonka, in ya zo ya yi sujada, yana fuskantar Haikalin nan,

33 ka ji daga Sama wurin zamanka, ka kuwa aikata bisa ga dukan irin roƙon da baƙon ya yi gare ka. Domin ta haka sauran al’umman duniya za su san sunanka, su kuma yi tsoronka, yadda jama’arka Isra’ila suke yi, za su kuma sani cewa wannan Haikali da na gina, ana kiransa da sunanka.

34 “Sa’ad da jama’arka za su fita don yin yaƙi da magabtansu, duk dai ko ta ina ne za ka aike su, in sun yi addu’a gare ka, suna fuskantar wannan birni wanda kai ka zaɓa, da Haikalin nan da na gina saboda sunanka,

35 sai ka ji addu’arsu da roƙe-roƙensu daga Sama, ka biya muradinsu.

36 “Sa’ad da suka yi maka zunubi (gama ba wani ɗan adam da ba ya yin zunubi), ka kuwa yi fushi da su, har ka bashe su a hannun magabtansu, magabtansu suka kakkama su suka kai wata ƙasa ta nesa ko ta kusa,

37 duk da haka idan sun yi niyya a ransu a can ƙasar da aka kai su baƙunta, suka tuba, suka roƙe ka a can ƙasar baƙunci tasu, suna cewa, ‘Mun yi zunubi, mun aikata laifi, mun kuma yi mugunta,’

38 in sun tuba da zuciya ɗaya, a ƙasar da aka kai su, in sun fuskanci ƙasarsu wadda ka ba kakanninsu, da birnin da ka zaɓa, suka yi addu’a, suna kuma fuskantar Haikalin nan da na gina domin sunanka,

39 sai ka ji addu’arsu da roƙe-roƙensu, daga wurin zamanka a Sama, ka sa su yi nasara, ka biya musu muradinsu, ka gafarta wa jama’arka waɗanda suka yi maka zunubi.

40 “Yanzu fa, ya Allahna, ina roƙonka, ka buɗe idanunka, ka kasa kunnuwanka, ka saurari addu’ar da ake yi a wannan wuri.

41 Yanzu fa, ya Ubangiji ka tashi ka tafi wurin hutawarka, kai da akwatin ikonka. Ya Ubangiji Allah ka yi wa firistocinka sutura da cetonka, adalanka kuma su yi farin ciki da nagartarka.

42 Ya Ubangiji Allah kada ka juya baya ga keɓaɓɓenka, ka tuna da madawwamiyar ƙaunarka ga bawanka Dawuda.”

Categories
2 TAR

2 TAR 7

Ƙeɓewar Haikali

1 Sa’ad da Sulemanu ya gama yin addu’arsa, sai wuta ta sauko daga sama, ta cinye hadayar ƙonawa tare da sauran hadayu, darajar Ubangiji kuma ta cika Haikalin.

2 Firistoci ba su iya shiga Haikalin Ubangiji ba saboda darajar Ubangiji ta cika Haikalin.

3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wuta ta sauko daga sama, ɗaukakar Ubangiji kuma na cike da Haikalin, sai suka sunkuyar da kansu ƙasa, suka yi sujada, suka yabi Ubangiji, saboda nagarinsa da madawwamiyar ƙaunarsa.

4 Sa’an nan sarki da dukan jama’a suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.

5 Sarki Sulemanu kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da dubu biyu (22,000), da tumaki dubu ɗari da dubu ashirin (120,000). Ta haka sarki tare da dukan jama’a suka keɓe Haikalin Allah.

6 Sai firistoci suka tsaya a matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a nasu matsayi riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji, gama madawwamiyar ƙaunarsa tabbatacciya ce har abada. A duk lokacin da Dawuda zai yabi Ubangiji tare da su, sai firistoci waɗanda suke daura da su su busa ƙaho, sa’an nan sai dukan Isra’ilawa su miƙe tsaye.

7 Sa’an nan Sulemanu ya tsarkake tsakiyar filin da yake a gaban Haikalin Ubangiji, gama a wurin ne ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayu domin salama, saboda bagaden tagulla wanda Sulemanu ya yi bai iya ɗaukar hadayu domin ƙonawa, da ta gari, da ta kitse ba.

