Categories
AYU

AYU 25

Bildad Bai Yarda Allah Zai Baratar da Mutum Ba

1 Bildad ya amsa.

2 “Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa,

A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama.

3 Akwai wanda zai iya ƙidaya mala’ikun da suke masa hidima?

Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?

4 Akwai wanda ya isa ya zama adali,

Ko mai tsarki a gaban Allah?

5 Hasken wata ba haske ba ne a gare shi,

Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa.

6 To, mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai.

Me mutum ya daɗa a gaban Allah?”

Categories
AYU

AYU 26

Ayuba Ha Hurta Sarautar Allah

1 Ayuba ya amsa.

2 “Kai ne mai taimakon marar ƙarfi,

Kai ne mai ceton rarrauna!

3 Kai ne kake ba marar hikima shawara,

Kai kake sanar da ilimi mai ma’ana a wadace!

4 Kana tsammani wane ne zai ji maganganunka duka?

Wane ne ya iza ka ka yi irin wannan magana?

5 “Lahira tana rawa,

Mazaunanta suna rawar jiki don tsoro.

6 Lahira tsirara take a gaban Allah,

Haka kuma Halaka take a gaban Allah.

7 Allah ne ya shimfiɗa arewa a sarari kurum,

Ya rataya duniya ba bisa kan kome ba.

8 Allah ne ya cika gizagizai masu duhu da ruwa,

Girgijen kuwa bai kece ba.

9 Ya rufe kursiyinsa, ya shimfiɗa girgije a kansa.

10 Ya shata da’ira a kan fuskar teku,

A kan iyakar da take tsakanin haske da duhu.

11 Ginshiƙan samaniya sun girgiza,

Sun firgita saboda tsautawarsa.

12 Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku,

Da saninsa ya hallaka dodon ruwan nan, wato Rahab.

13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi garau,

Ikonsa ne kuma ya sha zarar macijin nan mai gudu.

14 Amma waɗannan kaɗan ne kawai daga cikin al’amuransa.

Ɗan ƙis kaɗai muke ji a kansa.

Amma wa zai iya fahimtar ikon tsawarsa?”

Categories
AYU

AYU 27

Ayuba Ya Bayyana Rabon Mugaye

1 Ayuba ya amsa.

2 “Na rantse da Allah Mai Iko Dukka,

Wanda ya ƙwace mini halaliyata,

Wanda ya ɓata mini rai.

3 Muddin ina numfashi,

Ruhun Allah kuma yana cikin hancina

4 Bakina ba zai faɗi ƙarya ba,

Harshena kuma ba zai hurta maganganun yaudara ba.

5 Allah ya sawwaƙa in ce kun yi daidai,

Har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.

6 Ina riƙe da adalci kam, ba kuwa zan sake shi ba,

Zuciyata ba ta zarge ko ɗaya daga cikin kwanakin raina ba.

7 “Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum,

Wanda ya tashi gāba da ni ya zama kamar marar adalci.

8 Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah?

Sa’ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa?

9 Allah kuwa zai ji kukansa sa’ad da wahala ta same shi?

10 Ko Mai Iko Dukka zai zama abin farin ciki a gare shi?

Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?

11 “Zan koya muku zancen ikon Allah,

Abin da yake na wajen Mai Iko Dukka ba zan ɓoye ba.

12 Ga shi kuwa, dukanku kun gani da kanku,

Me ya sa kuka zama wawaye?

13 “Wannan shi ne rabon mugaye daga wurin Allah,

Gādo ne kuma wanda azzalumai za su karɓa daga wurin Mai Iko Dukka.

14 Idan ‘ya’yansu sun riɓaɓɓanya za su zama rabon takobi,

Zuriyarsu kuwa ba za su sami isasshen abinci ba.

15 Waɗanda suka tsira, annoba za ta kashe su,

Matansu ba za su yi makokin mutuwarsu ba.

16 Ko da yake sun tsibe azurfa kamar turɓaya,

Sun tara tufafi kamar ƙasa,

17 Za su tara, amma adalai za su sa,

Marasa laifi ne za su raba azurfar.

18 Sun gina gidajensu kamar saƙar gizo-gizo,

Kamar bukkar mai tsaro.

