Categories
AYU

AYU 15

Elifaz Ya Tsauta wa Ayuba

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Surutai, Ayuba! Surutai!

3 Ba wani mai hikima wanda zai yi magana irin taka,

Ko kuma ya kāre kansa da irin maganganun da ba su da ma’ana.

4 Kana karya jama’a, kana hana su jin tsoron Allah,

Kana hana su yin addu’a gare shi.

5 Mugun lamirinka shi ne yake magana yanzu,

Kana ƙoƙari ka ɓuya a bayan maganganunka na wayo.

6 Ba na bukata in kā da kai,

Kowace kalma da ka hurta ta kā da ka.

7 “Kana tsammani kai ne mutumin da aka haifa na farko?

Sa’ad da Allah ya yi duwatsu kana nan?

8 Ko ka taɓa jin shirye-shiryen da Allah ya yi?

Ko kai kaɗai kake da hikima a cikin mutane?

9 Ba wani abu da ka sani da mu ba mu sani ba.

10 Daga wurin mutanen da suka yi furfura muka koyi hikimarmu.

Mun koyi hikimarmu daga mutane waɗanda aka haife su

Tun kafin a haifi mahaifinka.

11 “Allah yana ta’azantar da kai,

Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi?

Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi.

12 Amma ka ta da hankalinka,

Kana ta zazzare mana ido da fushi.

13 Fushi kake yi da Allah, kana ƙinsa.

14 Akwai mutumin da yake tsarkakakke sarai?

Akwai mutumin da yake cikakke a wurin Allah?

15 Me ya sa Allah bai sakar wa mala’ikunsa kome ba?

Har su ma ba tsarkaka suke a gare shi ba.

16 Mutum yakan sha mugunta kamar yadda yake shan ruwa,

Hakika mutum ya lalace, ya zama mai rainako.

17 “Yanzu ka saurara, ya Ayuba, ga abin da na sani.

18 Mutane masu hikima sun koya mini gaskiya

Wadda suka koya daga wurin kakanninsu,

Ba su kuwa ɓoye mini asirin kome ba.

19 Ƙasaru ‘yantacciya ce daga baƙi

Ba wanda zai raba su da Allah.

20 “Mugun mutum mai zaluntar sauran mutane

Zai kasance da wahala muddin ransa.

21 Zai ji ƙarar muryoyi masu firgitarwa a kunnuwansa.

‘Yan fashi za su fāɗa masa

Sa’ad da yake tsammani ba abin da zai same shi.

22 Bai sa zuciya zai kuɓuta daga duhu ba,

Gama takobi yana jiransa a wani wuri don ya kashe shi.

23 Yana ta yawon neman abinci, yana ta cewa, ‘Ina yake?’

Ya sani baƙin ciki ne yake jiransa a nan gaba. Kamar sarki mai iko,

24 Haka masifa take shirin fāɗa masa.

25 “Wannan shi ne ƙaddarar mutum,

Wanda ya nuna wa Allah yatsa,

Ya kuwa raina Mai Iko Dukka.

26 Wannan mutum mai girmankai ne, ɗan tawaye.

27 Ya ɗauki garkuwarsa kamar ɗan yaƙi,

Ya ruga don ya yi yaƙi da Allah.

28 Shi ne mutumin da ya ci birane da yaƙi,

Ya ƙwace gidajen waɗanda suka tsere,

Amma yaƙi ne zai hallaka birane da gidaje.

29 Arzikinsa ba zai daɗe ba,

Duk abin da ya mallaka ba zai daɗe ba.

Har inuwarsa ma za ta shuɗe,

30 Ba kuwa zai kuɓuta daga duhu ba.

Zai zama kamar itacen da wuta ta ƙone rassansa,

Kamar itace kuma da iska ta kaɗe furensa.

31 Idan wauta tasa ta kai shi ga dogara ga mugunta,

To, mugunta ce kaɗai zai samu.

32 Kafin kwanakinsa su cika zai bushe,

Zai bushe kamar reshe, ba zai ƙara yin ganye ba.

33 Zai ama kamar itacen inabi

Wanda ‘ya’yansa suka kakkaɓe tun kafin su nuna,

Kamar itacen zaitun wanda bai taɓa yin ‘ya’ya ba.

34 Marasa tsoron Allah ba za su sami zuriya ba,

Wuta za ta cinye gidajen da aka gina da dukiyar rashawa.