8 A wannan lokaci, Sulemanu ya yi biki a wurin har kwana bakwai, tare da dukan Isra’ilawa, da waɗanda suka zo tun daga ƙofar Hamat, har zuwa rafin Masar, taron kuwa mai girma ne ƙwarai.

9 A rana ta takwas kuwa suka yi wani muhimmin taro, domin su keɓe bagaden. Sun yi kwana bakwai suna yin bikin.

10 A ran ashirin da uku ga watan bakwai, sai sarki ya sallami jama’a su koma gidajensu, suna ta murna da farin ciki a zuciyarsu saboda alherin da Ubangiji ya nuna wa Dawuda, da Sulemanu, da kuma jama’arsa Isra’ila.

Ubangiji Ya Sāke Bayyana ga Sulemanu

11 Haka kuwa Sulemanu ya gama Haikalin Ubangiji da fādar sarki. Ya fa yi nasara cikin dukan irin abin da ya yi niyya game da Haikalin Ubangiji da fādarsa.

12 Sa’an nan Ubangiji ya bayyana ga Sulemanu da dare, ya ce masa, “Na ji addu’arka, na kuwa zaɓi wannan wuri domin kaina, domin ya zama Haikalin miƙa hadaya.

13 Har idan na kulle sammai yadda ba za a yi ruwan sama ba, ko kuma in umarci fara su cinye ƙasar, ko kuwa in aiko da annoba cikin jama’ata,

14 in jama’ata waɗanda ake kiransu da sunana za su yi tawali’u, su yi addu’a, su nemi fuskata, su juyo su bar mugayen ayyukansu, sa’an nan sai in ji su daga Sama, in gafarta zunubansu, in kuma warkar da ƙasarsu.

15 Yanzu idanuna za su kasance a buɗe, kunnuwana kuma za su saurari addu’ar da za a yi a wannan wuri.

16 Yanzu fa na riga na zaɓi wannan Haikali, na kuwa keɓe shi domin sunana ya kasance a wurin har abada. Idanuna da zuciyata kuma za su kasance a wurin kullayaumin.

17 Amma kai, idan za ka yi zamanka a gabana kamar yadda tsohonka Dawuda ya yi, ka kuma aikata bisa ga dukan abin da na umarce ka, ka kiyaye dokokina da farillaina,

18 to, zan kafa gadon sarautarka, yadda na alkawarta wa tsohonka Dawuda, cewa ba za a rasa mutumin da zai yi mulkin Isra’ila ba.

19 Amma idan ka juya, ka bar dokokina da umarnaina waɗanda na sa a gabanka, har ka shiga bautar gumaka kana musu sujada,

20 to, sai in tumɓuke ka daga ƙasata wadda na ba ka, wannan Haikali kuma wanda na riga na keɓe domin sunana, zan kawar da shi daga fuskata, zan kuwa maishe shi abin karin magana, abin raini ga dukan sauran al’umma.

21 “Haikali kuwa, wanda aka ɗaukaka, duk mai wucewa zai yi mamaki ya ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi wa wannan ƙasa da wannan Haikali haka?’

22 “Sa’an nan kuma za su ce, ‘Saboda sun rabu da Ubangiji, Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga ƙasar Masar, amma suka bi waɗansu gumaka, suka yi musu sujada, suka bauta musu, saboda haka ne ya aukar musu da duk wannan bala’i.’ ”

Categories
2 TAR

2 TAR 8

Waɗansu Ayyukan Sulemanu

1 A ƙarshen shekara ashirin waɗanda Sulemanu ya yi yana gina Haikalin Ubangiji da fādarsa,

2 sa’an nan ya sāke giggina biranen da Hiram ya ba shi, ya zaunar da Isra’ilawa a cikinsu.

3 Sai Sulemanu ya tafi ya ci Hamat-zoba da yaƙi.

4 Sa’an nan ya gina Tadmor a jeji, a Hamat kuwa ya gina biranen ajiya.

5 Ya kuma gina Bet-horon ta kan tudu da Bet-horon ta kwari, birane masu kagara kuwa ya gina musu garu, da ƙofofi, da ƙyamare,

6 da kuma Ba’alat da dukan biranen ajiya waɗanda yake da su, da birane don karusansa, da birane don mahayan dawakansa, ya gina dukan abin da yake bukata a Urushalima, da Lebanon, da a dukan ƙasashen da suke cikin mulkinsa.

