Categories
ZAB

ZAB 103

Yabon Ƙaunar Allah

1 Ka yabi Ubangiji, ya raina!

Ka yabi sunansa mai tsarki!

2 Ka yabi Ubangiji, ya raina,

Kada ka manta da yawan alherinsa.

3 Ya gafarta dukan zunubaina,

Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.

4 Ya cece ni daga kabari,

Ya sa mini albarka da ƙauna da jinƙai.

5 Ya cika raina da kyawawan abubuwa,

Don in zauna gagau,

Ƙaƙƙarfa kamar gaggafa.

6 Ubangiji yakan yi wa waɗanda ake zalunta shari’a ta gaskiya.

Yakan ba su hakkinsu.

7 Ya faɗa wa Musa shirye-shiryensa.

Ya yardar wa jama’ar Isra’ila su ga manyan ayyukansa.

8 Ubangiji mai jinƙai ne, mai ƙauna ne kuma,

Mai jinƙirin fushi ne, cike yake da madawwamiyar ƙauna.

9 Ba zai yi ta tsautawa kullum ba,

Ba zai yi ta jin haushi har abada ba.

10 Yakan yi mana rangwame sa’ad da yake hukunta mu,

Ko sa’ad da yake sāka mana saboda zunubanmu da laifofinmu.

11 Kamar yadda nisan sararin sama yake bisa kan duniya,

Haka kuma girman ƙaunarsa yake ga waɗanda suke tsoronsa.

12 Kamar yadda gabas take nesa da yamma,

Haka nan ne ya nisantar da zunubanmu daga gare mu.

13 Kamar yadda uba yake yi wa ‘ya’yansa alheri,

Haka nan kuwa Ubangiji yake yi wa masu tsoronsa alheri.

14 Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi,

Yakan tuna, da ƙura aka yi mu.

15 Mutum fa, ransa kamar ciyawa ne,

Yakan yi girma, ya yi yabanya kamar furen jeji.

16 Sa’an nan iska ta bi ta kansa, yakan ɓace,

Ba mai ƙara ganinsa.

17 Amma ƙaunar Ubangiji ga waɗanda suke girmama shi har abada ce.

Alherinsa kuwa tabbatacce ne har dukan zamanai,

18 Ga waɗanda suke riƙe da alkawarinsa da gaskiya,

Waɗanda suke biyayya da umarnansa da aminci.

19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a Sama,

Shi yake sarautar duka.

20 Ku yabi Ubangiji, ku ƙarfafa, ku manyan mala’iku,

Ku da kuke biyayya da umarnansa,

Kuna kasa kunne ga maganarsa!

21 Ku yabi Ubangiji, ku dukan ikokin da suke a Sama,

Ku yabi Ubangiji, ku bayinsa masu aikata abin da yake so!

22 Ku yabi Ubangiji, dukanku da kuke halittattunsa,

A duk inda yake mulki!

Ka yabi Ubangiji, ya raina!

Categories
ZAB

ZAB 104

Ubangiji yana Kula da Halittarsa

1 Ka yabi Ubangiji, ya raina!

Ya Ubangiji Allahna, mai girma ne kai!

Kana saye da ɗaukaka da daraja,

2 Ka yi lulluɓi da haske.

Ka shimfiɗa sammai kamar alfarwa.

3 Ka gina wurin zamanka a bisa kan ruwan da yake sama.

Gajimare ne karusanka,

A bisa kan fikafikan iska kake tafiya.

4 Iska ce jakadanka,

Walƙiya kuwa ita ce baiwarka.

5 Ka sa duniya ta kahu sosai a bisa harsashin gininta,

Ba kuwa za a iya kawar da ita ba har abada.

6 Ka sa teku a bisanta kamar alkyabba,

Ruwan kuwa ya rufe manyan duwatsu.

7 Amma sa’ad da ka tsauta wa ruwa,

Sai ya tsere,

Sa’ad da ya ji ka daka tsawa,

Sai ya sheƙa a guje.

