Categories
NEH

NEH 8

Ezra Ya Karanta wa Jama’a Attaura

Da amaryar watan bakwai mutanen Isra’ila duk sun riga sun zauna a garuruwansu.

1 Dukan jama’a suka taru wuri ɗaya a filin Ƙofar Ruwa, suka faɗa wa Ezra, magatakarda, ya kawo Attaura ta Musa wanda Ubangiji ya ba Isra’ilawa.

2 A ran ɗaya ga watan bakwai, sai Ezra, firist, ya kawo Attaura a gaban taron jama’a, mata da maza, da dukan waɗanda za su ji, su fahimta.

3 Ya karanta Littafin, yana fuskantar filin Ƙofar Ruwa, a gaban mata da maza, da waɗanda za su iya fahimta. Mutane duka kuwa suka kasa kunne ga karatun Attaura, tun da sassafe har zuwa rana tsaka.

4 Sai Ezra, magatakarda, ya tsaya a wani dakali na itace, wanda suka shirya musamman domin wannan hidima. Sai Mattitiya, da Shema, da Anaya, da Uriya, da Hilkaya, da Ma’aseya, suka tsaya a wajen damansa, a wajen hagunsa kuwa Fedaiya, da Mishayel, da Malkiya, da Hashum, da Hashbaddana, da Zakariya, da Meshullam suka tsaya.

5 Ezra kuwa ya buɗe Littafin a gaban jama’a duka, domin yana sama da jama’a. Sa’ad da ya buɗe Littafin, sai jama’a duka suka miƙe tsaye.

6 Sai Ezra ya yabi Ubangiji Allah Maɗaukaki.

Jama’a duka suka amsa, “Amin, amin!” suna ɗaga hannuwansu. Suka sunkuyar da kansu har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada.

7 Sa’ad da jama’a suke tsaye a wurarensu, sai Lawiyawa, wato su Yeshuwa, da Bani, da Sherebiya, da Yamin, da Akkub, da Shabbetai, da Hodiya, da Ma’aseya, da Kelita, da Azariya, da Yozabad, da Hanan, da Felaya, suka fassara musu dokokin.

8 Suka karanta daga littafin dokokin Allah sosai, suka fassara musu, saboda haka jama’a suka fahimci karatun.

9 Nehemiya kuwa wanda yake mai mulki, da Ezra, firist da magatakarda, da Lawiyawa waɗanda suka fassara wa jama’a dokokin, suka ce wa dukan jama’a, “Wannan rana tsattsarka ce, ta Ubangiji Allahnku, kada ku yi baƙin ciki ko kuka.” Gama mutane duka sai kuka suke sa’ad da aka karanta musu dokokin.

10 Sa’an nan ya ce musu, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha ruwan inabi mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi, gama wannan rana tsattsarka ce ta Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin da Ubangiji ya ba ku shi ne ƙarfinku.”

11 Lawiyawa kuma suka bi suna rarrashin jama’a, suna cewa, “Ku yi shiru, gama wannan rana tsattsarka ce, kada ku yi baƙin ciki.”

12 Sai jama’a duka suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci. Suka yi murna ƙwarai domin sun fahimta dokokin da aka karanta musu.

Idin Bukkoki

13 Kashegari kuma sai shugabannin kakannin gidajen jama’a duka, tare da firistoci, da Lawiyawa, suka je wurin Ezra, magatakarda, domin su yi nazarin dokokin.

14 Sai suka iske an rubuta a cikin dokokin da Ubangiji ya umarta ta hannun Musa, cewa sai jama’ar Isra’ila su zauna a bukkoki a lokacin idi na watan bakwai.

15 Saboda haka sai suka yi shela a garuruwansu duka da a Urushalima cewa, “Ku fita zuwa tuddai ku kawo rassan zaitun, da na kadanya, da na dargaza, da na dabino, da sauran rassan itatuwa masu gazari, domin a yi bukkoki kamar yadda aka rubuta.”

16 Sai suka tafi suka kawo rassan, suka yi wa kansu bukkoki a kan rufin sorayensu, da a dandalinsu, da cikin harabar Haikalin Allah, da a dandalin Ƙofar Ruwa, da a dandalin Ƙofar Ifraimu.

17 Dukan taron jama’ar da suka komo daga zaman talala suka yi wa kansu bakkoki, suka zauna cikinsu, gama tun daga kwanakin Joshuwa ɗan Nun, har zuwa wannan rana, jama’ar Isra’ila ba su yin haka. Aka kuwa yi farin ciki mai yawa.

18 Kowace rana, tun daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra yakan karanta musu daga cikin littafin dokokin Allah. Suka kiyaye idin har kwana bakwai. A rana ta takwas kuma suka muhimmin taro bisa ga ka’ida.

Categories
NEH

NEH 9

Jama’a Sun Hurta Laifofinsu

1 A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, sai jama’ar Isra’ila suka taru, suna azumi, suna saye da tufafin makoki, suna zuba toka a kansu.

2 Suka ware kansu daga bāre duka, suka tsaya, suna hurta laifofinsu da na kakanninsu.

3 Sa’ad da suke tsaye a inda suke, sai suka ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu na yini, suna karanta littafin dokokin Ubangiji Allahnsu. Suka kuma ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu ɗin na yinin, suna ta hurta laifofi suna kuma yi wa Ubangiji Allahnsu sujada.

4 Sai Yeshuwa, da Bani, da Kadmiyel, da Shebaniya, da Bunni, da Sherebiya, da Bani, da Kenani suka tsaya a kan dakalin Lawiyawa, suka ta da murya da ƙarfi ga Ubangiji Allahnsu.

5 Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce,

“Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku,

Ku yabe shi har abada abadin.

Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii,

Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”

Addu’ar Hurta Laifi

6 Sa’an nan suka yi wannan addu’a, suka ce,

“Kai kaɗai ne Ubangiji, ya Ubangiji,

Kai ne ka yi samaniya da taurari da sararin sama.

Kai ne ka yi ƙasa, da teku, da kowane abu da yake cikinsu,

Ka ba dukansu rai,

Ikokin samaniya sun rusuna suna maka sujada.

7 Kai ne, ya Ubangiji Allah, ka zaɓi Abram,

Ka fito da shi daga Ur ta Kaldiyawa,

Ka sāke sunansa ya zama Ibrahim.

8 Ka iske shi amintacce a gare ka,

Ka kuwa yi masa alkawari.

Ka yi alkawari za ka ba shi ƙasar Kan’ana,

Da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa,

Da ta Yebusiyawa, da ta Girgashiyawa,

Ta zama inda zuriyarsa za su zauna.

Ka kuwa cika alkawarinka, gama kai mai aminci ne.

9 Ka ga wahalar kakanninmu a Masar,

Ka ji kukansu a Bahar Maliya.

10 Ka kuma aikata alamu da al’ajabai a kan Fir’auna,

Da fadawansa duka, da mutanen ƙasarsa,

Gama ka san yadda suka yi wa jama’arka danniya.