7 Dukan jama’ar da suka ragu a ƙasar, wato Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, waɗanda Isra’ilawa ba su hallaka ba,

8 daga cikin zuriyarsu waɗanda suka ragu a ƙasar a bayansu, waɗanda Isra’ilawa ba su hallaka ba, su ne Sulemanu ya tilasta su biya gandu, haka kuwa suke har wa yau.

9 Amma Sulemanu bai bautar da kowa daga cikin mutanen Isra’ila ba, su ne mayaƙansa, da shugabannin yaƙi, da shugabannin karusansa, da mahayan dawakansa.

10 Manyan shugabanni na sarki Sulemanu, mutum ɗari biyu ne da hamsin waɗanda suke iko da jama’a.

11 Sulemanu kuwa ya kawo ‘yar Fir’auna daga birnin Dawuda zuwa gidan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za ta zauna a gidan Dawuda, Sarkin Isra’ilawa ba, saboda duk wuraren da akwatin Ubangiji ya shiga sun tsarkaka.”

12 Sai Sulemanu ya miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji a gaban shirayi.

13 Sulemanu ya yi bisa ga abin da aka wajabta a yi kowace rana, bisa ga umarnin Musa a miƙa hadayu domin ranakun Asabar, da na amaryar wata, da kuma lokatan idodi uku na shekara, wato idin abinci marar yisti, da idin makonni, da na bukkoki.

14 Bisa ga ka’idar da tsohonsa Dawuda ya tsara, sai Sulemanu ya karkasa firistoci ƙungiya ƙungiya domin su yi hidima, Lawiyawa kuma bisa ga matsayinsu na yin yabo da hidima a gaban firistoci, kamar yadda aka wajabta kowace rana. Matsaran ƙofa kuma aka karkasa su ƙungiya ƙungiya bisa ga yawan ƙofofin, gama haka Dawuda, mutumin Allah, ya umarta.

15 Firistoci da Lawiyawa kuwa, ba su kauce wa umarnin sarki a kan kowane al’amari ba, ko a kan sha’anin taskoki.

16 Haka Sulemanu ya kammala aikinsa, da aka aza harsashin gina Haikalin Ubangiji, har zuwa ran da aka gama. Haka kuwa aka kammala aikin Haikalin Ubangiji.

17 Sai Sulemanu ya tafi Eziyon-geber da Elat da suke a gaɓar teku a ƙasar Edom.

18 Hiram kuwa ya aika wa Sulemanu jiragen ruwa tare da barori waɗanda suka saba da sha’ani a teku. Sai barorin tare da barorin Sulemanu, suka tafi Ofir, suka ɗauko zinariya talanti ɗari huɗu da hamsin, suka kawo wa sarki Sulemanu.

Categories
2 TAR

2 TAR 9

Sarauniyar Sheba ta Ziyarci Sulemanu

1 Sa’ad da Sarauniyar Sheba ta ji labarin irin suna da Sulemanu ya yi, sai ta zo Urushalima don ta jarraba shi da tambayoyi masu wuya. Ta zo da ‘yan rakiya masu yawa, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, da zinariya mai yawa, da duwatsu masu daraja. Sa’ad da ta zo wurin Sulemanu, ta faɗa masa dukan abin da yake a ranta.

2 Sulemanu kuwa ya amsa dukan tambayoyin da ta yi masa, ba wani abu da yake ɓoye ga Sulemanu wanda ya kāsa bayyana mata.

3 Sa’ad da Sarauniyar Sheba ta ga hikimar Sulemanu, da gidan da ya gina,

4 da irin abincin da yake kan tebur ɗinsa da irin zaman manyan mutanensa, da barorin da yake yi masa hidima, da irin tufafinsu, da masu ba da abin sha, da irin tufafinsu, ta kuma ga hadayun ƙonawa da yake miƙawa a Haikalin Ubangiji, sai ta ji ba ta da sauran kuzari.