35 Waɗannan su ne irin mutanen da suke shirya tarzoma, su aikata mugunta.

Kullum zuciyarsu cike take da ruɗarwa.”

Categories
AYU

AYU 16

Ayuba Ya Yi Kukan abin da Allah Yake Yi

1 Ayuba ya yi magana.

2 “Ai, na taɓa jin magana irin wannan,

Ta’aziyyar da kake yi azaba ce kawai.

3 Ka dinga yin magana ke nan har abada?

A kullum maganarka ita ce dahir?

4 In da a ce a matsayina kake, ni kuma ina a naka,

Ina iya faɗar duk abin da kake faɗa yanzu.

Da sai in kaɗa kaina da hikima,

In dulmuyar da kai a cikin rigyawar maganganu.

5 Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa,

In yi ta yi maka maganar ta’azantarwa.

6 “Amma ba abin da zan faɗa wanda zai taimaka,

Yin shiru kuma ba zai raba ni da azaba ba.

7 Ka gajiyar da ni, ya Allah,

Ka shafe iyalina.

8 Ka kama ni, kai maƙiyina ne.

Na zama daga fata sai ƙasusuwa,

Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne.

9 Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa,

Yana dubana da ƙiyayya.

10 Mutane sun buɗe baki don su haɗiye ni

Suna kewaye ni suna ta marina.

11 Allah ya bashe ni ga mugaye.

12 Dā ina zamana da salama,

Amma Allah ya maƙare ni,

Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni.

Allah ya maishe ni abin bārata.

13 Ya harbe ni da kibau daga kowane gefe.

Kiban sun ratsa jikina sun yi mini rauni,

Duk da haka bai nuna tausayi ba!

14 Ya yi ta yi mini rauni a kai a kai,

Ya fāɗa mini kamar soja da ƙiyayya ta haukata.

15 “Ina makoki saye da tsummoki,

Ina zaune cikin ƙura a kunyace.

16 Na yi ta kuka har fuskata ta zama ja wur,

Idanuna kuma suka yi luhuluhu.

17 Amma ban yi wani aikin kama-karya ba,

Addu’ata ga Allah kuwa ta gaskiya ce.

18 “Duniya, kada ki ɓoye laifofin da aka yi mini!

Kada ki yi shiru da roƙon da nake yi na neman adalci!

19 Akwai wani a Sama

Wanda zai tsaya mini ya goyi bayana.

20 Ina so Allah ya ga hawayena,

Ya kuma ji addu’ata.

21 “Ina so wanda zai yi roƙo ga Allah domina,

Kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.

22 Yanzu shekaruna wucewa suke yi,

Ina bin hanyar da ba a komawa.”

Categories
AYU

AYU 17

1 “Ƙarshen raina ya gabato, da ƙyar nake numfashi,

Ba abin da ya rage mini sai kabari.

2 Na lura da yadda mutane suke yi mini mummunar ba’a.

3 Ni amintacce ne, ya Allah, ka yarda da maganata.

Ba wanda zai goyi bayan abin da nake faɗa.

4 Ka baƙantar da hankalinsu, ya Allah,

Kada ka bar su su yi mini duban wulakanci yanzu.

5 A karin maganar mutanen dā an ce,

‘Kowa ya ci amanar abokinsa saboda kuɗi,

‘Ya’yansa sā sha wahala!’

6 Yanzu kuwa sun mai da wannan karin magana a kaina.

Da mutane suka ji,

Suka zo suka yi ta tofa mini yau a fuska.

7 Baƙin cikina ya kusa makantar da ni,

Hannuwana da ƙafafuna sun rame,

sun zama kamar kyauro.

8 Duk waɗanda suka zaci su adalai ne sun razana.

Dukansu sun kāshe ni, cewa ni ba mai tsoron Allah ba ne.

9 Har su ma da suke cewa su mutanen kirki ne

Suna ƙara tabbatarwa ba su yi kuskure ba.

10 Amma da a ce dukansu za su zo su tsaya a gabana,

Da ba zan sami mai hikima ko ɗaya daga cikinsu ba.

11 “Kwanakina sun ƙare, shirye-shiryena sun kāsa,

Ba ni da sauran sa zuciya.