Ta haka ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau.

11 Ka yi hanya ta cikin teku domin jama’arka,

Ka sa su bi ta ciki a kan sandararriyar ƙasa.

Ka sa waɗanda suke fafararsu suka hallaka cikin zurfin teku,

Suka nutse kamar dutse.

12 Da rana ka bishe su da al’amudin girgije,

Da dare ka bishe su da al’amudin wuta.

13 Ka kuma sauka a bisa Dutsen Sinai,

Ka yi magana da jama’arka a can,

Ka ba su ka’idodin da suka dace,

Da dokoki, da kyakkyawar koyarwa.

14 Ka koya musu su kiyaye Asabar ɗinka tsattsarka,

Ka kuma ba su dokokinka ta hannun Musa bawanka.

15 Ka ba su abinci daga sama sa’ad da suka ji yunwa,

Ruwa kuma daga dutse sa’ad da suka ji ƙishi,

Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka yi alkawari za ka ba su.

16 Amma kakanninmu suka yi fāriya, suka taurare,

Suka ƙi yin biyayya da umarnanka.

17 Suka ƙi yin biyayya,

Suka manta da dukan abin da ka yi,

Suka manta da al’ajaban da ka aikata.

Cikin fāriyarsu suka zaɓi shugaba,

Don su koma cikin bauta a Masar.

Amma kai Allah ne mai gafartawa,

Kai mai alheri ne, mai ƙauna,

Jinƙanka da girma yake, ba ka yashe su ba.

18 Ko sa’ad da suka yi wa kansu ɗan marakin zubi,

Suka ce shi ne allahn da ya fisshe su daga Masar,

Ai, sun yi maka ɓatanci, ya Ubangiji.

19 Amma ba ka rabu da su a hamada ba,

Saboda jinƙanka mai girma ne.

Ba ka kuwa kawar da girgije da wuta ba,

Waɗanda suke nuna musu hanya dare da rana.

20 Ta wurin alherinka ka faɗa musu abin da ya kamata su yi,

Ka ciyar da su da manna, ka ba su ruwa su sha.

21 Ka taimake su a jeji shekara arba’in,

Ka ba su dukan abin da suke bukata,

Ƙafafunsu ba su kumbura su yi musu ciwo ba.

22 “Ka sa sun ci al’ummai da mulkoki da yaƙi,

Ƙasashen da suke maƙwabtaka da tasu.

Suka ci ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon,

Da ƙasar Bashan, inda Og yake sarki.

23 Ka riɓaɓɓanya zuriyarsu kamar taurarin sararin sama,

Ka sa suka ci ƙasar, suka zauna cikinta,

Ƙasar da aka yi wa kakanninsu alkawari za ka ba su.

24 Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan’ana.

Ka rinjayi mutanen da suke zama a can.

Ka ba jama’arka iko su yi yadda suke so

Da mutane, da sarakunan ƙasar Kan’ana.

25 Sun ci birane masu garu, da ƙasa mai dausayi,

Da gidaje cike da dukiya, da rijiyoyi, da gonakin inabi,

Da itatuwan zaitun, da itatuwa masu ‘ya’ya.

Suka ci dukan abin da suke so, suka yi taiɓa,

Suka mori dukan kyawawan abubuwan da ka ba su.

26 “Amma suka yi maka rashin biyayya, suka tayar maka,

Suka juya wa dokokinka baya,

Suka karkashe anna bawan da suka faɗakar da su,

Waɗanda suka faɗa musu su juyo gare ka.

Suka yi ta saɓa maka lokaci lokaci.

27 Saboda haka ka bar abokan gābansu su ci su, mallake su.

A wahalarsu sun yi kira gare ka domin taimako,

Ka kuwa amsa musu daga Sama.

Ta wurin jinƙanka mai yawa ka aiko musu da shugabanni,

Waɗanda suka kuɓutar da su daga maƙiyansu.

28 Sa’ad da zaman salama ya komo, sai kuma su yi zunubi,

Kai kuma sai ka bar abokan gabansu su ci su.

Duk da haka idan sun tuba, suka roƙe ka ka cece su,

Kakan ji daga Sama,sau da yawa,

Ka cece su da jinƙanka mai yawa.

29 Ka gargaɗe su su yi biyayya da koyarwarka,

Amma sun bijire wa dokoki saboda girmankai,

Ko da yake kiyaye dokarka ita ce hanyar rai.

Masu taurinkai sun taurare, sun ƙi yin biyayya.

30 “Ka yi haƙuri da su shekaru da yawa, ka gargaɗe su,

Annabawanka sun yi musu magana, amma sun toshe kunne.

Saboda haka ka sa waɗansu al’ummai su mallaki jama’arka.

31 Duk da haka, saboda yawan jinƙanka,

Ba ka yashe su ko ka hallaka su ba.

Kai Allah mai alheri ne mai jinƙai!

32 “Ya Allah, Allahnmu, da girma kake!

Kai mai banrazana ne, cike da iko!

Da aminci ka cika alkawaranka da ka alkawarta.

Daga lokacin da Sarkin Assuriya ya danne mu,

Har yanzu ma, wace wahala ce ba mu sha ba!

Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu,

Da annabawanmu, da kakanninmu,

Da dukan sauran jama’arka sun sha wahala.

Ka san irin wahalar da muka sha.

33 Ka yi daidai da ka hukunta mu haka!

Kai mai aminci ne, mu kuwa mun yi zunubi.

34 Gama kakanninmu, da sarakunanmu,

Da shugabanninmu, da firistocinmu,

Ba su kiyaye dokarka ba.

Ba su kasakunne ga umarnanka da gargaɗinka ba.

Da waɗannan ne kake zarginsu.

35 Da albarkacinka sarakuna suke mulkin jama’arka,

Sa’ad da suke ƙasashen waje, ƙasa mai dausayi ka ba su,

Amma ba su juyo su bar zunubi, su bauta maka ba.

36 Ga shi, a yau mu bayi ne a ƙasar da ka ba mu,

Wannan ƙasa mai dausayi wadda take ba mu abinci.

37 Amfanin ƙasa duk yana tafiya ga sarakunan

Da ka ɗora su a kanmu saboda mun yi zunubi.

Suna yi mana yadda suka ga dama, mu da dabbobinmu,

Muna cikin baƙin ciki.”

Jama’a Sun Sa Hannu a Yarjejeniya

38 “Saboda wannan duka muke yin alkawari mai ƙarfi a rubuce. Shugabanninmu kuwa, da Lawiyawanmu, da firistocinmu, suka buga hatimi, suka sa hannu.”

Categories
NEH

NEH 10

1 Waɗanda suka fara sa hannu a takardar alkawarin, su ne mai mulki, wato Nehemiya ɗan Hakaliya, da Zadakiya,

2-8 sa’an nan firistoci, wato

Seraiya, da Azariya, da Irmiya,

Fashur, da Amariya, da Malkiya,

Hattush, da Shebaniya, da Malluki,

Harim, da Meremot, da Obadiya,

Daniyel, da Ginneton, da Baruk,

Meshullam, da Abaija, da Miyamin,

Mawaziya, da Bilgai, da Shemaiya.