8 Ya haura kan duwatsu, ya gangara cikin kwaruruka,

Wurin da ka shirya masa.

9 Ka ƙayyade masa kan iyaka da ba zai taɓa ƙetarewa ba,

Don kada ya sāke rufe duniya.

10 Ka sa maɓuɓɓugai suka gudano cikin kwaruruka,

Ka sa ruwa yana gudu tsakanin tuddai.

11 Su ne suke shayar da namomin jeji,

Jakunan jeji kuma, a nan sukan kashe ƙishinsu.

12 A itatuwan da suke kusa da wurin,

Tsuntsaye suke yin sheƙunansu suna ta raira waƙa.

13 Daga sararin sama kakan aiko da ruwa bisa duwatsu,

Ƙasa kuwa takan cika da albarkunka.

14 Kakan sa ciyawa ta yi girma don shanu,

Tsire-tsire kuma don amfanin mutum,

Saboda haka mutum zai iya shuka amfanin gona,

15 Don ya yi ruwan inabin da zai sa shi farin ciki,

Ya sami man zaitun wanda zai sa shi fara’a,

Da abincin da zai ba shi ƙarfi.

16 Itatuwan al’ul na Lebanon sukan sami isasshen ruwan sama,

Itatuwa ne na Ubangiji kansa, waɗanda shi ya dasa.

17 A nan tsuntsaye suke yin sheƙunansu,

A bisa itatuwan fir shamuwa suke yin sheƙa.

18 A kan duwatsu masu tsayi awakin jeji suke zama,

Remaye sukan ɓuya a kan tsaunukan bakin teku.

19 Ka halicci wata don ƙididdigar lokatai,

Rana kuwa ta san daidai lokacin fāɗuwarta.

20 Ka halicci dare, da duhu inda namomin jeji suke fitowa.

21 Sagarun zakoki sukan yi ruri sa’ad da suke farauta,

Suna neman abincin da Allah zai ba su.

22 Sa’ad da rana ta fito,

Sai su koma su kwanta a kogwanninsu.

23 Sa’an nan mutane sukan fita su yi aikinsu,

Su yi ta aiki har maraice ya yi.

24 Ya Ubangiji, ka halicci abubuwa masu yawa!

Da hikima ƙwarai ka halicce su!

Duniya cike take da talikanka.

25 Ga babbar teku mai fāɗi,

Inda talikai da ba su ƙidayuwa suke zaune,

Manya da ƙanana gaba ɗaya.

26 Jiragen ruwa suna tafiya a kansa,

Dodon ruwa wanda ka halitta, a ciki yake wasa.

27 Dukansu a gare ka suke dogara,

Don ka ba su abinci sa’ad da suke bukata.

28 Ka ba su, sun ci,

Ka tanada musu abinci, sun ƙoshi.

29 Sa’ad da ka rabu da su sukan tsorata,

In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu,

Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.

30 Amma sa’ad da ka hura musu numfashi, sai su rayu,

Kakan sabunta fuskar duniya.

31 Da ma darajar Ubangiji ta dawwama har abada!

Da ma Ubangiji ya yi farin ciki da abin da ya halitta!

32 Ya dubi duniya, sai ta girgiza,

Ya taɓa duwatsu, sai suka tuɗaɗo da hayaƙi.

33 Zan raira waƙa ga Ubangiji dukan raina,

Zan raira yabbai ga Allah muddin raina.

34 Da ma ya ji daɗin waƙata,

Saboda yakan sa ni in yi murna.

35 Da ma a hallakar da masu zunubi daga duniya,

Da ma mugaye su ƙare ƙaƙaf!

Ka yabi Ubangiji, ya raina!

Ka yabi Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 105

Allah da Jama’arsa

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa,

Ku sanar wa sauran al’umma abubuwan da ya yi!

2 Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi,

Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!

3 Ku yi murna saboda mu nasa ne,

Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

4 Ku je wurin Ubangiji neman taimako,

Ku tsaya a gabansa koyaushe.

5-6 Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,

Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu,

Ku tuna da mu’ujizansa masu girma, masu banmamaki,

Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

7 Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,

Umarnansa domin dukan duniya ne.