5 Sarauniya ta ce wa sarkin, “Ashe, gaskiya ce, labarinka da na ji a ƙasata a kan al’amuranka da hikimarka.

6 Amma dā ban gaskata labarinsu ba, sai da na zo na gani da idona, ashe, ko rabin yawan hikimarka ma ba a faɗa mini ba. Ashe, duk labarin da aka faɗa mini, ka zarce haka ƙwarai.

7 Masu farin ciki ne mutanenka, da barorinka waɗanda suke yi maka hidima kullayaumin, gama kullum suna jin hikimarka.

8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka wanda yake murna da kai, wanda ya hawar da kai gadon sarautarsa, don ka zama sarki a gaban Ubangiji Allahnka. Gama Allah yana ƙaunar Isra’ila, zai kuwa tabbatar da su har abada, shi ya sa ya naɗa ka sarkinsu, don ka aikata gaskiya da adalci.”

9 Sa’an nan kuma ta ba sarki zinariya talanti ɗari da ashirin, da kayan yaji masu yawan gaske, da duwatsu masu daraja. Irin kayan yajin da Sarauniyar Sheba ta ba sarki Sulemanu ba irinsa.

10 Bayan haka kuma barorin Hiram tare da barorin Sulemanu waɗanda suka kawo zinariya daga Ofir, sun kuma kawo itatuwan algum da duwatsu masu daraja.

11 Da itatuwan algum ɗin, sarki ya yi matakan Haikalin Ubangiji da na fādar sarki, ya kuma yi garayu, da molaye saboda mawaƙa. Ba a taɓa ganin irinsu a ƙasar Yahuza ba.

12 Sarki Sulemanu kuwa ya ba Sarauniyar Sheba duk abin da ranta take bukata, da iyakar abin da take so, banda abin da ta kawo wa sarki. Sa’an nan ta koma ƙasarta, ita da barorinta.

Dukiyar Sulemanu da Shahararsa

13 Yawan zinariya da Sulemanu yake samu a shekara guda, talanti ɗari shida da sittin da shida,

14 banda wadda ‘yan kasuwa da fatake sukan kawo masa. Dukan sarakunan Arabiya da masu mulkin ƙasar kuma sun kawo wa Sulemanu zinariya da azurfa.

15 Sai Sulemanu sarki ya ƙera manyan garkuwoyi guda ɗari biyu na zinariya, kowace garkuwa nauyinta shekel ɗari shida ne na zinariya.

16 Ya kuma ƙera garkuwa ɗari uku ƙanana na zinariya, kowace garkuwa nauyinta shekel ɗari uku ne. Sarki fa ya ajiye su a gidan da aka gina da katakai daga Lebanon.

17 Sarki ya yi babban gadon sarauta na hauren giwa, ya dalaye shi da zinariya.

18 Gadon sarautar yana da matakai da ‘yar kujerar zinariya ta ɗora ƙafa haɗe da gadon. A kowane gefen gadon an yi wurin ɗora hannu, akwai kuma siffar zaki a tsaye kusa da kowane wurin ɗora hannun.

19 Akwai kuma siffofin zaki goma sha biyu, zaki biyu a kowane mataki, gefe da gefe. Ba ma sarautar da aka taɓa yi irin wannan.

20 Dukan tasoshi da finjalai na sarki Sulemanu, da zinariya tsantsa aka yi su. Haka nan kuma dukan tasoshi da finjalai da suke cikin gidan da aka gina da katakai daga Lebanon, na zinariya ne tsantsa. Ba a mai da azurfa a bakin kome ba a zamanin Sulemanu.

21 Sau ɗaya a shekaru uku, sarki yakan aika da jiragen ruwa zuwa Tarshish tare da barorin Hiram, su kawo zinariya, da azurfa, da hauren giwa, da manyan birai, da ɗawisu.

22 Sarki Sulemanu ya fi dukan sarakunan duniya dukiya da hikima.

23 Sarakunan duniya duka suna nema su sadu da Sulemanu, don su ji irin hikimar da Allah ya ba shi.

24 Kowannensu yakan kawo masa kyautai na kayayyakin azurfa, da na zinariya, da riguna, da turare, da kayan yaji, da dawakai, da alfadarai, masu yawan gaske a kowace shekara.

25 Sulemanu kuwa yana da ɗakunan dawakai da na karusai dubu huɗu (4,000), yana da mahayan dawakai dubu goma sha biyu (12,000) waɗanda suke zaune a biranen karusai, waɗansu kuma a Urushalima tare da sarki.