9-13 Wajen Lawiyawa kuwa, su ne

Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi daga zuriyar Henadad da Kadmiyel.

‘Yan’uwansu kuwa su ne Shebaniya, da Hodiya,

Kelita, da Felaya, da Hanan,

Mika, da Rehob, da Hashabiya,

Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,

Hodiya, da Bani, da Beninu.

14-27 Shugabannin jama’a kuwa, su ne Farosh, da Fahat-mowab,

Elam, da Zattu, da Bani,

Bunni, da Azgad, da Bebai,

Adonaija, da Bigwai, da Adin,

Ater, da Hezekiya, da Azzur,

Hodiya, da Hashum, da Bezai,

Harif, da Anatot, da Nebai,

Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,

Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa,

Felatiya, da Hanan, da Anaya,

Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,

Hallohesh, da Filha, da Shobek,

Rehum, da Hashabna, da Ma’aseya,

Ahaija, da Hanan, da Anan,

Malluki, da Harim, da Ba’ana.

Alkawarin da Aka Yi

28 Jama’ar Isra’ila, da firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan Haikali, da dukan waɗanda suka ware kansu daga sauran al’umman waɗansu ƙasashe, domin su bi dokokin Allah, su da matansu, da ‘ya’yansu mata da maza, da dai duk waɗanda suke da sani da fahimta,

29 suka haɗa kai da ‘yan’uwansu, da shugabanninsu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye dokokin Allah waɗanda ya ba bawansa Musa ba. Suka rantse za su kiyaye, su aikata umarnai, da ka’idodi, da dokokin Ubangijinmu.

30 Suka ce, “Ba za mu aurar wa mutanen ƙasar da ‘ya’yanmu mata ba. Ba kuma za mu auro wa ‘ya’yanmu maza ‘ya’yansu mata ba.

31 “Idan kuma mutanen ƙasar sun kawo kayayyaki da hatsi don sayarwa a ranar Asabar, ba za mu saya ba, ko kuma a wata tsattsarkar rana.

“A kowace shekara ta bakwai ba za mu girbe amfanin gonakinmu ba, za mu kuma yafe kowane irin bashi.

32 “Muka kuma anita kowannenmu zai riƙa ba da sulusin shekel a shekara domin aikin Haikalin Allahnmu.

33 “Za mu tanadi gurasar ajiyewa, da hadayar gāri ta kullum, da ta ranakun Asabar, da ta amaryar wata, da ta ƙayyadaddun idodi, da abubuwa masu tsarki, da hadaya don zunubi saboda yi wa jama’ar Isra’ila kafara, da dukan aiki na Haikalin Allahnmu.

34 “Muka kuma jefa kuri’a wato firistoci, da Lawiyawa, da jama’a a kan kawo itacen hadaya a Haikalin Allahnmu, bisa ga gidajen kakanninmu, a kan ƙayyadaddun lokatai a shekara, don a ƙona hadayu a bisa bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda aka rubuta a dokoki.

35 “Wajibi ne kuma mu kawo nunan fari na gonakinmu, da nunan fari na ‘ya’yan itatuwanmu kowace shekara zuwa Haikalin Ubangiji.

36 “Za mu kuma kawo ‘ya’yan farinmu maza, da na shanunmu, da na tumaki, da awaki, kamar dai yadda aka rubuta a dokoki, haka za mu kawo su a Haikalin Allahnmu, da gaban firistocin da suke hidima a Haikalin Allahnmu.

37 “Za mu kuma kawo hatsinmu na fari kullum, da sadakokinmu, da ‘ya’yan itatuwanmu, da sabon ruwan inabi, da mai, a gaban firistoci, a shirayin Haikalin Allahnmu.

“Za mu kuma ba Lawiyawa zakar amfanin gonakinmu, gama Lawiyawa ne suke tara zaka a garuruwanmu na karkara.

38 Firist kuwa daga zuriyar Haruna zai kasance tare da Lawiyawa sa’ad da suke karɓar zakar. Lawiyawa kuma za su fid da zaka daga cikin zakar da aka tara musu, su kawo ɗakin ajiya na Haikalin Allah.

39 Gama jama’ar Isra’ila da Lawiyawa za su kawo sadakoki na hatsi,da na ruwan inabi, da na mai, a ɗakin ajiya inda tasoshin Haikali suke, da gaban firistocin da suke hidima, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa.

“Ba za mu ƙyale Haikalin Allahnmu ba.”

Categories
NEH

NEH 11

Mazaunan Urushalima

1 Shugabannin jama’a kuwa suka zauna a Urushalima. Sauran jama’a kuma suka jefa kuri’a don a sami mutum guda daga cikin goma wanda zai zauna a Urushalima, wato tsattsarkan birni, sauran tara kuwa su yi zamansu a sauran garuruwa.

2 Jama’a suka sa wa dukan waɗanda suka tafi su zauna a Urushalima da yardar ransu albarka.

3 Waɗannan su ne shugabannin lardi waɗanda suka zauna a Urushalima, amma a garuruwan Yahuza kowa ya zauna a mahallinsa a garuruwansu, wato Isra’ila, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan Haikali, da zuriyar barorin Sulemanu.

4 Waɗansu mutanen Yahuza da na Biliyaminu suka zauna a Urushalima.

Daga cikin mutanen Yahuza akwai Ataya ɗan Azariya, wato jīkan Zakariya ɗan Amariya. Sauran kakanninsa su ne Shefatiya, da Mahalalel, zuriyar Feresa ɗan Yahuza.

5 Akwai kuma Ma’aseya ɗan Baruk, jīkan Kolhoze. Sauran kakanninsa su ne Hazaiya, da Adaya, da Yoyarib, da Zakariya, zuriyar Shela ɗan Yahuza.

6 Dukan mutanen Feresa da suka zauna Urushalima su ɗari huɗu da sittin da takwas ne, dukansu kuwa muhimman mutane ne.

7 Waɗannan su ne mutanen Biliyaminu, Sallai ɗan Meshullam, jīkan Yowed. Sauran kakanninsa su ne Fedaiya, da Kolaiya, da Ma’aseya, da Itiyel da Yeshaya.

8 Sa’an nan kuma ga Gabbai da Sallai danginsa, mutum ɗari tara da ashirin da takwas.

9 Yowel ɗan Zikri shi ne shugabansu, Yahuza ɗan Hassenuwa shi ne shugaba na biyu cikin birnin.

10 Na wajen firistoci, su ne Yedaiya ɗan Yoyarib, da Yakin,

11 da Seraiya ɗan Hilkiya, jīkan Shallum. Sauran kakanninsa, su ne Zadok, da Merayot, da Ahitub, mai lura da Haikalin Allah.