19 Attajirai za su kwanta, amma daga wannan shi ke nan,

Za su buɗe ido su ga dukiyan nan ba ta.

20 Razana za ta auka musu kamar rigyawa.

Da dare iska za ta tafi da su.

21 Iskar gabas za ta fauce su su tafi,

Ta share su ta raba su da wurin zamansu.

22 Za ta murɗe su ba tausayi,

Hakika za su yi ƙoƙari su tsere daga ikonsa,

Sai su yi ƙundumbala.

23 Kowa zai tafa hannu yă yi musu tsaki har su tashi daga wurin da suke.”

Categories
AYU

AYU 28

Samun Hikima Yana da Wuya

1 “Hakika akwai ma’adinai na azurfa,

Da wuraren da ake tace zinariya.

2 Mutane sukan haƙo baƙin ƙarfe daga ƙasa,

Sukan narkar da tagulla daga dutse.

3 Mutane sukan kawar da duhu,

Sukan kuma bincike zuzzurfar iyaka,

Sukan haƙo duwatsun da suke cikin duhu, duhu baƙi ƙirin.

4 Sukan haƙa loto a fadama nesa da mutane,

Sukan kafa abin lilo su yi ta lilo nesa da mutane.

5 “Daga cikin ƙasa ake samun abinci,

Amma a ƙarƙashinta yakan zama kamar wuta.

6 Akwai duwatsu masu daraja cikin duwatsunta,

Akwai zinariya a ƙurarta.

7 Tsuntsu mai cin nama bai san wannan hanya ba.

Shaho ma bai gan ta ba.

8 Namomin jeji ba su taɓa bin hanyar ba,

Ko zaki ma bai taɓa binta ba.

9 “Mutane sun iya sarrafa ƙanƙarar dutse,

Suna kuma iya tumɓuke tushen duwatsu.

10 Sukan haƙa magudanar ruwa cikin duwatsu,

Idanunsu sukan ga kowane abu mai daraja.

11 Sukan datse rafuffuka su hana su gudu,

Su binciko abin da yake ɓoye, ya fito sarari.

12 Amma ina, a ina za a iya samun hikima?

A ina za a samo haziƙanci?

13 Mutane ba su san darajar hikima ba,

Ba a samunta a ƙasar masu rai.

14 Zurfafa sun ce, ‘Ba ta a cikinmu,’

Tekuna kuma sun ce, ‘Ba ta tare da mu.’

15 Ba za a saye ta da zinariya tsantsa ba.

Azurfa ba za ta iya biyan tamaninta ba.

16 Ko zinariyar Ofir, ko onis,

Ko saffir, wato duwatsu masu daraja, ba za su iya biyan tamaninta ba.

17 Ba daidai take da zinariya ko madubi ba,

Ba za a iya musayarta da kayayyakin da aka yi da zinariya tsantsa ba.

18 Kada ma a ko ambaci murjani,

Da duwatsu masu walƙiya.

Gama tamanin hikima ya fi na lu’ulu’ai mafiya daraja duka.

19 Ba za a daidaita tamaninta da na duwatsun tofaz na Habasha ba.

Tamaninta ya fi na zinariya tsantsa.

20 “To, daga ina hikima ta fito?

A wane wuri kuma haziƙanci yake?

21 Ba talikin da ya iya ganinta,

Ko tsuntsun da yake tashi sama.

22 Halaka da Mutuwa sun ce,

‘Da kunnuwanmu mun ji ƙishin-ƙishin a kanta.’

23 “Allah ne kaɗai ya san hanya zuwa gare ta,

Ya san inda hikima take,

24 Saboda yana ganin duniya ɗungum,

Yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sararin sama.

25 Sa’ad da Allah ya sa iska ta hura,

Ya yi wa tekuna iyaka.

26 Sa’ad da ya ba da umarni ga ruwan sama,

Da kuma hanyar da tsawa za ta bi,

27 Shi ya san hikimar, shi ya sanar,

Ya tabbatar da ita, ya bincike ta sarai.