26 Ya mallaki dukan sarakuna tun daga Yufiretis, har zuwa ƙasar Filistiyawa har kuma zuwa kan iyakar Masar.

27 Sarki ya sa azurfa ta gama gari, kamar duwatsu a Urushalima, ya kuma sa itatuwan al’ul su yalwata kamar itatuwan ɓaure a Shefela.

28 Dawakan Sulemanu, sayo su aka yi daga Masar, da dukan sauran ƙasashe.

Rasuwar Sulemanu

29 Sauran ayyukan Sulemanu daga farko har ƙarshe an rubuta su a tarihin annabi Natan. An kuma rubuta su a annabcin Ahaija Bashilone, da kuma a wahayin Iddo maigani, game da Yerobowam ɗan Nebat.

30 A Urushalima, Sulemanu ya yi shekara arba’in yana mulkin dukan Isra’ila.

31 Sulemanu ya rasu aka binne shi tare da kakanninsa a birnin tsohonsa Dawuda, Rehobowam ɗansa shi ya gāje shi.

Categories
2 TAR

2 TAR 10

Kabilan Arewa sun yi Tawaye

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ilawa sun tafi don su naɗa shi sarki.

2 Da Yerobowam ɗan Nebat, ya ji wannan labari (gama a Masar yake sa’ad da ya guje wa sarki Sulemanu), Yerobowam kuwa ya komo daga Masar.

3 Aka aika a kira shi, sai Yerobowam da dukan Isra’ilawa, suka je wurin Rehobowam suka ce,

4 “Tsohonka ya tsananta mana, yanzu sai ka sawwaƙa mana irin tsananin da muka sha daga wurin tsohonka, da irin tilastawar da ya yi mana, sa’an nan sai mu bauta maka.”

5 Rehobowam kuwa ya ce musu, “Ku komo bayan kwana uku.” Sai jama’a suka tafi.

6 Rehobowam ya nemi shawara a gun dattawan da suke tare da tsohonsa Sulemanu, sa’ad da yake da rai, ya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa jama’ar nan?”

7 Su kuwa suka ce masa, “Idan za ka nuna wa jama’ar nan alheri, ka daɗaɗa musu rai, ka kuma yi musu magana mai daɗi, za su zama barorinka har abada.”

8 Amma ya ƙi yarda da shawarar da dattawan suka ba shi, ya nemi shawara daga wurin matasa waɗanda suka girma tare, masu yi masa hidima.

9 Ya ce musu, “Wace irin shawara za ku bayar wadda za mu amsa wa jama’an nan da suka ce mini, ‘Ka sawwaƙa mana wahalar da muka sha daga wurin tsohonka’?”

10 Sai matasa waɗanda suka girma tare da shi, suka ce masa, “Ga abin da za ka faɗa wa jama’an nan da suka ce maka, tsohonka ya tsananta musu, yanzu sai ka sawwaƙa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun ubana kauri!

11 Ubana ya tsananta muku ƙwarai, amma ni zan tsananta muku fiye da shi, ubana ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunamai.’ ”

12 Sai Yerobowam tare da dukan jama’a suka koma wurin Rehobowam a rana ta uku, kamar yadda sarki ya faɗa, “Bayan kwana uku ku komo.”

13 Sarki Rehobowam ya amsa musu da kakkausan harshe, gama bai karɓi shawarar dattawan ba.

14 Sarki Rehobowam ya yi aiki da shawarar da matasa suka ba shi, ya ce, “Ubana ya tsananta muku fiye da shi, ya hore ku da bulala, amma ni, da kunama zan hore ku.”

15 Sarki bai kasa kunne ga jama’ar ba, gama wannan al’amari, Allah ne ya aukar da shi, domin ya cika maganar da ya faɗa wa Yerobowam ɗan Nebat, ta bakin Ahaija Bashilone.

16 Da Isra’ilawa duka suka ga sarki bai saurare su ba, jama’ar kuwa suka amsa wa sarkin, suka ce, “Wane rabo muke da shi a wurin Dawuda? Ba mu da gādo a wurin ɗan Yesse. Kowa ya tafi alfarwarsa, ya ku Isra’ilawa. Ku bar Rehobowam ya lura da gidansa.”