8 Zai cika alkawarinsa har abada,

Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

9 Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim,

Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

10 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra’ila,

Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa’ad da ya ce,

11 “Zan ba ka ƙasar Kan’ana,

Za ta zama mallakarka.”

12 Jama’ar Ubangiji kima ne,

Baƙi ne kuwa a ƙasar.

13 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,

Daga wannan mulki zuwa wancan,

14 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,

Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

15 Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu,

Kada ku cuci annabawana!”

16 Sa’ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu,

Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,

17 Sai ya aika da Yusufu ya riga su zuwa,

Shi wanda aka sayar da shi kamar bawa.

18 Ƙafafunsa suka yi rauni saboda an ɗaure su da sarƙa,

Aka kuma sa wa wuyansa ƙuƙumi na baƙin ƙarfe,

19 Har kafin faɗar da ya yi, ta cika.

Maganar Ubangiji ta tabbatar da gaskiyar abin da ya faɗa.

20 Sa’an nan Sarkin Masar ya sake shi,

Mai mulkin dukan sauran al’umma ya ‘yantar da shi.

21 Ya sa shi ya lura da mulkinsa,

Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.

22 Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma’aikatan hukuma.

Ya ba shi ikon umartar mashawartansa.

23 Sa’an nan Yakubu ya tafi Masar,

Ya zauna a ƙasar.

24 Ubangiji ya sa jama’arsa suka hayayyafa da yawa,

Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.

25 Ya sa Masarawa suka ƙi jinin jama’arsa,

Suka yi wa bayinsa munafunci.

26 Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa.

27 Suka aikata manya manyan ayyuka na Allah,

Suka kuma yi ayyukan al’ajabi a Masar.

28 Ya aika da duhu a bisa ƙasar.

Musa da Haruna ba su tayar wa umarnansa ba.

29 Ya mai da ruwan kogunansu su zama jini,

Ya karkashe kifayensu duka.

30 Ƙasarsu ta cika da kwaɗi,

Har a fādar sarki.

31 Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwari

Suka cika dukan ƙasar.

32 Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsu

Maimakon ruwan sama.

33 Ya lalatar da ‘ya’yan inabinsu da itatuwan ɓaurensu,

Ya kakkarya itatuwansu.

34 Ya ba da umarni, sai fāri suka zo,

Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa.

35 Suka cinye dukan tsire-tsire na ƙasa.

Suka cinye dukan amfanin gonaki.

36 Ya karkashe dukan ‘ya’yan fari maza

Na dukan iyalan Masarawa.

37 Sa’an nan ya bi da Isra’ilawa, suka fita,

Suka kwashi azurfa da zinariya,

Dukansu kuma ƙarfafa ne lafiyayyu.

38 Masarawa suka yi murna da fitarsu,

Gama sun tsoratar da su.

39 Ya sa girgije ya yi wa jama’arsa inuwa,

Da dare kuma wuta ta haskaka musu.

40 Suka roƙa, sai aka ba su makware,

Ya ba su abinci daga sama da za su ci su ƙoshi.

41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya bulbulo,

Yana gudu cikin hamada kamar kogi.

42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki

Wanda ya yi wa bawansa Ibrahim.

43 Haka kuwa ya bi da jama’arsa, suka fita suna raira waƙa,

Ya bi da zaɓaɓɓun jama’arsa, suna sowa ta farin ciki.

44 Ya ba su ƙasar baƙi,

Ya sa su gāje gonakinsu,

45 Don jama’arsa su yi biyayya da dokokinsa,

Su kuma kiyaye umarninsa.

Ku yabi Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 106

Tawayen Isra’ila

1 Ku yabi Ubangiji!

Ku yi wa Ubangiji godiya, gama nagari ne shi,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

2 Wa zai iya faɗar dukan manya manyan ayyuka da ya yi?

Wa zai iya yi masa isasshen yabo?

3 Masu farin ciki ne waɗanda suke biyayya da umarnansa,

Waɗanda kullayaumi suke aikata abin da yake daidai!

