Categories
ZAB

ZAB 123

Addu’ar Neman Jinƙai

1 Ya Ubangiji, ina zuba ido gare ka,

A Sama inda kake mulki.

2 Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa,

Baranya kuma ga uwargijiyarta,

Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu,

Har mu sami jinƙanka.

3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai,

An gwada mana wulakanci matuƙa!

4 Attajirai sun daɗe suna ta yi mana ba’a,

Azzalumai masu girmankai sun raina mu!

Categories
ZAB

ZAB 124

Allah Ne Mai Ceton Jama’arsa

1 Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu,

Da me zai faru?

Ba da amsa, ya Isra’ila!

2 “Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu,

A lokacin da abokan gābanmu suka auka mana,

3 Da sun haɗiye mu da rai a lokacin nan,

Saboda zafin fushi da suke yi da mu,

4 Da rigyawa ta kwashe mu,

Da ruwa yi ci mu,

5 Kwararowar ruwa ya nutsar da mu.”

6 Sai mu gode wa Ubangiji,

Da bai bar abokan gābanmu su hallaka mu ba.

7 Mun kuɓuta kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta,

Tarkon ya tsinke, mun ‘yantu!

8 Taimakonmu daga wurin Ubangiji yake zuwa,

Shi wanda ya yi sama da duniya.

Categories
ZAB

ZAB 125

Zaman Lafiyar Jama’ar Allah

1 Waɗanda suke dogara ga Ubangiji,

Suna kama da Dutsen Sihiyona,

Wanda ba zai jijjigu ba, faufau.

Faufau kuma ba za a kawar da shi ba.

2 Kamar yadda duwatsu suka kewaye Urushalima,

Haka nan Ubangiji zai kewaye jama’arsa,

Daga yanzu har abada.

3 Ba a koyaushe mugaye za su yi mulki a ƙasar jama’ar Allah ba,

Idan kuwa suka yi, to, ya yiwu jama’ar Allah su yi laifi.

4 Ya Ubangiji, ka yi wa mutanen kirki alheri,

Su waɗanda suke biyayya da umarnanka!

5 Amma ka hukunta waɗanda suke bin mugayen al’amuransu,

Sa’ad da kake hukunta wa masu aikata mugunta!

Salama ta kasance tare da Isra’ila!

Categories
ZAB

ZAB 126

Godiyar Samun Ceto

1 Sa’ad da Ubangiji ya komar da mu cikin Sihiyona,

Sai abin ya zama kamar mafarki!

2 Muka kece da dariya, muka raira waƙa don farin ciki,

Sa’an nan sai sauran al’umma suka ambace mu, suka ce,

“Ubangiji ya yi manyan al’amura masu girma, sabili da su!”

3 Hakika ya aikata manyan al’amura sabili da mu,

Mun kuwa yi farin ciki ƙwarai!

4 Ya Ubangiji, ka komar da mu ƙasarmu

Kamar yadda ruwan da kake yi yakan koma cikin busassun koguna,

5 Ka sa waɗanda suke kuka a lokacin da suke dashe,

Su tattara albarkar kaka da farin ciki!

6 Su waɗanda suka yi kuka a sa’ad da suka fita suna ɗauke da iri,

Za su komo ɗauke da albarkar kaka,

Suna raira waƙa don farin ciki!

Categories
ZAB

ZAB 127

Yabon Alherin Ubangiji

1 Idan ba Ubangiji ne ya gina gidan ba,

Aikin magina banza ne.

Idan ba Ubangiji ne ya tsare birnin ba,

Ba wani amfani a sa matsara su yi tsaro.

2 Ba wani amfani a sha wahalar aiki saboda abinci,

A yi asubancin tashi, a yi makarar kwanciya,

Gama Ubangiji yakan hutar da waɗanda yake ƙauna.

3 ‘Ya’ya kyauta ne daga wurin Ubangiji,

Albarka ce ta musamman.

4 ‘Ya’ya maza da mutum ya haifa a lokacin ƙuruciyarsa

Kamar kibau suke a hannun mayaƙi.

5 Mai farin ciki ne mutumin da yake da irin waɗannan kibau da yawa!

Faufau ba za a ci nasara a kansa ba,

Sa’ad da ya kara da maƙiyansa a wurin shari’a.

Categories
ZAB

ZAB 128

Albarkar Mai Tsoron Ubangiji

1 Mai farin ciki ne wanda yake tsoron Ubangiji,

Wanda yake zamansa bisa ga umarnansa!

2 Za ka sami isasshen abin biyan bukatarka,

Za ka yi farin ciki ka arzuta.

3 Matarka za ta zama kamar kurangar inabi

Mai ‘ya’ya a gidanka,

‘Ya’yanka maza kuma kamar dashen zaitun

Suna kewaye da teburinka.

4 Mutumin da yake yi wa Ubangiji biyayya,

Hakika za a sa masa albarka kamar haka.

5 Ubangiji ya sa maka albarka daga Sihiyona!

Ya sa ka ga Urushalima ta arzuta

Dukan kwanakinka!