Isra’ilawa duka kowa ya tafi alfarwarsa.

17 Amma Rehobowam ya ci gaba da mulki bisa Isra’ilawan da suke a biranen Yahuza.

18 Sai sarki Rehobowam ya aiki Adoniram shugaban aikin dole, jama’ar Isra’ila kuwa suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sai sarki Rehobowam ya gaggauta ya hau karusarsa, ya tsere zuwa Urushalima.

19 Tun daga wannan lokaci kuwa har zuwa yau, Isra’ilawa suka tayar wa gidan Dawuda.

Categories
2 TAR

2 TAR 11

Annabcin Shemaiya

1 Sa’ad da Rehobowam ya kai Urushalima, sai ya tattara zaɓaɓɓun mayaƙa, mutum dubu ɗari da dubu tamanin (180,000) daga cikin jama’ar Yahuza da ta Biliyaminu don su yi yaƙi da Isra’ila, su komo wa Rehobowam da mulki.

2 Sai Ubangiji ya yi magana da Shemaiya, mutumin Allah, ya ce,

3 “Ka faɗa wa Rehobowam ɗan Sulemanu, Sarkin Yahuza, da dukan Isra’ilawa da suke a Yahuza da Biliyaminu, ka ce,

4 ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, kada ku yi yaƙi da ‘yan’uwanku, kowa ya komo alfarwarsa, gama wannan al’amari daga gare ni yake.’ ” Suka kuwa ji maganar Ubangiji, suka koma, ba su tafi yaƙi da Yerobowam ba.

Rehobowam Ya Arzuta

5 Rehobowam ya zauna a Urushalima, ya kuwa gina birane masu kagara a Yehuza.

6 Ya gina Baitalami, da Itam, da Tekowa,

7 da Bet-zur, da Soko, da Adullam,

8 da Gat, da Maresha, da Zif,

9 da Adorayim, da Lakish, da Azeka,

10 da Zora, da Ayalon, da Hebron. Waɗannan su ne birane masu kagara a Yahuza da Biliyaminu.

11 Ya kuma ƙara ƙarfin kagaran, ya sa sarakunan yaƙi a cikinsu. Ya tara abinci, da mai, da ruwan inabi a cikinsu.

12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen nan, ya ƙara musu ƙarfi ƙwarai. Haka ya riƙe Yahuza da Biliyaminu.

Firistoci da Lawiyawa sun Zo Yahuza

13 Firistoci da Lawiyawa da suke a dukan Isra’ila kuwa suka komo gare shi daga dukan wuraren da suke.

14 Sai Lawiyawa suka bar makiyayarsu da dukiyarsu, suka koma Yahuza da Urushalima, saboda Yerobowam da ‘ya’yansa maza sun hana su yi hidimarsu ta firistocin Ubangiji.

15 Sai Yerobowam ya naɗa firistoci don masujadansa, saboda siffofin bunsurai, da na maruƙa, waɗanda ya yi.

16 Amma su waɗanda zuciyarsu take ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga kowace kabilar Isra’ila, sukan bi Lawiyawa zuwa Urushalima domin su miƙa hadaya ga Ubangiji, Allah na kakanninsu.

17 Sai suka ƙarfafa mulkin Yahuza, suka tsare mutuncin Rehobowam ɗan Sulemanu har shekara uku. Suka yi shekara uku suna tafiya a tafarkin Sulemanu.

Iyalin Rehobowam

18 Rehobowam kuwa ya auri Mahalat ‘yar Yeremot ɗan Dawuda, wadda Abihail ‘yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.

19 Mahalat ta haifa masa ‘ya’ya maza, su ne Yewush, da Shemariya, da Zaham.

20 Banda Mahalat kuma, sai ya auri Ma’aka ‘yar Absalom, wadda ta haifa masa Abaija, da Attai, da Ziza, da kuma Shelomit.

21 Rehobowam ya fi ƙaunar Ma’aka, ‘yar Absalom, fiye da dukan matansa, da ƙwaraƙwaransa. Yana kuwa da matan aure goma sha takwas, da ƙwaraƙwarai sittin. ‘Ya’yan da ya haifa maza ashirin da takwas ne, ‘ya’ya mata kuwa sittin.