28 “Allah ya ce wa mutane,

‘Duba, tsoron Ubangiji shi ne hikima,

Rabuwa da mugunta kuma, ita ce haziƙanci.’ ”

Categories
AYU

AYU 29

Ayuba Ya Tuno da Farin Cikinsa na Dā

1 Ayuba ya ci gaba da magana.

2 Da ma ina cikin lokacin da ya wuce ne,

Lokacin da Allah yake lura da ni,

3 Sa’ad da fitilarsa take haskaka mini,

Ta wurin haskensa kuma nake tafiya da duhu,

4 Kwanakin da nake gaɓar raina,

Lokacin da ni’imar Allah take kan gidana,

5 Sa’ad da Mai Iko Dukka yake tare da ni,

‘Ya’yana duka kuma suka kewaye ni,

6 Sa’ad da aka wanke ƙafafuna da madara,

Duwatsu kama suna ɓulɓulo mini da rafuffukan mai!

7 A sa’ad da nakan tafi kofar birni,

In shirya wurin zamana a dandali,

8 Da samari sun gan ni, sai su kawar da jiki,

Tsofaffi kuma su miƙe tsaye,

9 Sarakuna sun yi shiru sun kame bakinsu.

10 Manyan mutane sukan yi shiru, harshensu ya liƙe a dasashi.

11 Waɗanda suka ji labarina sukan sa mini albarka,

Waɗanda suka gan ni sukan yi na’am da ni.

12 Domin sa’ad da matalauta suka yi kuka, ni nake cetonsu,

Nakan taimaki marayu waɗanda ba su da mai taimako.

13 Waɗanda suke bakin mutuwa sukan sa mini albarka,

Na taimaki gwaurayen da mazansu suka mutu,

Su raira waƙa don murna.

14 Adalci shi ne suturata,

Gaskiya ita ce rigata da rawanina.

15 Ni ne idon makafi, guragu kuma, ni ne ƙafarsu.

16 Ni mahaifi ne ga matalauta,

Nakan bincika don in warware al’amarin da ya dami baƙi.

17 Nakan karya muƙamuƙin marar adalci,

In sa yă saki ganimar da yă kama.

18 “Da na zaci zan mutu cikin sutura,

Kwanakina kuma su riɓaɓɓanya, su yi yawa kamar yashi,

19 Saiwoyina a shimfiɗe suke cikin ruwa,

Dukan dare raɓa na sauka a kan rassana .

20 Darajata garau take a gare ni,

Bakana kullum sabo yake a hannuna.

21 Mutane sukan kasa kunne su jira, su yi shiru

Sa’ad da nake ba da shawara.

22 Bayan na gama magana ba wanda zai ƙara wata magana.

Maganata takan shige su.

23 Suna jirana kamar yadda ake jiran ruwan sama,

Da baki buɗe, kamar yadda ake jiran ruwan bazara.

24 Nakan yi musu murmushi sa’ad da suka fid da zuciya,

Ba su yi watsi da fara’ata ba.

25 Nakan zaɓar musu hanyar da za su bi,

Ina zaune kamar sarki a tsakanin mayaƙansu,

Kamar mai ta’azantar da masu makoki.”

Categories
AYU

AYU 30

Ayuba Ya Yi Kuka saboda Masifunsa

1 “Amma yanzu waɗanda na girme su, sai ba’a suke mini,

Waɗanda iyayensu maza ba su fi karnukan da suke kiwon garken tumakina ba.

2 Wace riba zan samu ta wurin ƙarfin hannuwansu waɗanda ba su da sauran kuzari?

3 Saboda rashi da matsananciyar yunwa sun rame,

Sai gaigayar ƙasa suke yi da dare, a cikin kufai.

4 Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci,

Sukan ci doyar jeji.

5 Aka kore su daga cikin mutane,

Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo,

6 Sai a kwazazzabai suke zama

Da a ramummuka da kogwannin duwatsu.

7 Suka yi ta kuka a jeji,

Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.

8 Mutane ne marasa hankali marasa suna!

Aka kore su daga ƙasar.

9 “Yanzu na zama abin waƙa gare su,

Abin ba’a kuma a gare su.

10 Suna ƙyamata, guduna suke yi,

Da ganina, sai su tofa mini yau.

11 Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,

Saboda haka sun raba ni da zuriyata,

12 A hannun dama ‘yan tā da zaune tsaye sun taso mini,

Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.

13 Sun datse hanyata,

Sun jawo mini bala’i,

Ba kuwa wanda ya hana su.

14 Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka,

Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi.