12 Amma abokaina sun ce dare shi ne hasken rana,

Sun kuma ce haske yana kusa,

Ko da yake ina cikin duhu.

13 Ba ni da sauran sa zuciya,

Gidana yana lahira,

Inda zan kwanta in yi ta barci cikin duhu.

14 Zan ce kabari shi ne mahaifina,

Tsutsotsin da suke cinye ni su ne mahaifiyata, da ‘yan’uwana mata.

15 Ina ne zan sa zuciyata?

Wane ne ya ga inda zan sa ta?

16 Akwai wanda ya yi shiri a binne shi tare da ni,

Mu tafi tare da shi zuwa lahira?”

Categories
AYU

AYU 18

Bildad Ya Bayyana Abin da Za a Yi wa Mugun Mutum

1 Bildad ya amsa.

2 “Ayuba, mutane kamarka sun taɓa yin shiru?

Da ka yi ƙoƙari ka kasa kunne da mun yi magana da kai.

3 Me ya sa kake tsammani mu dakikai ne kamar shanu?

4 Cutar kanka kake yi saboda fushin da kake ji.

Duniya za ta ƙare ne sabili da kai?

Za a kawar da duwatsu sabili da kai?

5 “Za a kashe hasken mugun mutum,

Harshen wutarsa ba zai ƙara ci ba.

6 Fitilar da take cikin alfarwarsa ba za ta ba da haske ba.

7 A dā gagau yake tafiya, amma yanzu ɗingishi yake yi,

Shawararsa ta kāshe shi.

8 Yana tafiya, sai ya fāɗa cikin tarko.

Tarkon ya kama ƙafafunsa.

9 Tarko ya kama diddigensa ya riƙe shi,

10 An binne masa tarko a ƙasa,

An kafa masa tarko a hanyarsa.

11 “Kewaye da shi duka razana tana jiransa,

Duk inda ya nufa tana biye da shi,

12 Dā attajiri ne, amma yanzu ya talauce,

Kusa da shi bala’i na tsaye yana jiransa.

13 Mummunan ciwo ya bazu ko’ina a jikinsa,

Yana sa hannuwansa da ƙafafunsa su ruɓe,

14 Dā yana zaune lafiya,

Sai razana ta tatike shi,

Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa.

15 Yanzu kowa zai iya zama a alfarwarsa,

Bayan da an karkashe ƙwayoyin cuta da farar wuta.

16 Saiwoyinsa da rassansa suka yi yaushi suka bushe.

17 Sunansa ya ƙare a gida da a jeji,

Ba wanda yake ƙara tunawa da shi.

18 Za a kore shi daga ƙasar masu rai,

Za a kore shi daga haske zuwa duhu.

19 Ba shi da zuriya, da sauran waɗanda suka ragu da rai.

20 Daga gabas zuwa yamma, duk wanda ya ji labarin ƙaddarar da ta same shi,

Zai yi makyarkyata, ya yi rawar jiki don tsoro.

21 Wannan ita ce ƙaddarar mugaye,

Wannan ita ce ƙaddarar mutane waɗanda ba su damu da kome na Allah ba.”

Categories
AYU

AYU 19

Bangaskiyar Ayuba Ta Sa Allah Zai Goyi Bayansa

1 Ayuba ya amsa.

2 “Me ya sa kuke azabta ni da maganganu?

3 A kowane lokaci kuna wulakanta ni,

Ba kwa jin kunya yadda kuke zagina.

4 Da a ce ma na aikata abin da yake ba daidai ba ne,

Da me ya cuce ku?

5 Tsammani kuke kun fi ni ne,

Kuna ɗauka cewa wahalar da nake sha

Ta tabbatar ni mai laifi ne.

6 Ba ku iya ganin abin da Allah ya yi mini,

Ya kafa tarko don ya kama ni.

7 Na ce ban yarda da kama-karyarsa ba,

Amma ba wanda ya kasa kunne.

Na nema a aikata gaskiya, amma sam, babu.

8 Allah ya rufe hanya, na kasa wucewa,

Ya rufe hanyata da duhu,

9 Gama ya kwashe dukiyata duka,

Ya ɓata mini suna.

10 Ya mammangare ni,

Ya tumɓuke sa zuciyata,

Ya bar ni in yi yaushi, in mutu.

11 Allah ya zaburo mini da fushi,

Ya maishe ni kamar mafi mugunta daga cikin maƙiyansa.