12 Tare da ‘yan’uwansu waɗanda suka yi aiki a Haikali, su ɗari takwas da ashirin da biyu ne.

Akwai kuma Adaya ɗan Yeroham, jīkan Felaliya. Sauran kakanninsa su ne Amzi, da Zakariya, da Fashur, da Malkiya.

13 Tare da ‘yan’uwansu shugabannin gidajen kakanni, su ɗari da arba’in da biyu. Sai kuma Amashai ɗan Azarel, jīkan Azai. Sauran kakanninsa su ne Meshillemot, da Immer.

14 Tare da ‘yan’uwansu, su ɗari da ashirin da takwas ne gwarzayen sojoji ne. Shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.

15 Na wajen Lawiyawa kuwa su ne Shemaiya ɗan Hasshub, jīkan Azrikam. Sauran kakanninsa su ne Hashabiya, da Bunni,

16 da Shabbetai, da Yozabad, ɗaya daga cikin manyan shugabanni na Lawiyawa, waɗanda suke lura da kewayen Haikalin Allah.

17 Da kuma Mattaniya ɗan Mika, jīkan Zikri, zuriyar Asaf, shi ne shugaba na farko na mawaƙan addu’a ta godiya. Bakbukiya, shi ne mataimakin Mattaniya. Ga kuma Obadiya ɗan Shemaiya, jīkan zuriyar Galal, zuriyar Yedutun.

18 Dukan Lawiyawa da suke a tsattsarkan birni su ɗari biyu da tamanin da huɗu ne.

19 Masu tsaron ƙofofi kuma su ne Akkub, da Talmon, da ‘yan’uwansu, su ɗari da saba’in da biyu ne.

20 Sauran jama’ar Isra’ila kuwa, da firistoci, da Lawiyawa suka zauna a dukan garuruwan Yahuza, kowa ya zauna a gādonsa.

21 Amma ma’aikatan Haikali suka zauna a Ofel. Ziha da Gishfa, su ne shugabannin ma’aikatan Haikali.

22 Shugaban Lawiyawan da yake a Urushalima, shi ne Uzzi ɗan Bani, jīkan Hashabiya. Sauran kakanninsa su ne Mattaniya, ɗan Mika daga zuriyar Asaf. Su ne mawaƙa a Haikalin Allah.

23 Sarki ya yi wa shugabannin mawaƙa umarni da ƙarfi a kan abin da za su yi kowace rana.

24 Fetahiya ɗan Meshezabel, daga zuriyar Zera na kabilar Yahuza, shi ne wakilin sarki a kan dukan abin da ya shafi jama’a.

Mutanen da Suke a Sauran Garuruwa da Birane

25 Game da ƙauyuka da gonakinsu kuma, waɗansu mutanen Yahuza suka zauna a Kiriyat-arba, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta,

26 da a biranen Yeshuwa, da Molada, da Bet-felet,

27 da Hazar-shuwal, da Biyer-sheba da ƙauyukanta,

28 da Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta,

29 da En-rimmon, da Zora, da Yarmut,

30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da Azeka da ƙauyukanta. Haka suka yi zango daga Biyer-sheba zuwa kwarin Hinnom.

31 Mutanen kabilar Biliyaminu suka zauna a Geba, da Mikmash, da Ayya, da Betel da sauran ƙauyuka na kewaye,

32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,

33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,

34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,

35 da Lod, da Ono, wato kwarin masu sana’a.

36 Waɗansu kashi na Lawiyawan da suke a Yahuza, aka sa su zauna a yankin ƙasar Biliyaminu.

Categories
NEH

NEH 12

Firistoci da Lawiyawa

1 Firistoci da Lawiyawa da suka komo tare da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, da Yeshuwa, su ne

Seraiya, da Irmiya, da Ezra,

2-7 Amariya, da Malluki, da Hattush,

Shekaniya, da Rehum, da Meremot,

Iddo, da Ginneton, da Abaija,

Miyamin, da Mawadiya, da Bilga,

Shemaiya, da Yoyarib, da Yedaiya,

Sallai, da Amok, da Halkiya, da Yedaiya.

Waɗannan su ne shugabannin firistoci da ‘yan’uwansu a zamanin Yeshuwa.

8-9 Lawiyawa su ne,

Yeshuwa, da Binnuyi, da Kadmiyel,

Sherebiya, da Yahuza, da Mattaniya wanda yake lura da waƙoƙin godiya, da shi da ‘yan’uwansa.

Bukbukiya da Unno, ‘yan’uwansu, suka tsaya daura da su a taron sujada.

Zuriyar Yeshuwa Firist

10 Yeshuwa shi ne ya haifi Yoyakim, Yoyakim ya haifi Eliyashib, Eliyashib ya haifi Yoyada.

11 Yoyada ya haifi Jonatan, Jonatan ya haifi Yadduwa.

Shugabannin Iyalin Firistoci

12-21 A zamanin Yoyakim babban firist, waɗannan su ne shugabannin iyalin firistoci,

na wajen Seraiya, Meraiya ne

na wajen Irmiya, Hananiya ne

na wajen Ezra, Meshullam ne

na wajen Amariya, Yehohanan ne

na wajen Malluki, Jonatan ne

na wajen Shebaniya, Yusufu ne

na wajen Harim, Adana ne

na wajen Merayot, Helkai ne

na wajen Iddo, Zakariya ne

na wajen Ginneton, Meshullam ne

na wajen Abaija, Zikri ne

na wajen Miniyamin da Mowadiya, Filtai ne

na wajen Bilga, Shimeya ne

na wajen Shemaiya, Yehonatan ne

na wajen Yoyarib, Mattenai ne

na wajen Yedaiya, Uzzi ne

na wajen Sallai, Kallai ne

na wajen Amok, Eber ne

na wajen Hilkiya, Hashabiya ne

na wajen Yedaiya, Netanel ne

Lissafin Manya na Iyalin Firistoci da Lawiyawa

22 A zamanin Eliyashib, da Yoyada, da Yohenan, da Yadduwa, Lawiyawa, har zuwa zamanin mulkin Dariyus, mutumin Farisa, aka rubuta shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa da firistoci.

23 Aka kuma rubuta shugabannin gidajen kakannin zuriyar Lawi a tarihi, har zuwa zamanin Yohenan ɗan Eliyashib.

An Rarraba Ayyukan Haikali

24 Shugabannin Lawiyawa kuwa, su ne Hashabiya, da Sherebiya, da Yeshuwa, da Kadmiyel. ‘Yan’uwansu suna tsaye kusa da su daki daki domin su yi yabo, su yi godiya kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.

25 Mattaniya, da Bakbukiya, da Obadiya, da Meshullam, da Talmon, da Akkub su ne masu tsaron ƙofofi, suna tsaron ɗakunan ajiya na wajen ƙofofi.

26 Waɗannan suna nan a zamanin Yoyakim ɗan Yeshuwa, jikan Yehozadak, da zamanin mai mulki Nehemiya, da Ezra, firist da magatakarda.