15 Sun firgita ni,

Sun kori darajata kamar da iska,

Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.

16 “Yanzu zuciyata ta narke

Kwanakin wahala sun same ni.

17 Da dare ƙasusuwana karkaɗuwa suke,

Azaba tana ta gaigayata ba hutawa.

18 An yi mini kamun kama-karya,

An ci wuyan rigata.

19 Allah ya jefar da ni cikin laka,

Na zama kamar ƙura ko toka,

20 “Na yi kira gare ka, ya Allah, amma ba ka amsa mini ba,

Na yi addu’a kuma, amma ba ka kula da ni ba.

21 Ka zama mugu a gare ni,

Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.

22 Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta,

Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri.

23 Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa,

Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai.

24 “Ashe, wanda yake gab da gagarumar hallaka,

Ba zai miƙa hannu ya roƙi taimako a masifar da yake sha ba?

25 Ashe, ban yi kuka saboda wanda yake shan wahala ba?

Ashe, ban yi ɓacin rai saboda matalauta ba?

26 Amma sa’ad da na sa zuciya ga alheri, sai ga mugunta,

Sa’ad da nake jiran haske, sai ga duhu ya zo.

27 Zuciyata tana tafasa, ba ta kwanciya,

Kwanakin wahala sun auko mini.

28 Na yanƙwane, amma ba yanƙwanewar rana ba,

Na tsaya a gaban taron jama’a, ina roƙon taimako.

29 “Na zama ɗan’uwan dila,

Na kuma zama aminin jiminai.

30 Fatata ta takura, ta zama baƙa,

Ƙasusuwana suna zogi saboda zafi,

31 Saboda haka garayata ta zama ta makoki,

Sarewata kuma ta zama muryar masu kuka.”

Categories
AYU

AYU 31

Ayuba Ya Tabbatar da Mutuncinsa

1 “Na yi alkawari da idanuna,

Me zai sa in ƙyafaci budurwa?

2 Wane rabo zan samu daga wurin Allah a Sama?

Wane gādo kuma zan samu daga wurin Mai Iko Dukka a can samaniya?

3 Yakan aika da masifa da lalacewa

Ga waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba.

4 Allah ya san dukan abin da nake yi,

Yana ƙididdige dukan takawata.

5 “Idan ina tafiya da rashin gaskiya,

Ina hanzari don in aikata yaudara,

6 Bari Allah ya auna ni da ma’aunin da yake daidai,

Zai kuwa san mutuncina.

7 Idan dai na kauce daga hanya,

Ko kuwa zuciyata ta bi sha’awar idanuna,

Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna,

8 To, bari in shuka, wani ya ci amfanin,

Bari a tumɓuke amfanin gonata.

9 “Idan na yi sha’awar wata mace,

Har na je na laɓe a ƙofar maƙwabcina,

10 To, bari matata ta yi wa wani abinci,

Bari waɗansu su kwana da ita.

11 Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai,

Wanda alƙalai ne za su hukunta.

12 Za ta zama wuta mai ci har ta hallaka,

Za ta cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.

13 “Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba,

Sa’ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,

14 To, wace amsa zan ba Allah sa’ad da ya tashi don ya hukuntar?

Me zan iya faɗa sa’ad da Allah ya zo yi mini shari’a?

15 Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa,

Ba shi ne ya halicce su ba?

Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?

16 “Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba,

Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba,

17 Ko kuwa in bar marayu da yunwa sa’ad da nake cin abincina,

18 Tun suna yara nake goyonsu,

Ina lura da su kamar ‘ya’yan cikina.

19 “Amma idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura,

Ko wani matalauci marar abin rufa,

20 Idan a zuciyarsa bai sa mini albarka ba,

Ko bai ji ɗumi da ulun tumakina ba,

21 Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya,

Don na ga ina da kafar kuɓuta,

22 To, ka sa kafaɗuna su ɓaɓɓalle daga inda suke.

Ka kakkarya gwiwoyin hannuna.

23 Gama bala’i daga wurin Allah ya razanar da ni,

Saboda ɗaukakarsa ba zan iya yin kome ba.