12 Ya aiko da rundunar sojansa don ta fāɗa mini,

Suka haƙa ramummuka kewaye da alfarwata inda za su yi kwanto.

13 “’Yan’uwana sun yashe ni,

Na zama baƙo ga idon sanina.

14 Dangina da abokaina sun tafi.

15 Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni.

Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa.

16 Sa’ad da na kira barana, ba ya amsawa,

Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni.

17 Har matata ma ba ta iya jurewa da ɗoyin numfashina,

‘Yan’uwana maza kuwa ba su ko zuwa kusa da ni.

18 ‘Yan yara sukan raina ni su yi mini dariya sa’ad da suka gan ni.

19 Aminaina na kusa sukan dube ni, duban ƙyama,

Waɗanda na fi ƙaunarsu duka sun zama maƙiyana.

20 Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi,

Da ƙyar na kuɓuta.

21 Ku abokaina ne! Ku ji tausayina!

Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.

22 Me ya sa kuke ɓata mini rai kamar yadda Allah ya yi?

Azabar da kuka yi mini har yanzu ba ta isa ba?

23 “Da ma a ce wani zai rubuta abin da nake faɗa,

Ya rubuta shi a littafi!

24 Ko kuwa ya zana kalmomina da kurfi a kan dutse,

Ya rubuta su don su tabbata har abada!

25 Amma na sani akwai wani a Samaniya

Wanda a ƙarshe zai zo ya tsaya mini.

26 Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata,

A wannan jiki zan ga Allah.

27 Zan gan shi ido da ido,

Ba kuwa zai zama baƙo a gare ni ba.

“Zuciyata ta karai saboda ku mutane kun ce,

28 ‘Ta ƙaƙa za mu yi masa azaba?’

Kuna neman sanadin da za ku fāɗa mini.

29 Amma yanzu, sai ku ji tsoron takobi,

Ku ji tsoron takobin da yake kawo hasalar Allah a kan zunubi.

Don haka za ku sani akwai wani mai yin shari’a.”

Categories
AYU

AYU 20

Zofar Ya Nuna Rabon Mugu

1 Zofar ya amsa.

2 “Ayuba, ka ɓata mini rai,

Ba zan yi haƙuri ba, sai na ba ka amsa.

3 Abin da ka faɗa raini ne,

Amma na san yadda zan ba ka amsa.

4 “Hakika ka sani tun daga zamanin dā,

Sa’ad da aka fara sa mutum a duniya,

5 Ba wani mugun mutum wanda ya taɓa daɗewa da farin ciki.

6 Mai yiwuwa ne ya ƙasaita, ya zama kamar hasumiya a sararin sama.

Ya ƙasaita har kansa ya taɓa gizagizai.

7 Amma zai shuɗe kamar ƙura.

Waɗanda dā suka san shi,

Za su yi mamaki saboda rashin sanin inda ya tafi.

8 Zai ɓace kamar mafarki, kamar wahayi da dad dare,

Ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.

9 Ba za a ƙara ganinsa a wurin zamansa ba.

10 Tilas ‘ya’yansa maza su biya zambar da ya yi wa matalauta,

Tilas hannuwansa su biya dukiyar da ya ƙwace.

11 Ko da yake gagau yake, ma’aikaci ne kuma sa’ad da yake yaro,

Duk da haka ba da jimawa ba, zai zama ƙura.

12-13 Ɗanɗana mugunta yana da daɗi a gare shi ƙwarai,

Yakan sa wata a bakinsa don ya riƙa jin daɗin tsotsanta.

14 Amma a cikinsa wannan abinci yakan zama da ɗaci,

Ɗacinsa kamar na kowane irin dafi mai ɗaci ne.

15 Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba,

Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa.

16 Abin da mugu ya haɗiye kamar dafi yake,

Yakan kashe shi kamar saran maciji mai mugu dafi.

17 Zai mutu bai ga kogunan man zaitun ba,

Ba kuwa zai ga rafuffukan da suke da yalwar albarka ba.

18 Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa.

Ba dama ya mori dukiyarsa,

19 Saboda zalunci da rashin kula da matalauta,

Da ƙwace gidajen da waɗansu suka gina.

20 “Har abada ba zai kai ga samun abin da yake wahala ba.

21 Sa’ad da ya ci ba zai yi saura ba,

Gama yanzu dukiyarsa ta ƙare.