4 Ka tuna da ni sa’ad da za ka taimaki jama’arka, ya Ubangiji!

Ka sa ni cikinsu, sa’ad da za ka cece su.

5 Ka yardar mini in ga wadatar jama’arka,

In yi tarayya da jama’arka da farin cikinsu,

In yi farin ciki tare da waɗanda suke murna ta fāriya domin su naka ne.

6 Mun yi zunubi yadda kakanninmu suka yi,

Mugaye ne, mun aikata mugunta.

7 Kakanninmu a Masar

Ba su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba,

Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu,

Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya.

8 Amma duk da haka ya cece su, kamar yadda ya alkawarta,

Domin ya nuna ikonsa mai girma.

9 Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe,

Har ya bi da jama’arsa su haye

Kamar a bisa busasshiyar ƙasa.

10 Ya cece su daga maƙiyansu,

Ya ƙwato su daga wurin abokan gābansu.

11 Ruwa ya cinye maƙiyansu,

Ba wanda ya tsira.

12 Sa’an nan jama’arsa suka gaskata alkawarinsa,

Suka raira yabo gare shi.

13 Amma nan da nan, suka manta da abin da ya yi,

Suka aikata, ba su jira shawararsa ba.

14 Suka cika da sha’awa cikin hamada,

Suka jarraba Allah,

15 Sai ya ba su abin da suka roƙa,

Amma ya aukar musu da muguwar cuta.

16 Can cikin hamada suka ji kishin Musa

Da Haruna, bayin Ubangiji, tsarkaka,

17 Sai ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan,

Ta binne Abiram da iyalinsa.

18 Wuta ta sauko bisa magoya bayansu,

Ta ƙone mugayen mutanen nan.

19 Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb,

Suka yi masa sujada.

20 Suka musaya ɗaukakar Allah

Da siffar dabba mai cin ciyawa.

21 Suka manta da Allah wanda ya cece su,

Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.

22 Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al’ajabi a can!

Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya!

23 Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama’arsa,

Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah,

Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba.

24 Sai suka ƙi ƙasan nan mai ni’ima,

Saboda ba su gaskata alkawarin Allah ba.

25 Suka zauna cikin alfarwansu suna ta gunaguni,

Sun ƙi su saurari Ubangiji.

26 Saboda haka ya yi musu kakkausan kashedi,

Cewa shi zai sa su duka su mutu a jejin,

27 Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna,

Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa.

28 Sai jama’ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba’al sujada, a Feyor,

Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli.

29 Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu,

Mugawar cuta ta auka musu,

30 Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin,

Aka kuwa kawar da annobar.

31 Tun daga lokacin nan ake ta tunawa da shi,

Saboda abin da ya yi.

Za a yi ta tunawa da shi a dukan zamanai masu zuwa.

32 Jama’ar Ubangiji suka sa ya yi fushi.

A maɓuɓɓugan Meriba,

Musa ya shiga uku saboda su.

33 Suka sa Musa ya husata ƙwarai,

Har ya faɗi abubuwan da bai kamata ya faɗa ba.

34 Suka ƙi su kashe arna,

Yadda Ubangiji ya umarta,

35 Amma suka yi aurayya da su,

Suka kwaikwayi halayen arnan.

36 Jama’ar Allah suka yi wa gumaka sujada.

Wannan kuwa ya jawo musu hallaka.

37 Suka miƙa ‘ya’yansu mata da maza hadaya ga allolin arna.

38 Suka karkashe mutane marasa laifi,

Wato ‘ya’yansu mata da maza.

Suka miƙa su hadaya ga gumakan Kan’ana,

Suka ƙazantar da ƙasar saboda kashe-kashenkan da suke yi.

39 Ta wurin ayyukansu, suka ƙazantar da kansu,

Suka zama marasa aminci ga Allah.

40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da jama’arsa,

Ransa bai ji daɗinsu ba.

41 Sai ya bar su ƙarƙashin ikon arna,

Abokan gābansu suka mallake su.