24 “Idan na ce ga zinariya na dogara, ko zinariya tsantsa ita ce jigona,

25 Idan kuma saboda yawan dukiyata nake fariya,

Ko saboda abin da na mallaka ne,

26 Idan ga hasken rana nake zuba ido,

Ko ga hasken farin wata ne,

27 Zuciyata ta jarabtu ke nan a asirce,

Ni da kaina ina sumbatar hannuna,

28 Wannan ma zai zama laifi ne wanda alƙalai za su hukunta,

Gama na zama munafukin Allah Mai Iko Dukka ke nan.

29 “Idan na yi murna saboda wahala ta sami maƙiyana,

Ko na yi fariya saboda mugun abu ya same shi,

30 Ban yi zunubi da bakina ba,

Ban nemi ran wani ta wurin la’anta shi ba.

31 Ko mutanen da suke cikin alfarwata ba wanda zai ce,

Ga wani can da bai ƙoshi da nama ba.

32 Ban bar baƙi su kwana a titi ba,

Ƙofar gidana a buɗe take ga matafiya.

33 Idan na ɓoye laifofina a zuciyata,

34 Ko na tsaya shiru saboda tsoron taron jama’a,

Saboda kuma baƙar maganar mutane ta razanar da ni,

35 Da a ce ina da wanda zai kasa kunne gare ni,

Da sai in sa hannu a kan abin da na faɗa,

Allah kuwa Mai Iko Dukka ya amsa mini.

“Da ƙarar da maƙiyana suke kai ni, a rubuce ne,

36 Hakika da sai in ɗauke ta a kafaɗata,

In kuwa naɗa ta a kaina kamar rawani.

37 Da na ba Allah dukan lissafin abin da na taɓa yi,

In tinƙare shi kamar ni basarauce ne.

38 “Idan ƙasata tana kuka da ni,

Ita da kunyoyinta,

39 Ko na ci amfaninta ban biya ba,

Ko na yi sanadin mutuwar mai ita,

40 Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama,

Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha’ir.”

Maganar Ayuba ta ƙare.

Categories
AYU

AYU 32

Jawaban Elihu

1 Mutanen nan uku sun daina ba Ayuba amsa, saboda yana ganin kansa adali ne.

2 Sai Elihu, ɗan Barakel, mutumin Buz, daga cikin iyalin Arama, ya husata, yana fushi da Ayuba saboda ya baratar da kansa, bai bari Allah ya baratar da shi ba.

3 Yana kuma fushi da abokan nan uku na Ayuba, domin sun rasa amsar da za su ba Ayuba, ko da yake sun hurta Ayuba ne yake da laifi.

4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.

5 Sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da wata amsa da za su ba Ayuba, sai ya yi fushi.

6 Elihu ɗan Barakel, mutumin Buz, ya fara magana, ya ce,

“A shekaru dai ni yaro ne ku kuwa manya ne,

Don haka ina jin nauyi,

Ina kuma jin tsoro in faɗa muku ra’ayina.

7 Na ce wa kaina, ‘Ya kamata kwanaki su yi magana,

Yawan shekaru kuma su koyar da hikima.’

8 Amma Ruhun Allah Mai Iko Dukka ne wanda yake cikin mutum,

Yakan ba mutane basira.

9 Ba tsofaffi ne masu wayo ba,

Ba kuma masu yawan shekaru kaɗai yake gane abin da yake daidai ba.

10 Don haka na ce ku kasa kunne gare ni,

Bari in faɗa muku nawa ra’ayi.

11 “Ga shi, na dakata na ji maganarku,

Na kasa kunne ga maganarku ta hikima,

Tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.

12 Na kasa kunne gare ku sosai,

Amma ko ɗaya ba wanda ya kā da Ayuba.

Ba kuma wanda ya ba shi amsar tambayarsa.

13 Ku lura kada ku ce kuna da hikima,

Allah ne kaɗai yake da iko ya kā da shi, ba mutum ba.

14 Ba da ni Ayuba yake magana ba,

Saboda haka ba zan amsa masa da irin amsarku ba.

15 “Abin ya cika musu ciki, ba su ƙara amsawa ba,

Wato ba su da ta cewa.

16 Ni kuma sai in tsaya don ba su ce kome ba?

Sun tsaya kurum, don ba su da ta cewa?

17 A’a, ni kuma zan ba da tawa amsa,

In kuma faɗi ra’ayina.