22 Sai Rehobowam ya zaɓi Abaija ɗan Ma’aka, ya zama shugaban ‘yan’uwansa, gama nufinsa ya zama sarki.

23 Sai ya yi hikima ya rarraba waɗansu ‘ya’yansa maza ko’ina cikin gundumomin ƙasar Yahuza da ta Biliyaminu, a dukan birane masu kagara, ya tanada musu abinci a yalwace. Ya kuma samo musu mata masu yawan gaske.

Categories
2 TAR

2 TAR 12

Shishak Ya Kai wa Yahuza Yaƙi

1 Da mulkin Rehobowam ya kahu, ya kuma yi ƙarfi, sai Rehobowam da dukan Isra’ilawa tare da shi suka bar bin shari’ar Ubangiji.

2 A shekara ta biyar ta mulkin sarki Rehobowam, Isra’ilawa ba su bi Ubangiji da aminci ba, saboda haka Shishak, Sarkin Masar, ya hauro don ya yi yaƙi da Urushalima.

3 Aka faɗo masa da karusai dubu da ɗari biyu (1,200), da mahayan dawakai mutum dubu sittin (60,000). Mutanen da suka taho tare da sarki Shishak daga Masar, ba a san adadinsu ba, akwai Libiyawa, da Sukkimiyawa, da kuma Habashawa.

4 Ya ci birane masu kagara na Yahuza, har ya dangana da Urushalima.

5 Sai annabi Shemaiya ya zo wurin Rehobowam da sarakunan Yahuza waɗanda suka tattaru a Urushalima saboda Shishak, ya ce musu, “Ubangiji ya ce kun yashe shi, don haka shi ma ya bashe ku a hannun Shishak.”

6 Sai sarakunan Isra’ila tare da sarki Rehobowam, suka ƙasƙantar da kansu, suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”

7 Da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai ya yi magana da Shemaiya cewa, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.

8 Duk da haka fa, za su zama bayin Shishak don su san bautata dabam take da wadda ake yi wa mulkokin ƙasashe.”

9 Sai Shishak Sarkin Masar ya zo ya fāɗa wa Urushalima da yaƙi, ya kuwa kwashe dukiyoyin da suke cikin Haikalin Ubangiji, da na fādar sarki, ya yi musu ƙaƙaf. Ya kuma kwashe garkuwoyi na zinariya, waɗanda Sulemanu ya yi.

10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara, masu tsaron gidan sarki.

11 A duk lokacin da sarki ya shiga Haikalin Ubangiji, sai matsara su kawo su, daga baya kuma su maishe su a ɗakin matsaran.

12 Da sarki Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, sai fushin Ubangiji ya huce, don haka bai sa aka hallaka shi ƙaƙaf ba, har ma halin zama a ƙasar Yahuza ya yi kyau.

Mulkin Rehobowam a Taƙaice

13 Sarki Rehobowam kuwa ya kafa mulkinsa sosai a Urushalima, yana da shekara arba’in da ɗaya da haihuwa ya ci sarauta, ya yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila domin ya sa sunansa a wurin. Sunan tsohuwar Rehobowam Na’ama, Ba’ammoniya.

14 Amma ya aikata mugunta domin bai nemi Ubangiji a zuciyarsa ba.

15 Ayyukan Rehobowam, daga farko har zuwa ƙarshe an rubuta su a littafin tarihin annabi Shemaiya, da na Iddo maigani. Kullum yaƙi ne tsakanin Rehobowam da Yerobowam.

16 Rehobowam fa ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda. Abaija ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

Categories
2 TAR

2 TAR 13

Sarki Abaija na Yahuza

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yerobowam, sai Abaija ya ci sarautar Yahuza.

2 Ya yi mulki shekara uku a Urushalima, sunan tsohuwarsa Ma’aka, ‘yar Uriyel na Gibeya.

Sai yaƙi ya ɓarke a tsakanin Abaija da Yerobowam.

3 Abaija ya tafi da rundunar jarumawansa, dubu ɗari huɗu (400,000) zaɓaɓɓun mutane. Yerobowam shi kuma ya jā dāgar yaƙi don ya kara da Abaija, yana da mutum dubu ɗari takwas (800,000), zaɓaɓɓun mayaƙa ƙarfafa.