42 Abokan gābansu suka zalunce su,

Suka tilasta su, su yi musu biyayya.

43 Sau da yawa Ubangiji yakan ceci jama’arsa,

Amma sun fi so su yi masa tawaye,

Suna ta nutsawa can cikin zunubi.

44 Duk da haka Ubangiji ya ji su sa’ad da suka yi kira gare shi,

Ya kula da wahalarsu.

45 Saboda su ne ya tuna da alkawarinsa,

Ya sāke ra’ayinsa saboda ƙaunarsa mai yawa.

46 Ubangiji ya sa waɗanda suka kama su

Su ji tausayinsu.

47 Ka cece mu, ya Ubangiji Allahnmu,

Ka komo da mu daga cikin sauran al’umma,

Domin mu yabi sunanka mai tsarki,

Mu kuma yi murna mu yi maka godiya.

48 Sai mu yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila,

Mu yabe shi yanzu da har abada kuma!

Dukan jama’a za su amsa su ce, “Amin! Amin!”

Ku yabi Ubangiji!

Categories
ZAB

ZAB 107

Ubangiji Ne Mai Kuɓutarwa daga Wahala

1 Ku gode wa Ubangiji, gama shi nagari ne,

Ƙaunarsa madawwamiya ce!

2 Ku zo mu yabi Ubangiji tare,

Dukanku waɗanda ya fansa,

Gama ya ƙwato ku daga maƙiyanku.

3 Ya komo da ku daga ƙasashen waje,

Daga gabas da yamma, kudu da arewa.

4 Waɗansu suka yi ta kai da kawowa a hamada inda ba hanya,

Sun kasa samun hanyar da za ta kai su garin da za su zauna a ciki.

5 Suka yi ta fama da yunwa, da ƙishirwa,

Suka fid da zuciya ga kome.

6 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji,

Ya kuwa cece su daga wahalarsu.

7 Ya fisshe su, ya bi da su sosai,

Zuwa birnin da za su zauna.

8 Dole ne su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa,

Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu!

9 Ya shayar da waɗanda suke jin ƙishirwa,

Ya kuma ƙosar da mayunwata da alheransa.

10 Waɗansu suna zaune cikin duhu da inuwar mutuwa,

‘Yan sarƙa suna shan wahala da sarƙoƙi,

11 Saboda sun tayar, sun ƙi bin umarnan Allah Maɗaukaki,

Sun kuwa ƙi koyarwarsa.

12 Suka gaji tiƙis saboda tsananin aiki,

Za su faɗi ƙasa, ba mataimaki.

13 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji,

Ya kuwa cece su daga wahalarsu.

14 Ya fisshe su daga cikin duhu da inuwar mutuwa,

Ya tsintsinka sarƙoƙinsu.

15 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa,

Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.

16 Ya kakkarya ƙofofin da aka yi da tagulla.

Ya kuma ragargaza ƙyamaren da aka yi da baƙin ƙarfe.

17 Waɗansu suka yi ciwo sabili da zunubansu,

Suna ta shan wahala saboda muguntarsu.

18 Ba su so su ga abinci,

Sun kusa mutuwa.

19 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji,

Ya kuwa cece su daga azabar da suke sha.

20 Da umarninsa ya warkar da su,

Ya cece su daga kabari.

21 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa,

Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.

22 Dole su gode masa, su miƙa masa hadayu,

Su raira waƙoƙin murna,

Su faɗi dukan abin da ya yi!

23 Waɗansu suka yi tafiya a teku da jirage,

Suna samun abin zaman garinsu daga tekuna.

24 Suka ga abin da Ubangiji ya aikata,

Ayyukansa masu banmamaki waɗanda ya yi a tekuna.

25 Ya ba da umarni, sai babbar iska ta tashi,

Ta fara hurowa, ta sa raƙuman ruwa su tashi.

26 Aka ɗaga jiragen ruwa sama,

Sa’an nan suka tsinduma cikin zurfafa.

Da mutanen suka ga irin hatsarin da suke ciki,

Sai zuciyarsu ta karai.