18 Cike nake da magana,

Ruhun da ka cikina ya iza ni.

19 Ga zuciya tana kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska,

Kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda take shirin fashewa.

20 Tilas in yi magana don in huce,

Dole in ba da amsa.

21 Ba zan yi wa kowa son zuciya ba,

Ko kuma in yi wa wani fādanci.

22 Gama ni ban iya fādanci ba,

Idan na yi haka kuwa

Mahaliccina zai kashe ni nan da nan.”

Categories
AYU

AYU 33

Elihu Ya Tsauta wa Ayuba

1 “Amma yanzu, kai Ayuba, ka yarda ka ji maganata,

Ka kasa kunne ga dukan abin da zan faɗa.

2 Ga shi, na buɗe baki in yi magana.

3 Maganar da zan hurta ainihin gaskiyar da take a zuciyata ce,

Abin da zan faɗa kuma dahir ne.

4 Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai.

5 “Ka amsa mini, in ka iya,

Ka shirya abubuwan da za ka faɗa mini, ka yi tsaye a kansu.

6 Duba, ni da kai ɗaya muke a wajen Allah,

Dukanmu biyu kuma daga yumɓu aka siffata mu.

7 Don haka kada ka razana saboda ni,

Abin da zan faɗa maka, ba abin da zai fi ƙarfinka.

8 “Hakika na ji maganar da ka yi,

Na kuwa ji amon maganganunka,

9 Ka ce kai tsattsarka ne, ba ka da laifi,

Kai tsabtatacce ne, ba ka da wata ƙazanta.

10 Ka ce Allah ya zarge ka ya ɗauke ka tankar maƙiyansa,

11 Ya saka ka a turu,

Yana duban dukan al’amuranka.

12 “Amma a kan wannan, Ayuba, ka yi kuskure, zan ba ka amsa,

Gama Allah ya fi kowane mutum girma.

13 Me ya sa kake yi wa Allah gunaguni,

Cewa ba ya karɓar maganarka ko ɗaya?

14 Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne,

I, har sau biyu, duk da haka mutum ba ya lura.

15 Yakan sanar a mafarkai ko a wahayi

Sa’ad da barci mai nauyi ya ɗauke su,

A sa’ad da suke barci a gadajensu.

16 Yakan buɗe kunnuwan mutane,

Ya tsorata su da faɗakarwarsa,

17 Domin ya kawar da su daga aikin da suke yi,

Ya kuma kawar musu da girmankai.

18 Yakan hana su zuwa kabari,

Ya hana ransu halaka da takobi.

19 “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa,

Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,

20 Ransa yana ƙyamar abinci,

Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa.

21 Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje.

22 Yana gab da shiga kabari,

Ransa yana hannun mala’ikun mutuwa.

23 “Da a ce akwai wani mala’ika mai sulhuntawa a tsakani,

Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum,

24 Mala’ikan da zai yi masa alheri ya ce,

‘Ka cece shi daga gangarawa zuwa cikin kabari,

Na sami abin da zai fanshe shi!’

25 Naman jikinsa zai koma kamar na saurayi,

Zai komo kamar lokacin da yake gaɓar ƙarfinsa.

26 Sa’an nan ne mutum zai yi addu’a ga Allah, ya karɓe shi,

Ya zo gabansa da murna,

Allah zai komar wa mutum da adalcinsa.

27 Zai raira waƙa a gaban jama’a, ya ce, ‘Na yi zunubi. Ban yi daidai ba,

Amma ba a sa ni in biya ba.

28 Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari,

Raina kuwa zai ga haske.’

29 “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,

30 Don ya komo da ran mutum daga kabari,

Domin a haskaka shi da hasken rai.

31 “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne,

Ga abin da nake faɗa,

Ka yi shiru, zan yi magana.

32 Amma idan kana da ta cewa, to, amsa,

Yi magana, gama ina so in kuɓutar da kai.

33 In kuwa ba haka ba, sai ka yi shiru,

Ka kasa kunne gare ni,

Zan kuwa koya maka hikima.”

Categories
AYU

AYU 34

Elihu ya ga Allah ya yi Daidai

1 Elihu ya ci gaba.

2 “Ku mutane masu hikima, ku ji maganata,

Ku kasa kunne ga abin da zan faɗa, ku masana.