4 Sai Abaija ya hau kan Dutsen Zemarayim, wanda yake a ƙasar Ifraimu mai tuddai, ya ce, “Ku kasa kunne gare ni, ya Yerobowam da dukanku Isra’ilawa.

5 Ashe, ba ku sani ba, Ubangiji Allah na Isra’ila, ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda, da ‘ya’yansa maza har abada, ta wurin alkawarin gishiri?

6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, baran Sulemanu ɗan Dawuda, ya tashi, ya yi wa ɗan ubangidansa tawaye,

7 waɗansu marasa amfani, ‘yan iska, suka taru suka goyi bayansa, suka raina Rehobowam ɗan Sulemanu, saboda a lokacin shi yaro ne, ba shi da ƙarfin zuciya, bai iya tsayayya da su ba.

8 Yanzu kuma, so kuke ku ƙi mulkin Ubangiji wanda yake hannun ‘ya’yan Dawuda, maza, saboda yawan da kuke da shi, da gumakan maruƙan zinariya da kuke da su, waɗanda Yerobowam ya yi muku.

9 Ashe, ba ku kori firistocin Ubangiji, ‘ya’yan Haruna, maza, da Lawiyawa ba, kuka yi wa kanku firistoci kamar na al’umman sauran ƙasashe? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don ya tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.

10 “Amma a gare mu, Ubangiji shi ne Allahnmu, ba mu kuwa rabu da shi ba. Muna da firistoci, ‘ya’yan Haruna, maza, masu yi wa Ubangiji hidima, da Lawiyawa masu yi musu hidima.

11 Safe da yamma suna miƙa wa Ubangiji hadayun ƙonawa, da turare mai daɗin ƙanshi, sukan ajiye gurasar ajiyewa a kan tebur ɗin zinariya tsantsa, sukan lura da alkukin zinariya, da kuma fitilunsa kowane maraice, gama muna riƙe da umarnin Ubangiji Allahnmu, amma ku kun rabu da shi.

12 Ga shi kuwa, Allah yana tare da mu, shi ne shugabanmu, firistocinsa kuwa suna da ƙahon da akan busa lokacin yaƙi, don su busa kira na yin yaƙi. Ya ku Isra’ilawa, kada ku yi yaƙi da Ubangiji, Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”

13 Ashe, Yerobowam ya riga ya sa ‘yan kwanto, su yi musu yankan baya. Ƙungiyar mayaƙan Isra’ila tana fuskantar ta Yahuza, ‘yan kwanto kuma suna bayansu.

14 Da Yahuza suka duba, sai ga yaƙi a gabansu da bayansu. Sai suka yi kuka ga Ubangiji, firistoci kuma suka busa ƙaho.

15 Mutanen Yahuza suka yi kūwwar yaƙi. Da suka yi kuwwar yaƙin sai Ubangiji ya sa Yerobowam da dukan jama’ar Isra’ila su gudu a gaban Abaija da Yahuza.

16 Mutanen Isra’ila kuwa suka gudu a gaban Yahuza, Allah ya bashe su a hannunsa.

17 Abaija fa, da jama’arsa suka karkashe su, mugun kisa. Mutum dubu ɗari biyar (500,000) zaɓaɓɓu na Isra’ila, aka karkashe.

18 Haka kuwa aka ci nasara a kan mutanen Isra’ila a wannan lokaci. Mutanen Yahuza sun yi rinjaye saboda sun dogara ga Ubangiji, Allah na kakanninsu.

19 Abaija ya runtumi Yerobowam, ya ƙwace masa waɗansu birane, wato Betel tare da ƙauyukanta, da Yeshana tare da ƙauyukanta, da kuma Efron tare da ƙauyukanta.

20 Mulkin Yerobowam bai ƙara farfaɗowa a zamanin Abaija ba. Ubangiji kuma ya bugi Yerobowam, ya mutu.

21 Amma Abaija ya ƙasaita, ya auro mata goma sha huɗu, ya haifi ‘ya’ya maza ashirin da biyu, da ‘ya’ya mata goma sha shida.

22 Sauran ayyukan Abaija, da al’amuransa, da jawabansa, an rubuta su a littafin tarihin annabi Iddo.