22 A lokacin da yake gaɓar samunsa,

Baƙin ciki mai nauyin gaske zai ragargaza shi.

23 Bari ya ci duk irin abin da yake so!

Allah zai hukunta shi da hasala da fushi.

24 Lokacin da yake ƙoƙari ya kuɓuta daga takobin baƙin ƙarfe,

Za a harbe shi da bakan tagulla ya fāɗi warwar.

25 Kibiya za ta kafe a jikinsa

Tsininta zai yi ta ɗiɗɗiga da jini,

Razana ta kama zuciyarsa.

26 Aka hallaka dukan abin da ya tattara,

Wutar da ba hannun mutum ya kunna ba

Ta ƙone shi, shi da iyalinsa duka.

27 Samaniya ta bayyana zunubin wannan mutum,

Duniya kuma ta ba da shaida gāba da shi.

28 Dukan dukiyarsa za a hallaka ta a rigyawar fushin Allah.

29 “Wannan ita ce ƙaddarar mugaye,

Wadda Allah ya ƙayyade musu.”

Categories
AYU

AYU 21

Ayuba Ya Yi Magana a kan Wadatar Mugaye

1 Ayuba ya amsa.

2 “Ku kasa kunne ga abin da nake faɗa,

Wannan ita ce ta’aziyyar da nake nema a gare ku.

3 Ku ba ni zarafi in yi magana, sa’an nan in na gama ku amsa in kun ga dama.

4 “Ba da ‘yan adam nake faɗa ba,

Ina da isasshen hanzarin da zai sa in yi fushi.

5 Ku dube ni, ashe, wannan bai isa ya sa ku yi zuru,

Ku firgita, ku yi shiru ba?

6 Sa’ad da na tuna da abin da ya same ni,

Sai jikina ya yi suwu, in yi ta makyarkyata ina rawar jiki.

7 Me ya sa Allah yake barin mugaye

Har su tsufa su kuma yi arziki?

8 ‘Ya’yansu da jikokinsu sukan girma a idonsu.

9 Allah bai taɓa aukar wa gidajensu da bala’i ba,

Ba su taɓa zama a razane ba.

10 Hakika shanunsu suna ta hayayyafa,

Suna haihuwa ba wahala.

11 ‘Ya’yansu suna guje-guje,

Suna tsalle kamar ‘yan raguna,

12 Suna rawa ana kaɗa garaya,

Ana busa sarewa.

13 Suka yi zamansu da salama,

Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba.

14 Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum,

Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.

15 Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah,

Ko a yi addu’a gare shi domin samun wata fa’ida.

16 Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara,

Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.

17 “An taɓa kashe hasken mugun mutum?

Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu?

Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi,

18 Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa?

Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa?

19 “Kukan ce Allah yakan hukunta yaro saboda zunuban mahaifinsa.

A’a! Allah dai yakan hukunta wa masu zunubi.

Ya kuma nuna ya yi haka saboda zunubansu ne.

20 Bari dai a hukunta masu zunubi

Su kuma ga hasalar Allah.

21 Bayan rasuwar mutum,

Ruwansa ne ya sani ko ‘ya’yansa suna jin daɗi?

22 Mutum zai iya koya wa Allah?

Mutum zai iya shara’anta wa Allah Mai Iko Dukka?

23 “Waɗansu mutane sukan yi zamansu ba ciwon kome har ranar mutuwarsu,

Suna cikin farin ciki da jin daɗi,

24 Jikunansu kuwa sun yi ɓulɓul.

25 Waɗansu kuwa ba su taɓa sanin farin ciki ba.

Sukan yi dukan kwanakinsu su mutu da baƙin ciki.

26 Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne,

Tsutsotsi su lulluɓe su duka.

27 “Na san irin tunaninku na hassada,

28 Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu,

Wato mutumin da yake aikata mugunta?’

29 “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba?

Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?

30 A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci,

A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.

31 Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun,

Ko ya mayar masa da martani.

32 Sa’ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi,

A inda ake tsaron kabarinsa,

33 Dubban mutane sukan tafi wurin jana’izarsa,

Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali.

34 “Amma ku, ƙoƙari kuke yi ku ta’azantar da ni da maganganun banza.

Duk abinda kuka faɗa ƙarya ne!”