An Keɓe Garun Birni

27 A lokacin keɓe garun Urushalima, sai aka nemo Lawiyawa a wurarensu duka don a kawo su Urushalima, su yi bikin keɓewa da farin ciki da godiya, da raira waƙoƙi da kuge, da garaya, da molo.

28 Aka tattara mawaƙa daga kewayen Urushalima da ƙauyukan Netofatiyawa.

29 Da kuma daga Betgilgal da karkarar Geba, da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.

30 Sai firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma tsarkake jama’a, da ƙofofi, da garun.

31 Sai na sa shugabannin Yahuza su hawo garu, sa’an nan na sa manyan ƙungiyoyi biyu waɗanda za su yi godiya, su tafi a jere.

Ƙungiya guda ta bi wajen dama a kan garun zuwa Ƙofar Juji.

32 Hoshaiya da rabin sugabannin Yahuza suka bi bayansu,

33 tare da Azariya, da Ezra, da Meshullam,

34 da Yahuza, da Biliyaminu, da Shemaiya, da Irmiya.

35 Sa’an nan waɗansu ‘ya’yan firistoci, masu busar ƙaho, su ne Zakariya ɗan Jonatan, jīkan Shemaiya. Sauran kakanninsa su ne Mattaniya, da Mikaiya, da Zakkur, daga zuriyar Asaf.

36 Sauran ‘yan’uwansa su ne Shemaiya, da Azarel, da Milalai, da Gilalai, da Ma’ai, da Netanel, da Yahuza, da Hanani. Suna da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗekaɗe. Ezra magatakarda ne yake gabansu.

37 A Ƙofar Maɓuɓɓuga kuwa, sai suka yi gaba sosai wajen matakan birnin Dawuda, wajen hawan garu, daga bisa gidan Dawuda, zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.

38 Ƙungiyar jama’a ta biyu ta masu yin waƙoƙin godiya, ta bi ta wajen hagu. Na bi su tare da rabin jama’a a kan garu, sama da Hasumiyar Tanderu zuwa garu mai fādi,

39 da Kuma sama da Ƙofar, Ifraimu da wajen Tsohuwar Ƙofar, da wajen Ƙofar Kifi, da Hasumiyar Hananel, da Hasumiyar Ɗari zuwa Ƙofar Tumaki, sai suka tsaya a Ƙofar Tsaro.

40 Haka fa ƙungiyoyi biyu ɗin nan masu raira waƙoƙin godiya suka tsaya a Haikalin Allah.

Ni da rabin shugabanni muna tare da su.

41 Tare da firistoci kuma, wato su Eliyakim, da Ma’aseya, da Miniyamin, da Mikaiya, da Eliyehoyenai, da Zakariya, da Hananiya, suna busa ƙaho,

42 da kuma Ma’aseya, da Shemaiya, da Ele’azara, da Uzzi, da Yehohanan, da Malkiya, da Elam, da Ezer, suna raira waƙoƙi, Yezrahiya kuma shi ne shugabansu.

43 Jama’a suka miƙa hadayu da yawa a wannan rana, suka yi murna, gama Allah ya faranta musu zuciya ƙwarai. Mata da yara kuma suka yi murna. Aka ji muryar murnar mutanen Urushalima daga nesa.

Shiri don Firistoci da Lawiyawa

44 A ran nan aka sa mutanen da za su lura da ɗakunan ajiya, da sadakoki, da nunan fari, da zaka. Su ne za su tara nunan fari daga gonakin da suke kusa da garuruwa, bisa ga yadda doka ta ce, saboda firistoci da Lawiyawa, gama mutanen Yahuza sun yi murna saboda hidimar da firistoci da Lawiyawa suka yi.

45 Sun yi wa Allahnsu sujada, sun yi hidimar tsarkakewa tare da mawaƙa da masu tsaron ƙofofi kamar yadda Dawuda da ɗansa Sulemanu suka umarta.

46 A dā a zamanin Dawuda da Asaf akwai shugaban mawaƙa, akwai kuma waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.

47 A zamanin Zarubabel da zamanin Nehemiya dukan jama’ar Isra’ila suka biya wa mawaƙa da masu tsaron ƙofofi bukatarsu ta kowace rana. Sun kuma ba Lawiyawa sadokoki, su Lawiyawa kuma suka ba zuriyar Haruna nasu rabo.

Categories
NEH

NEH 13

Gyare-gyaren da Nehemiya Ya Yi

1 A wannan rana aka karanta daga littafin Musa a kunnuwan jama’a. A cikinsa aka tarar da inda aka rubuta, cewa kada Ba’ammone, ko mutumin Mowab ya shiga taron jama’ar Allah.

2 Gama ba su taryi jama’ar Isra’ila da abinci da abin sha ba, amma suka yi ijara da Bal’amu ya zo ya la’anta musu su, amma Allahnmu ya juyar da la’anar ta zama albarka.

3 Da mutane suka ji dokokin, sai suka ware dukan waɗanda suke ba Isra’ilawa ba.

4 Kafin wannan lokaci Eliyashib, firist, wanda aka sa shi shugaban ɗakunan ajiya na Haikalin Allahnmu, wanda yake da dangantaka da Tobiya,

5 ya shirya wa Tobiya babban ɗaki inda dā aka ajiye hadaya ta gari, da turare, da tasoshi, da zakar hatsi, da ruwan inabi, da mai, waɗanda aka umarta a ba Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da inda aka ajiye sadakokin da ake ba firistoci.

6 Ba na nan a Urushalima sa’ad da wannan abu ya faru, gama a shekara ta talatin da biyu ta sarautar Artashate, Sarkin Babila, na tafi wurin sarki. Daga baya sarki ya ba ni izini in koma.

7 Da na komo Urushalima, sai na ga mugun abin da Eliyashib ya yi domin Tobiya, yadda ya shirya masa ɗaki a filin Haikalin Allah.

8 Sai na husata ƙwarai, na fitar da kayan ɗakin Tobiya a waje.

9 Sai na umarta, suka kuwa tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da tasoshin Haikalin Allah, da hadaya ta gari, turare a ciki.

10 Na kuma iske ba a ba Lawiyawa rabonsu ba. Saboda wannan Lawiyawa da mawaƙa masu hidima suka watse zuwa gonakinsu.

11 Sai na yi wa shugabanni faɗa, na ce, “Me ya sa aka ƙi kula da Haikalin Allah?” Sa’an nan na tara Lawiyawa da mawaƙa, na sa su a wuraren aikinsu.

12 Sai dukan mutanen Yahuza suka kawo zakar hatsi, da ta ruwan inabi, da ta mai, a ɗakunan ajiya.

13 Sai na sa Shelemiya, firist, da Zadok, magatakarda, da Fedaiya daga cikin Lawiyawa su zama masu lura da ɗakunan ajiya. Na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, jikan Mattaniya ya yi aiki tare da su, gama su amintattu ne. Aikinsu shi ne su raba wa ‘yan’uwansu abin da aka kawo.