27 Suka yi ta tuntuɓe suna ta tangaɗi kamar bugaggu,

Gwanintarsu duka ta zama ta banza.

28 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji,

Ya kuwa cece su daga azabarsu.

29 Ya sa hadiri ya yi tsit,

Raƙuman ruwa kuma suka yi shiru.

30 Suka yi murna saboda wurin ya yi shiru,

Ya kuma kai su kwatar jiragen ruwa lafiya,

Wurin da suke so.

31 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa,

Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.

32 Dole su yi shelar girmansa cikin taron jama’a,

Su kuma yabe shi a gaban majalisar dattawa.

33 Ubangiji ya sa koguna suka ƙafe ƙaƙaf,

Ya hana maɓuɓɓugai su gudana.

34 Ya mai da ƙasa mai dausayi ta zama mai gishiri, marar amfani,

Saboda muguntar waɗanda suke zaune a can.

35 Ya sāke hamada ta zama tafkunan ruwa,

Ya kuma mai da busasshiyar ƙasa ta zama maɓuɓɓugai masu gudana.

36 Ya bar mayunwata su zauna a can,

Suka kuwa gina birni don su zauna a ciki.

37 Suka shuka gonaki suka dasa kurangar inabi,

Waɗanda suka ba da amfani mai yawan gaske.

38 Ya sa wa jama’arsa albarka,

Suka kuwa haifi ‘ya’ya da yawa.

Bai bar garkunan shanunsu su ragu ba.

39 Sa’ad da aka ci nasara a kan jama’ar Allah,

Aka ƙasƙantar da su ta wurin mugun zalunci,

Da wahalar da aka yi musu.

40 Sai Allah ya wulakanta waɗanda suka zalunci jama’arsa.

Ya sa su suka yi ta kai da kawowa

A hamada inda ba hanya.

41 Ya tsamo masu bukata daga cikin baƙin cikinsu,

Ya sa iyalansu su riɓaɓɓanya kamar garkunan tumaki.

42 Da adalai suka ga wannan, sai suka yi murna,

Mugaye kuwa aka rufe bakinsu.

43 Da ma a ce masu hikima

Za su yi tunani a kan waɗannan abubuwa,

Da ma kuma su yarda

Da madawwamiyar ƙaunar Ubangiji.

Categories
ZAB

ZAB 108

Addu’ar Neman Tsari daga Maƙiya

1 A shirye nake, ya Allah,

Na shirya sosai!

Zan raira waƙa in yabe ka!

Ka farka, ya raina!

2 Ku farka, ya molona da garayata!

Zan farkar da rana!

3 Zan yi maka godiya a tsakiyar sauran al’umma, ya Ubangiji!

Zan yabe ka a tsakiyar kabilai!

4 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har can saman sammai,

Amincinka kuma ya kai sararin sammai.

5 Ya Allah, ka bayyana girmanka a sararin sama,

Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!

6 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu’ata,

Domin jama’ar da kake ƙauna ta sami cetonka.

7 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce,

“Da nasara zan raba Shekem,

Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama’ata.

8 Gileyad tawa ce, har da Manassa ma,

Ifraimu ne kwalkwalina,

Yahuza kuma sandana ne na sarauta.

9 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki,

Edom kuwa kamar akwatin takalmina.

Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.”

10 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara?

Wa zai kai ni Edom?

11 Da gaske ka yashe mu ke nan?

Ba za ka yi tafiya

Tare da sojojinmu ba?

12 Ka taimake mu, mu yaƙi abokin gāba,

Domin taimako irin na mutum banza ne!

13 Idan Allah yana wajenmu,

Za mu yi nasara,

Zai kori abokan gābanmu.

Categories
ZAB

ZAB 109

Kukan Mutumin da Yake Shan Wahala

1 Ina yabonka, ya Allah, kada ka yi shiru!

2 Mugaye da maƙaryata sun tasar mini,

Suna ta faɗar ƙarairayi a kaina.