Categories
AYU

AYU 22

Elifaz ya Zargi Ayuba a kan Aikata Mugunta

1 Elifaz ya yi magana.

2 “Akwai wani mutum, ko mafi hikima,

Wanda zai amfani Allah?

3 Gaskiyar da kake yi za ta amfani Allah?

Ko kuwa abin kirki da kake yi zai taimake shi?

4 Ai, ba don tsoron Allah da kake yi ba ne,

Ya sa wannan tsautawa da jarrabawa suka same ka.

5 Ko kusa ba haka ba ne,

Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne.

Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata.

6 Don ka sa ɗan’uwanka ya biya ka bashin da kake binsa,

Ka ƙwace tufafinsa, ka bar shi huntu.

7 Ka hana wa waɗanda suke ji ƙishi ruwan sha,

Ka hana waɗanda suke jin yunwa abinci.

8 Ka mori ikonka da matsayinka,

Don ka mallaki dukan ƙasar.

9 Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba,

Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su.

10 Don haka ne yanzu akwai ramummuka ko’ina kewaye da kai,

Tsoro ya kama ka nan da nan.

11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani,

Rigyawa ta sha kanka.

12 “Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba?

Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne.

13 Duk da haka ka ce, ‘Allah bai san kome ba.

Gizagizai sun lulluɓe shi, ƙaƙa zai iya yi mana shari’a?’

14 Kana tsammani gizagizai masu duhu sun hana shi gani,

A lokacin da yake tafiya a kan iyakar da take tsakanin duniya da sararin sama.

15 “Ka ɗauka a ranka ka bi gurbin da mugaye suke bi kullum?

16 Kafin ma su kai ga kwanakinsu,

Sai rigyawa ta shafe su.

17 Su ne mutanen da suka ƙi Allah,

Suka kuwa gaskata ba shi da ikon yi musu kome,

18 Ko da yake Allah ne ya arzuta su.

Ba na iya gane tunanin mugaye.

19 Mutanen kirki suna murna,

Marasa laifi kuma suna dariya

Sa’ad da suka ga ana hukunta mugaye.

20 Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka,

Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu.

21 “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah,

Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka,

In ka yi haka, to, za ka sami albarka.

22 Ka karɓi koyarwar da yake yi,

Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.

23 Hakika sai ka yi tawali’u, ka koma wurin Allah,

Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka.

24 Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau,

Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura.

25 Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka,

Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka.

26 Sa’an nan za ka dogara ga Allah kullayaumin,

Ka kuma tarar shi ne asalin farin cikinka.

27 Sa’ad da ka yi addu’a zai amsa maka,

Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi.

28 Za ka yi nasara a kowane abu da za ka yi,

Haske kuma zai haskaka hanyarka.

29 Allah yakan ƙasƙantar da mai girmankai,

Yakan ceci mai tawali’u.

30 Zai ceci wanda yake da laifi,

Idan abin da kake yi daidai ne.”

Categories
AYU

AYU 23

Ayuba Yana Marmarin Kai Ƙara Gaban Allah

1 Ayuba ya amsa.

2 “Duk da haka zan yi tawaye in yi wa Allah gunaguni,

In dinga yin nishi.

3 Da ma na san inda zan same shi,

In kuma san yadda zan kai wurinsa,

4 Da zan kai ƙarata a gare shi, in faɗa masa duk muhawarata, in kāre kaina ne.

5 Ina so in san irin amsar da zai mayar mini,

Ina kuma so in san yadda zai amsa mini.

6 Allah kuwa da dukan ƙarfinsa zai yi gāba da ni?

A’a, zai saurara in na yi magana.

7 Ina da aminci, zan faɗa wa Allah ra’ayina,

Zai tabbatar da amincina duka.

8 “Na nemi Allah a gaba, amma ban same shi a can ba,

Ban kuwa same shi a baya ba sa’ad da na neme shi.

9 Allah ya tafi wurin aiki a dama,

Ya kuma tafi hagu, amma har yanzu ban gan shi ba.

10 Duk da haka Allah ya san kowane irin hali da nake ciki.

Idan ya jarraba ni zai tarar ni tsattsarka ne.

11 Da aminci ina bin hanyar da ya zaɓa,

Ban kuwa taɓa kaucewa daga wannan gefe zuwa wancan ba.

12 A kullum ina aikata abin da Allah ya umarta,

Ina bin nufinsa, ba nufin kaina ba.