14 “Ka tuna da ni, ya Allahna, saboda wannan. Kada ka manta da ayyukan kirki da na yi a Haikalin Allah da kuma na hidimarsa.”

15 A kwanakin nan na ga mutane a Yahuza suna matse ruwan inabi, suna labta wa jakunansu buhunan hatsi, da ruwan inabi, da ‘ya’yan inabi, da ɓaure, da kaya iri iri, suna kawo su cikin Urushalima a ran Asabar. Sai na yi musu faɗa a kan sayar da abinci a wannan rana.

16 Mutanen Taya da suke zaune a birnin sukan kawo kifi da kaya iri iri, su sayar wa mutanen Yahuza a Urushalima a ranar Asabar.

17 Sai na tsauta wa manyan mutanen Yahuza, na ce musu, “Wane irin mugun abu ne kuke yi haka, kuna ɓata ranar Asabar?

18 Ashe, ba haka kakanninku suka yi ba, har wannan ya sa Allahnmu ya kawo mana masifa, mu da dukan birnin? Duk da haka kuna ƙara kawo wa Isra’ila hasala saboda kuna ɓata ranar Asabar.”

19 Magariba na yi kafin ranar Asabar, sai na yi umarni a rufe ƙofofin Urushalima, kada a buɗe su sai Asabar ta wuce. Na sa waɗansu barorina a ƙofofin, don kada su bari a shigo da kaya ran Asabar.

20 Sau ɗaya ko sau biyu, ‘yan kasuwa da masu sayar da abubuwa iri iri suka kwana a bayan Urushalima.

21 Amma na tsauta musu, na ce, “Me ya sa kuka kwana a bayan garu? Idan kun ƙara yin haka zan kama ku.” Tun daga wannan lokaci ba su ƙara zuwa a ranar Asabar ba.

22 Sai kuma na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu, su yi tsaron ƙofofin don a kiyaye ranar Asabar da tsarki.

“Ya Allahna, ka tuna da wannan aiki nawa, ka rayar da ni saboda girman madawwamiyar ƙaunarka.”

23 A waɗannan kwanaki kuma na ga waɗansu Yahudawa waɗanda suka auro mata daga Ashdod, da Ammon, da Mowab.

24 Rabin ‘ya’yansu suna magana da harshen Ashdod, ko wani harshe dabam, amma ba su iya yin magana da harshen Yahuza ba.

25 Sai na yi musu faɗa na la’ance su, na bugi waɗansu daga cikinsu, na ciccire gashin kansu, na sa su rantse da Allah, cewa ba za su aurar da ‘ya’yansu mata ga ‘ya’yan maza na bare ba, ko kuma su auro wa ‘ya’yansu maza ‘yan matan bare, ko su auro wa kansu.

26 Na faɗa musu cewa, “Ba a kan irin wannan ba ne Sulemanu Sarkin Isra’ila ya yi laifi? A al’ummai, ba sarki kamarsa. Allahnsa ya ƙaunace shi, ya sarautar da shi a Isra’ila, duk da haka baren mata suka sa shi ya yi zunubi.

27 Ba za mu yarda da abin da kuke yi ba, har mu aikata wannan mugunta ta rashin aminci ga Allahnmu, da za mu auro baren mata.”

28 Ɗaya daga cikin ‘ya’yan Yoyada ɗan Eliyashib, babban firist, surukin Sanballat ne, Bahorone, saboda haka sai na kore shi daga wurina.

29 “Ka tuna da su, ya Allahna don sun ƙazantar da aikin firistoci da alkawarin zama firist da Lawiyawa.”

30 Da haka na tsarkake su daga kowane baƙon abu, na sa firistoci da Lawiyawa cikin aiki, kowa ya kama aikinsa.

31 Na kuma shirya yadda za a tara itace domin yin hadaya a kan kari, da kuma lokacin da za a kawo nunan fari.

“Ya Allahna, ka tuna da ni, ka yi mini alheri.”

Categories
ESTA

ESTA 1

Sarauniya Bashti Ta Raina Sarki Ahasurus

1 Ahasurus ya yi sarauta daga Hindu har zuwa Habasha, ya mallaki larduna ɗari da ashirin da bakwai.

2 A waɗannan kwanaki, sarki Ahasurus yake zaune a gadon sarautarsa a Shushan, masarauta.

3 A shekara ta uku ta sarautarsa, sai ya yi biki saboda sarakunansa, da barorinsa, da sarakuna yaƙin Farisa da Mediya, da manyan mutane, da hakiman larduna.

4 Sai ya nuna wadatar mulkinsa, da martabarsa, da darajarsa har kwanaki masu yawa, wato kwana ɗari da tamanin.

5 Bayan da waɗannan kwanaki sun cika, sai sarki ya yi wa manya da ƙanana waɗanda suke a Shushan, wato masarauta, biki, har na kwana bakwai a filin lambun fādar sarki.

6 Aka kewaye wurin da fararen labule da na shunayya na lallausan lilin, aka ɗaure da kirtani na lallausan lilin mai launin shunayya haɗe da zobban azurfa da ginshiƙai na sassaƙaƙƙun duwatsu masu daraja. Akwai gadaje na zinariya da na azurfa a kan daɓen da aka yi da duwatsu masu daraja, masu launi iri iri.

7 Aka ba da sha a finjalai iri iri na zinariya. Aka shayar da su da ruwan inabi irin na sarauta a yalwace bisa ga wadatar sarki.

8 Aka yi ta sha bisa ga doka, ba wanda aka matsa masa, gama sarki ya umarci fādawansa su yi wa kowa yadda yake so.

9 Sarauniya Bashti kuma ta yi wa mata babban biki a fādar sarki Ahasurus.

10 A rana ta bakwai sa’ad da zuciyar sarki take murna saboda ruwan inabi, sai ya umarta bābāninsa guda bakwai, waɗanda suke yi masa hidima, wato Mehuman, da Bizta, da Harbona, da Bigta, da Abagta, da Zetar, da Karkas,

11 su kirawo sarauniya Bashti ta zo wurinsa da kambin sarauta, don ya nuna wa jama’a da shugabanni kyanta, gama ita kyakkyawa ce.

12 Amma sarauniya Bashti ta ƙi zuwa kamar yadda sarki ya umarci bābānin su faɗa mata. Wannan ya sa sarki ya husata ƙwarai.

13 Sarki kuwa ya nemi shawara ga masu hikima waɗanda suka ƙware zamani, gama sarki ya saba da yin haka ga waɗanda suka san doka da shari’a.

14 Su ne mutanen da suke kusa da shi, wato Karshena, da Shetar, da Admata, da Tarshish, da Meres, da Marsena, da Memukan. Su ne sarakuna bakwai na Farisa da Mediya, su ne masu zuwa wurin sarki, su ne kuma na fari a mulkin.

15 Sarki ya ce, “Bisa ga doka, me za a yi da sarauniya Bashti da yake ba ta yi biyayya da umarnin da na aika ta hannun babani ba?”