3 Suna faɗar mugayen abubuwa a kaina.

Suna tasar mini ba dalili.

4 Suna ƙina ko da yake ina ƙaunarsu,

Har ina yi musu addu’a.

5 Sukan sāka mini alheri da mugunta,

Sukan sāka mini ƙauna da ƙiyayya.

6 Ka zaɓi lalataccen mutum ya shara’anta maƙiyina,

Ka sa ɗaya daga cikin maƙiyansa

Ya gabatar da ƙararsa.

7 Ka sa a same shi da laifi a shari’ar da ake yi masa,

Ka sa har addu’ar da yake yi

Ta zama babban laifi!

8 Ka aukar masa da ajalinsa nan da nan,

Ka sa wani ya ɗauki matsayinsa!

9 Ka sa ‘ya’yansa su zama marayu,

Matarsa kuwa ta zama gwauruwa!

10 Ka sa ‘ya’yansa su rasa gidan zama, su riƙa yawon bara.

Ka sa a kore su daga kufan da suke zaune!

11 Ka sa waɗanda suke binsa bashi su kwashe

Dukan abin da yake da shi.

Ka sa baƙi su kwashe dukan abin da ya sha wahalar nema.

12 Ka sa kada kowa ya yi masa alheri sam,

Kada ka bar kowa ya lura da marayunsa.

13 Ka sa dukan zuriyarsa su mutu,

Har a manta da sunansa a tsara mai zuwa.

14 Sai ka tuna, ya Ubangiji, da muguntar kakanninsa,

Kada ka manta da zunuban mahaifiyarsa.

15 Ka tuna da zunubansu kullayaumin, ya Ubangiji,

Amma su kansu a manta da su ɗungum!

16 Gama mutumin nan bai taɓa tunanin yin alheri ba,

Yakan tsananta wa talakawa, da matalauta, da kasassu, har ya kashe su.

17 Yana jin daɗin la’antarwa, ka sa a la’anta shi!

Ba ya son sa albarka, ka sa kada kowa ya sa masa albarka!

18 Yakan la’antar a sawwaƙe kamar yadda yake sa tufafinsa.

Ka sa la’antarwa da yake yi

Su jiƙa shi kamar ruwa,

Su shiga har ƙasusuwansa kamar mai,

19 Su lulluɓe shi kamar tufa,

Su kuma kewaye shi kamar ɗamara.

20 Ya Ubangiji, ka sa haka,

Wato ya zama yadda za a hukunta wa maƙiyana ke nan,

Waɗanda suke faɗar mugayen abubuwa a kaina!

21 Amma ya Ubangiji, Allahna, ka taimake ni,

Yadda ka alkawarta,

Ka cece ni sabili da alherin ƙaunarka.

22 Ni talaka ne, matalauci,

Na ji zafi ƙwarai a can zuciyata.

23 Na kusa ɓacewa kamar inuwar maraice,

An hurar da ni can kamar ƙwaro.

24 Gwiwoyina sun yi suwu saboda rashin abinci,

Jikina kuma ya rame, ba shi da ƙarfi.

25 Sa’ad da mutane suka gan ni sun yi mini ba’a,

Suna kaɗa kai saboda raini.

26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna,

Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka!

27 Ka sa maƙiyana su sani,

Kai ne Mai Cetona.

28 Watakila su la’anta ni,

Amma kai za ka sa mini albarka,

Ka sa a kori waɗanda suke tsananta mini.

Da ma ka sa ni da nake bawanka, in yi murna.

29 Ka sa kunya ta rufe maƙiyana,

Ka sa su sa kunyarsu kamar riga.

30 Da murya mai ƙarfi zan yi wa Ubangiji godiya.

Zan yabe shi a taron jama’a,

31 Saboda yakan kāre talaka,

Domin ya cece shi daga waɗanda

Suka sa masa laifin mutuwa.

Categories
ZAB

ZAB 110

Ubangiji Ya Ba Sarkin da Ya Zaɓa Iko

1 Ubangiji ya ce wa Mai Girma, Sarkina,

“Zauna nan a damana,

Har in sa maƙiyanka a ƙarƙashin sawayenka.”