13 “Bai taɓa sākewa ba. Ba wanda zai iya gāba da shi,

Ko kuma ya hana shi yin abin da yake so ya aikata.

14 Zai tabbatar da abin da ya shirya domina,

Wannan ma ɗaya daga cikin shirye-shiryen da ya yi ne.

15 Don haka in rawar jiki a gabansa saboda tsoro.

16 Allah Mai Iko Dukka ya lalatar da ƙarfin halina.

Allah ne ya tsorata ni,

17 Amma ban damu da damu ba,

Ko da yake duhu ya dunɗe idanuna.”

Categories
AYU

AYU 24

Ayuba Ya Yi Kuka da Yake Allah Bai Kula da Mugunta Ba

1 “Me ya sa Allah bai tsai da ranar da zai yi shari’a ba?

Me ya sa ba ya tsai da ranar adalci ga

Waɗanda suka bauta masa?

2 Mugaye sukan ci iyaka,

Don su ƙara yawan gonarsu.

Sukan saci tumaki su zuba cikin garkunansu.

3 Sukan saci jakunan marayu,

Su kama san gwauruwa,

Su ce sai ta biya basusuwanta.

4 Sukan hana matalauta samun halaliyarsu,

Sukan tilasta wa masu bukata su gudu su ɓuya.

5 Kamar jakunan jeji waɗanda sukan nemi abinci a busasshen jeji,

Haka matalauta suke,

Ba inda za su iya samo wa ‘ya’yansu abinci.

6 Ya zama tilas a gare su su girbe gonakin da ba nasu ba,

Su tattara ‘ya’yan inabi daga gonakin mugaye.

7 Da dare sukan kwanta, ba su da abin rufa,

Ba su da abin da zai hana su jin sanyi.

8 Sukan jiƙe sharkaf da ruwan sama wanda yake kwararowa daga kan duwatsu.

Sun takure a gefen duwatsu neman mafaka.

9 “Mugaye sukan bautar da yara marayu,

Sukan kama ‘ya’ya matalauta a bakin bashin da suke bi.

10 Amma tilas matalauta su fita huntaye, ba sa da abin sutura.

Tilas su girbi alkama suna kuwa jin yunwa.

11 Suna matse mai daga ‘ya’yan zaitun.

Suna kuma matse ruwan inabi daga ‘ya’yan inabi,

Amma su kansu suna fama da ƙishi.

12 Kana jin kukan waɗanda suka yi rauni da

Waɗanda suke baƙin mutuwa a birni,

Amma Allah bai kula da addu’o’insu ba.

13 “Akwai mugaye waɗanda suke ƙin haske,

Ba su fahimce shi ba, suka ƙi bin hanyarsa.

14 Da asuba mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci,

Da dare kuma ya yi fashi.

15 Mazinaci yakan jira sai da magariba,

Sa’an nan ya ɓoye fuskarsa don kada a gane shi.

16 Da dare ɓarayi sukan kutsa kai cikin gidaje,

Amma da rana sukan ɓuya, su guje wa haske.

17 Gama tsananin duhu kamar safiya yake gare su,

Sun saba da razanar duhu.

18 “Rigyawa takan ci mugun mutum,

Ƙasar da ya mallaka kuwa tana ƙarƙashin la’anar Allah.

Ba ya kuma iya zuwa aiki a gonar inabinsa.

19 Kamar dusar ƙanƙara take a lokacin zafi da a lokacin fari,

Haka mai zunubi yakan shuɗe daga ƙasar masu rai.

20 Ba wanda zai tuna da shi,

mahaifiyarsa ma ba za ta lura da shi ba.

Tsutotsi sukan ci shi su hallaka shi sarai.

Za a sare mugunta kamar itace.

21 Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye.

Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba.

22 Allah, da ikonsa, yakan hallaka masu ƙarfi,

Allah yakan aikata, sai mugun mutum ya mutu.

23 Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya,

Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa.

24 Mugun mutum yakan ci nasara ɗan lokaci,

Daga nan sai ya yi yaushi kamar tsiro,

Ya yi yaushi kamar karan dawa da aka yanke.

25 Akwai wanda zai iya cewa, ba haka ba ne?

Akwai wanda zai tabbatar da cewa kalmomina ba gaskiya ba ne?”