6 Ya kuma sa ka ka ga jikokinka!

Salama ta kasance ga Isra’ila!

Categories
ZAB

ZAB 129

Addu’a a kan Maƙiyan Isra’ila

1 Isra’ila, sai ka faɗi irin muguntar

Da maƙiyanka suka tsananta maka da ita,

Tun kana ƙarami!

2 “Maƙiyana suka tsananta mini da mugunta,

Tun ina ƙarami,

Amma ba su yi nasara da ni ba.

3 Suka sa mini raunuka masu zurfi a bayana,

Suka mai da shi kamar gonar da aka nome.

4 Amma Ubangiji mai adalci,

Ya ‘yantar da ni daga bauta.”

5 Allah ya sa duk waɗanda suke ƙin Sihiyona,

A yi nasara da su a kuma kore su!

6 Allah ya sa su zama kamar ciyawar da take girma a kan soraye,

Ta kuwa bushe kafin ta isa yanka.

7 Ba wanda zai tattara ta,

Ya ɗaure ta dami dami.

8 Duk waɗanda suke wucewa a hanya ba za su ce,

“Ubangiji ya sa maka albarka!” ba,

Ko su ce, “Muna sa maka albarka da sunan Ubangiji!”

Categories
ZAB

ZAB 130

Sa Zuciya ga Ceton Allah

1 A cikin fid da zuciyata,

Na yi kira gare ka, ya Ubangiji.

2 Ka ji kukana, ya Ubangiji,

Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!

3 Idan kana yin lissafin zunubanmu,

Wa zai kuɓuta daga hukunci?

4 Amma kakan gafarta mana,

Domin mu zama masu tsoronka.

5 Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji,

Ga maganarsa na dogara.

6 Ina jiran Ubangiji,

Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir,

I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir.

7 Ya Isra’ila, ki dogara ga Ubangiji,

Saboda ƙaunarsa madawwamiya ce,

A koyaushe yana da nufin yin gafara.

8 Zai fanshi jama’arsa Isra’ila

Daga dukan zunubansu.

Categories
ZAB

ZAB 131

Addu’ar Tawali’u

1 ‘Ya Ubangiji, na rabu da girmankai,

Na bar yin fariya,

Ba ruwana da manyan al’amura,

Ba ruwana kuma da zantuttukan da suka fi ƙarfina.

2 Amma na haƙura, raina a kwance,

Kamar jinjirin da yake kwance jalisan a hannun mahaifiyarsa,

Haka zuciyata take kwance.

3 Ya Isra’ila, ka dogara ga Ubangiji,

Daga yanzu har abada!

Categories
ZAB

ZAB 132

Yabo saboda Tsattsarkan Wuri

1 Ya Ubangiji, kada ka manta da Dawuda

Da dukan irin aikin da ya yi.

2 Ka tuna, ya Ubangiji, da alkawarin da ya yi,

Da rantsuwar da ya yi maka, ya Maɗaukaki, Allah na Isra’ila,

3 “Ba zan tafi gida ko in kwanta ba,

4 Ba zan huta, ko in yi barci ba,

5 Sai sa’ad da na shirya wa Ubangiji wuri,

Wato Haikali domin Maɗaukaki, Allah na Isra’ila.”

6 Mun ji labari akwatin alkawari yana Baitalami,

Amma muka same shi a kurmi.

7 Muka ce, “Bari mu tafi Haikalin Ubangiji,

Mu yi sujada a gaban kursiyinsa!”

8 Ka zo wurin hutawarka, ya Ubangiji,

Tare da akwatin alkawari,

Alama ce ta ikonka.

9 Ka suturta firistoci da adalci,

Ka sa dukan jama’arka su yi sowa ta farin ciki!

10 Ka yi wa bawanka Dawuda alkawari,

Kada ka rabu da zaɓaɓɓen sarkinka, ya Ubangiji!

11 Ka yi wa Dawuda muhimmin alkawari,

Ba kuwa za ka ta da alkawarin ba.

Ka ce, “Za naɗa ɗaya daga cikin ‘ya’yanka maza yă zama sarki,

Zai yi mulki a bayanka.

12 Idan ‘ya’yanka maza za su amince da alkawarina,

Da umarnan da na yi musu,

‘Ya’yansu maza kuma za su bi bayanka su zama sarakuna,

A dukan lokaci.”

13 Ubangiji ya yaɓi Sihiyona,

A can yake so ya gina Haikalinsa, ya ce,

14 “A nan zan zauna har abada.

A nan kuma nake so in yi mulki.

15 Zan tanada wa Sihiyona dukan abin da take bukata a yalwace,

Zan ƙosar da matalautanta da abinci.

16 Zan sa firistocinta su yi shela,

Cewa ina yin ceto,

Jama’ata kuma za su raira waƙa,

Suna sowa don farin ciki.

17 A nan ne zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyar Dawuda

Yake zama babban sarki,

A nan ne kuma zan wanzar da

Mulkin zaɓaɓɓen sarkina.

18 Zan sa maƙiyansa su sha kunya,

Amma mulkinsa zai arzuta.

Ya kuma kahu.”