2 Tun daga Sihiyona Ubangiji zai faɗaɗa sarautarka, ya ce,

“Ka yi mulki bisa maƙiyanka.”

3 A ranar da za ka yi yaƙi da maƙiyanka,

Jama’arka za su kawo maka gudunmawa don kansu.

Kamar yadda raɓa take da sassafe,

Haka samarinka za su zo wurinka a tsarkakan tsaunuka.

4 Ubangiji ya yi muhimmin alkawari,

Ba kuwa zai fasa ba!

“Za ka zama firist har abada

Bisa ga tsabi’ar Malkisadik firist.”

5 Ubangiji yana damanka,

Zai kori sarakuna a ranar da ya husata.

6 Zai shara’anta wa dukan sauran al’umma,

Ya rufe fagen fama da gawawwaki,

Zai kori sarakunan duk duniya.

7 Sarkin zai sha ruwan rafin da yake kan hanya,

Ya wartsake ya sami ƙarfi.

Zai yi tsayawar nasara.

Categories
ZAB

ZAB 111

Kiyayewar Ubangiji ga Jama’arsa

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zan yi wa Ubangiji godiya da zuciya ɗaya,

A cikin taron jama’arsa.

2 Abubuwan banmamaki ne Ubangiji yake aikatawa!

Duk waɗanda suke murna da su

Suna so su fahimce su.

3 Dukan abin da yake yi,

Cike yake da girma da ɗaukaka,

Adalcinsa har abada ne.

4 Ubangiji ba zai bar mu mu manta da ayyukansa masu banmamaki ba,

Shi mai alheri ne, mai jinƙai kuma.

5 Yakan tanada wa masu tsoronsa abinci,

Bai taɓa mantawa da alkawarinsa ba.

6 Ya nuna ikonsa ga jama’arsa

Saboda ya ba su ƙasashen baƙi.

7 Iyakar abin da yake yi duka, da aminci da adalci ne.

Dukan umarnansa, abin dogara ne.

8 Sukan tabbata har abada,

Da gaskiya da adalci aka ba da su.

9 Ya kawo wa jama’arsa ceto,

Ya kuma yi musu madawwamin alkawari.

Mai Tsarki ne shi, Maɗaukaki!

10 Hanyar samun hikima, ita ce tsoron Ubangiji,

Yakan ba da kyakkyawar ganewa

Ga dukan waɗanda suke bin umarnansa,

Sai ku yabe shi har abada!

Categories
ZAB

ZAB 112

Wadatar Mai Tsoron Allah

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Mai farin ciki ne mutumin da yake tsoron Ubangiji,

Mai farin ciki ne shi wanda yake jin daɗin yin biyayya da umarnansa.

2 ‘Ya’yansa za su zama manyan ƙasar,

Zuriyar mutumin kirki za ta yi albarka.

3 Iyalinsa za su zama attajirai masu dukiya,

Adalcinsa zai tabbata har abada.

4 Haske yakan haskaka wa mutanen kirki a cikin duhu,

Da waɗanda suke yin alheri, da jinƙai, da gaskiya.

5 Mai farin ciki ne mutumin da yakan ba da rance hannu sake,

Wato wanda yake yin harkarsa da gaskiya.

6 Mutumin kirki ba zai kāsa ba daɗai,

Ba za a taɓa mantawa da shi ba.

7 Ba ya tsoron jin mugun labari,

Bangaskiyarsa tana da ƙarfi,

Ga Ubangiji yake dogara.

8 Ba shi da damuwa ko tsoro,

Ya tabbata zai ga faɗuwar maƙiyansa.

9 Yakan bayar ga matalauta hannu sake,

Alherinsa kuwa dawwamamme ne.

Zai zama mai iko wanda ake girmamawa.

10 Sa’ad da mugaye suka ga wannan,

Sai suka tunzura, suka harare shi da fushi, suka ɓace,

Sa zuciyarsu ta ƙare har abada.