16 Sai Memukan ya amsa a gaban sarki da sauran sarakai, ya ce, “Ba sarki ne kaɗai sarauniya Bashti ta yi wa laifi ba, amma har dukan sarakai, da sauran jama’a da suke cikin dukan lardunan sarki Ahasurus.

17 Gama za a sanar wa dukan mata abin da sarauniya ta yi, gama abin da ta yi zai sa su raina mazansu, gama za su ce, ‘Sarki Ahasurus ya umarta a kirawo masa sarauniya Bashti, amma ta ki.’

18 Yau ma matan Farisa da Mediya waɗanda suka ji abin da sarauniya ta yi, haka za su faɗa wa dukan hakimai. Wannan zai kawo raini da fushi mai yawa.

19 Idan sarki ya yarda, bari ya yi doka, a kuma rubuta ta cikin dokokin Farisa da Mediya don kada a sāke ta, cewa Bashti ba za ta ƙara zuwa wurin sarki Ahasurus ba. Bari sarki ya ba da matsayinta na sarauta ga wata wadda ta fi ta.

20 Sa’ad da aka ji dokar sarki, wadda zai yi a dukan babbar ƙasarsa, dukan mata za su girmama mazansu, ƙanana da manya.”

21 Wannan shawara ta gamshi sarki da sauran sarakai, sarki ya yi kamar yadda Memukan ya shawarta.

22 Sai ya aika da takardu zuwa dukan lardunan sarki, kowane lardi da irin rubutunsa, kowaɗanne mutane kuma da harshensu, domin kowane namiji ya zama shugaban gidansa, ya kuma zama mai faɗa a ji.

Categories
ESTA

ESTA 2

Esta Ta Zama Sarauniya

1 Bayan waɗannan abubuwa, sa’ad da sarki Ahasurus ya huce daga fushinsa, sai ya tuna da abin da Bashti ta yi, da dokar da aka yi a kanta.

2 Sa’an nan barorin sarki waɗanda suke yi masa hidima suka ce masa, “Bari a samo wa sarki ‘yan mata, budurwai, kyawawa.

3 Bari kuma sarki ya sa shugabanni a cikin dukan lardunan mulkinsa su tara dukan kyawawan ‘yan mata, budurwai, a gidan matan kulle a masarauta a Shushan, ƙarƙashin Hegai bābā na sarki, wanda yake lura da mata. A riƙa ba budurwan man shafawa.

4 Bari sarki ya zaɓi budurwar da ta gamshe shi, ta zama sarauniya maimakon Bashti.”

Sarki fa ya ji daɗin wannan shawara, ya kuwa yi haka ɗin.

5 Akwai wani Bayahude a masarauta a Shushan, mai suna Mordekai ɗan Yayir, ɗan Shimai, ɗan Kish mutumin Biliyaminu.

6 An kamo shi a Urushalima tare ‘yan zaman talala waɗanda aka kwashe tare da Yekoniya Sarkin Yahuza, wanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kai su zaman talala.

7 Mordekai ne ya goyi Hadassa, wato Esta, ‘yar kawunsa, gama ita marainiya ce. Ita kuwa kyakkyawa ce. Sa’ad da iyayenta suka rasu, sai Mordekai ya karɓe ta tankar ‘yarsa.

8 Sa’ad da aka yi shelar dokar sarki, aka kuma tattara ‘yan mata a masarauta a Shushan, a hannun Hegai, sai aka ɗauko Esta zuwa fādar sarki, aka sa ta a hannun Hegai wanda yake lura da mata.

9 Esta kuwa ta gamshi Hegai, ta kuma sami farin jini a wurinsa, sai nan da nan ya ba ta man shafawa, da rabon abincinta, da zaɓaɓɓun kuyangi guda bakwai daga fādar sarki. Ya kuma kai ta da kuyanginta a wuri mafi kyau na gidan matan kulle.

10 Esta ba ta riga ta bayyana asalin mutanenta, da danginta ba, gama Mordekai ya umarce ta kada ta yi.

11 Kowace rana Mordekai yakan zo shirayin gidan matan kulle don ya san yadda Esta take.

12 Sa’ad da lokacin kowace budurwa ya yi da za ta shiga wurin sarki Ahasurus, bayan da ta riga ta yi wata goma sha biyu na ka’idar yin kwalliyar mata, wato takan shafe jiki da man ƙanshi wata shida, ta kuma shafe jiki da turare da man shafawa wata shida,

13 sa’an nan budurwar za ta shiga wurin sarki, sai a ba ta dukan abin da take bukata ta ɗauko daga gidan matan kullen zuwa fādar sarki.

14 Takan tafi da yamma, ta koma gidan matan kulle na biyu da safe, a hannun Shawashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwaraƙwarai. Ba za ta ƙara zuwa wurin sarki ba, sai ko ta sami farin jini a wurin sarki sa’an nan a kirawo ta.

15 Sa’ad da lokacin Esta ‘yar Abihail, kawun Mordekai, wadda Mordekai ya karɓe ta tankar ‘yarsa, ya yi da za ta shiga wurin sarki, ba ta bukaci kome ba, sai dai abin da Hegai, bābā na sarki, wanda yake lura da mata, ya ce. Esta kuwa tana da farin jini a idon duk wanda ya gan ta.

16 Sa’ad da aka kai Esta wurin sarki Ahasurus a fādarsa a wata na goma, wato watan Tebet, a shekara ta bakwai ta sarautarsa,

17 sai sarki ya ƙaunaci Esta fiye da dukan sauran matan. Ta kuwa sami alheri da farin jini a wurinsa fiye da sauran budurwan, saboda haka ya sa kambin sarauta a kanta. Ya naɗa ta sarauniya maimakon Bashti.

18 Sarki kuwa ya yi wa sarakunansa da barorinsa ƙasaitaccen biki saboda Esta. Ya kuma ba larduna hutu, ya ba da kyautai da yawa irin na sarauta.

Mordekai Ya Ceci Ran Sarki

19 Sa’ad da aka tara budurwai a karo na biyu, Mordekai yana zaune a ƙofar sarki.

20 Har yanzu dai Esta ba ta bayyana asalin danginta da mutanenta ba, kamar yadda Mordekai ya umarce ta, gama Esta tana yi wa Mordekai biyayya kamar ta yi tun lokacin da yake renonta.

21 A kwanakin nan sa’ad da Mordekai yake zaune a ƙofar sarki, sai babani biyu na sarki, wato Bigtana da Teresh waɗanda suke tsaron ƙofar, suka yi fushi, har suka nema su kashe sarki Ahasurus.

22 Wannan maƙarƙashiya ta sanu ga Mordekai, shi kuwa ya faɗa wa sarauniya Esta. Esta kuma ta faɗa wa sarki da sunan Mordekai.

23 Sa’ad da aka bincika al’amarin aka tarar haka yake. Sai aka rataye mutum biyu ɗin a kan gumagumai. Aka kuma rubuta labarin a littafin tarihi a gaban sarki.