3 Kunne yake rarrabewa da magana,

Kamar yadda harshe yake rarrabewa da ɗanɗanar abinci.

4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai,

Bari kuma mu daidaita abin da yake mai kyau tsakanin junanmu.

5 Gama Ayuba ya ce, ‘Ni marar laifi ne,

Amma Allah ya ƙwace mini halaliyata.

6 Duk da rashin laifina an ɗauke ni a maƙaryaci,

Raunina ba ya warkuwa ko da yake ba ni da laifin kome.’

7 “Wane irin mutum ne kai, Ayuba,

Da kake shan raini kamar yadda kake shan ruwa,

8 Wanda yake cuɗanya da ƙungiyar masu aikata laifi,

Kana yawo tare da mugaye?

9 Gama ka ce, ‘Bai amfana wa mutum kome ba

Ya yi murna da Allah.’

10 “Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai,

Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne,

A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure,

11 Gama bisa ga aikin mutum yake sāka masa,

Yana sa aniyarsa ta bi shi.

12 Gaskiya ce, Allah ba zai aikata mugunta ba,

Mai Iko Dukka ba zai kauce wa adalci ba.

13 Wa ya shugabantar da shi a kan duniya?

Wa ya mallakar masa da duniya duka?

14 Da zai amshe ruhu da numfashin da ya hura wa mutum,

15 Da duk mai rai ya halaka,

Mutum kuma ya koma ƙura.

16 “Idan kai haziƙi ne, to, ji wannan,

Kasa kunne ga abin da zan faɗa.

17 Da Allah maƙiyin adalci ne, da ya yi mallaka?

Ka iya sa wa Adali, Mai Iko Dukka laifi?

18 Ka iya sa wa Allah laifi,

Shi da ya ce, ‘Sarki marar amfani ne,

Hakimai kuma mugaye’?

19 Ba ya nuna sonkai ga sarakuna,

Ko kuma ya fi kulawa da attajira fiye da matalauta,

Gama shi ya halicce su duka.

20 Sukan mutu nan da nan,

Da tsakar dare manya da ƙanana sukan shuɗe farat ɗaya,

An kawar da su ba da hannun mutum ba.

21 “Gama yana ganin al’amuran mutum,

Yana kuma ganin dukan manufarsa.

22 Ba wani duhu, ko duhu baƙi ƙirin

Inda masu aikata mugunta za su ɓuya.

23 Ba ajiyayyen lokacin da ya ajiye wa kowane mutum

Da zai je shari’a a gaban Allah.

24 Yakan ragargaza ƙarfafa ba tare da wani bincike ba,

Ya sa waɗansu a madadinsu.

25 Saboda sanin ayyukansu,

Yakan kaɓantar da su da dare ya ragargaza su,

26 Yakan buge su a gaban mutane saboda muguntarsu,

27 Don sun daina binsa, ba su kula da ko ɗaya

Daga cikin umarnansa ba.

28 Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah,

Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa.

29 Idan Allah zai yi shiru, da wa zai sa wa wani laifi?

Idan ya ɓoye fuskarsa, wa zai iya ganinsa,

Ko aka yi wa al’umma ko ga mutum?

30 Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba,

Don kada ya tura jama’a cikin tarko.

31 “Akwai wanda zai ce wa Allah, ‘Ni horarre ne,

Ba zan ƙara yin laifi ba?

32 Ka koya mini abin da ban sani ba,

Idan na yi laifi, ba zan ƙara yi ba.’

33 Zai kuɓutar domin ya gamshe ka saboda ka ƙi yarda?

Tilas kai za ka zaɓa, ba ni ba,

Saboda haka sai ka hurta abin da ka sani.

34 “Haziƙan mutane da mutum mai hikima da suka ji ni za su ce,

35 ‘Ayuba yakan yi magana ne ba tare da sanin abin da yake yi ba,

Maganarsa ba ta mai hangen nesa ba ce.

36 Da ma a gwada Ayuba har ƙarshe,

Saboda amsar da yake bayarwa ta mugaye.

37 Gama ya ƙara zunubinsa da tayarwa,

Yana tafa hannunsa a tsakaninmu,

Yana yawaita maganganunsa gāba da Allah.’ ”