Categories
ESTA

ESTA 3

Maƙaƙashiyar Haman don Ya Hallaka Yahudawa

1 Bayan waɗannan abubuwa, sai sarki Ahasurus ya gabatar da Haman ɗan Hammedata Ba’agage. Ya fīfita shi bisa dukan sarakunan da suke tare da shi.

2 Dukan barorin sarki waɗanda suke a bakin ƙofar sarki suka rusuna suka yi wa Haman mubaya’a, gama sarki ya umarta a yi masa haka. Amma Mordekai bai rusuna ya yi masa mubaya’a ba.

3 Sai barorin sarki waɗanda suke a bakin ƙofar sarki suka ce wa Mordekai, “Me ya sa ka karya dokar sarki?”

4 Sa’ad da suka yi ta yi masa magana kowace rana, shi kuwa bai kasa kunne gare su ba, sai suka faɗa wa Haman, don su gani ko maganar Mordekai za ta tabbata, gama ya faɗa musu shi Bayahude ne.

5 Sa’ad da Haman ya ga Mordekai bai rusuna ya yi masa mubaya’a ba, sai ya husata.

6 Har ma ya ga a kashe Mordekai kaɗai, wannan bai isa ba. Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya nema ya hallaka dukan Yahudawa, wato kabilar Mordekai, waɗanda suke a dukan mulkin Ahasurus.

7 A watan fari, wato watan Nisan, a shekara ta goma sha biyu ta sarautar sarki Ahasurus, sai suka yi ta jefa Fur, wato kuri’a, a gaban Haman kowace rana da kowane wata har kuri’a ta faɗo a kan watan goma sha biyu, wato watan Adar.

8 Sa’an nan Haman ya ce wa sarki Ahasurus, “Akwai waɗansu mutane da suke warwatse a jama’ar dukan lardunan mulkinka. Dokokinsu sun sha bambam da na sauran mutane, ba su kuma kiyaye dokokin sarki, don haka ba shi da amfani a wurin sarki ya yi ta haƙuri da su.

9 Idan ya gamshi sarki, bari a yi doka a hallaka su, ni kuwa zan ba waɗanda suke tafiyar da aikin sarki, talanti dubu goma (10,000) na azurfa, don su sa a baitulmalin sarki.”

10 Sarki kuwa ya zare zobensa na hatimi daga hannunsa ya ba Haman Ba’agage, ɗan Hammedata, maƙiyin Yahudawa.

11 Sa’an nan ya ce masa, “Da kuɗin, da mutanen duk an ba ka, ka yi yadda ka ga dama da su.”

12 Sai aka kirawo magatakardun sarki a rana ta goma sha uku ga watan fari. Bisa ga umarnin Haman aka rubuta doka zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da masu mulkin dukan larduna, da sarakunan shugabannin jama’a. Aka rubuta zuwa kowane lardi da irin rubutunsa, da kowaɗanne mutane kuma da harshensu da sunan sarki Ahasurus. Aka hatimce ta da hatimin zoben sarki.

13 Aka ba ‘yankada-ta-kwana takardun zuwa dukan lardunan sarki don a hallaka Yahudawa, a karkashe, a ƙarasa su, ƙanana da manya, mata da maza, duk a rana ɗaya, wato ran goma sha uku ga watan goma sha biyu, wato watan Adar, a kuma washe dukiyoyinsu.

14 Sai a ba kowane lardi fassarar dokar, don a yi shelarta ga dukan mutane, su kasance a shirye don ranar.

15 Bisa ga umarnin sarki, sai ‘yankada-ta-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a Shushan, masarauta. Sarki da Haman kuwa suka zauna don su sha, amma birnin Shushan ya ruɗe.

Categories
ESTA

ESTA 4

Esta Ta Ta Yi Roƙo don Mutanenta

1 Da Mordekai ya ji dukan abin da aka yi, sai ya yage tufafinsa, sa’an nan ya sa rigar makoki, ya zuba toka a kā. Ya fita zuwa tsakiyar birni, yana ta rusa kuka da ƙarfi.

2 Ya tafi kusa da ƙofar sarki, gama ba a yarda wani ya shiga ƙofar sarki da rigar makoki ba.

3 A kowane lardi inda aka kai umarni da dokar sarki, Yahudawa suka yi babban baƙin ciki, da azumi, da kuka, da makoki. Waɗansu da yawa da rigunan makoki a cikin toka suka kwanta.

4 Sa’ad da kuyangin Esta da bābāninta suka tafi suka faɗa mata abin da Mordekai yake yi, sai sarauniya Esta ta damu ƙwarai, ta aika da riguna a sa wa Mordekai, ya tuɓe rigar makokinsa, amma Mordekai ya ƙi, bai yarda ba.

5 Sai Esta ta kirawo Hatak, ɗaya daga cikin bābānin sarki, wanda aka sa ya yi mata hidima, ta aike shi wurin Mordekai, don ya ji abin da ya faru, har ya sa yake yin haka.

6 Hatak kuwa ya tafi wurin Mordekai a dandalin birnin, a gaban ƙofar sarki.

7 Sai Mordekai ya faɗa masa dukan abin da ya faru da shi, da yawan ƙudin da Haman ya ce zai biya a sa a baitulmalin sarki don a hallaka Yahudawa.

8 Mordekai kuma ya ba Hatak takardar dokar da aka yi a Shushan don a hallaka Yahudawa domin ya tafi ya nuna wa Esta ya sanar da ita, ya kuma umarce ta ta tafi wurin sarki don ta roƙi arziki ga sarki saboda mutanenta.

9 Sai Hatak ya tafi, ya faɗa wa Esta abin da Mordekai ya ce.

10 Esta kuma ta yi magana da Hatak sa’an nan ta aike shi da saƙo a wurin Mordekai cewa,

11 “Dukan barorin sarki da mutanen lardunan sarki sun sani duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, ba tare da an kira shi ba, to, doka ɗaya ce take kan mutum, wato kisa, ko mace ko namiji, sai dai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don ya rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”

12 Hatak ya tafi ya faɗa wa Mordekai abin da Esta ta ce.

13 Sai Mordekai ya ce masa ya je ya faɗa wa Esta haka, “kada ki yi tsammani za ki tsira a fādar sarki fiye da sauran Yahudawa.

14 Gama idan kin yi shiru a irin wannan lokaci, to, taimako da ceto za su zo wa Yahudawa ta wata hanya dabam, amma ke da gidan iyayenki za ku halaka. Wa ya sani ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan maƙami?”

15 Sa’an nan Esta ta ce masa ya je ya faɗa wa Mordekai cewa,

16 “Ka tattara dukan Yahudawan da suke a Shushan, su yi domin, kada su ci ko su sha dare da rana, har kwana uku. Ni kuma da kuyangina za mu yi haka nan. Sa’an nan zan tafi wurin sarki, ko da yake ba bisa ga doka ba, idan na halaka, na halaka ke nan.”

17 Sai Mordekai ya tafi ya yi abin da Esta ta umarce shi.